Skip to content

Chapter 80

Chapter 80

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,205 words 0 views Progress saved
Download Book

kalli Ummi cikin nitsuwa yace. "In sha Allah jibi zamu tafi india, kuma Alhamdulillahi kafinma muje bayanan zuwanmu ya shiga hannun doctors d'insu." cikin sauk'e numfashi Ummi tace. "To Allah ya kaimu lfy ya kuma bada sa'an aiki." cikin son kontar mata da hankalin Dr Adnan yace. "Yanzu Ummi keda Ishaq zaku koma gombe gobe." da sauri Ummi tace. "In koma Gombe kuma?." Cikin nitsuwa Ya Rabi'u ya gyad'a mata kai tare da cewa. "Eh Ummi ba matsala ke da Ishaq ku koma gombe, Ahmad da Hayatuddeen kuwa dasu za'a tafi, tare da Dr Adnan kuma shima in yaje ba dad'ewa zaiba in yaga anyi aiki dai to zai dawo kiji labarin jikin Saifuddeen d'in kuma, in ya dawo keda Ishaq da bappa Ali zakuje." kai ta sunkuyar kana murya a sanyaye tace. "Yanzu sai in zauna a tafi dashi har wata k'asa ta daban." Ahmad ne ya d'an kalleta tare cewa. "Ummi nida Hayatuddeen zamuyi duk abinda zakiyi mishi karki damu zamu kula dashi." still dai kamar bata gamsuba ido ta zubawa Dr Batulu da ta dafa kafad'unta tare da cewa. "Ummin Saifuddeen ki kwantar da hankalinki shi jinyan namiji saida namiji d'an uwanshi hakama mace saida macce yar uwarta, kuma duk sanda kikeson zuwa zakije ki duboshi." cikin gamsuwa tace. "To ba komai Allah ya shige mana gaba." Sai ta kuma juyawa ta kalli Saifuddeen da yake kallonta fuska cike da bege murya can k'asa tace. "Allah ya baka lfy babana." Amin Amin suka amsa baki d'aya, shi kuwa Hayatuddeen wayarshi daketa ringing ya d'aga ganin Salisu ne ya sashi mik'awa Ummi. "Barka da safiya Ummi." "Barka dai Salisu ya kasuwa?." "Lfy lau Alhamdulillahi, ya Saifuddeen da jikin?." Cikin rawan murya tace. "To Alhamdulillahi jiki sai dai ace da sauk'i. Amman yanzuma fa shiri akeyi wai za'a fiddashi k'asar India." sai ta kuma share hawayenta tare da ci gaba da cewa. "Kuma sunce wai baza'a je daniba." Cikin k'arfin hali Salisu yace. "Ba komai Ummi in sha zai samu lfy ki kwantar da hankalin ki, nima daga nan in na gama abinda nakeyi bazan dawo Nigeria ba zan wuce can india inga jikinshi kafin in dawo, ki kwantar da hankalinki ai yanzu duniya a had'e wuri d'aya take." sosai ya bata k'arfin guiwa sannan yace ta bawa Ahmad nan ta bashi suka gaisa. Daga nan duk suka tafi dan ganin azahar tayi kuma doctor yace su fita su bashi wuri ya huta. Koda suka koma gidan Ya Rabi'u, sosai Aunty Mami tayi ta karfafawa Ummi zuciya har dai ta nitsu akan washe gari zasuyi sammako diraban ya Rabi'u zai maidasu Gombe kana ya taho dasu Rahma suma su ganshi kafin ya tafi. Washe gari bayan an idar da sallan asuba Ayuba ya d'auki Ummi da Ishaq dan zasuyi sammako, jin zasu biya asibiti ne yasa Hayatuddeen cewa to zai bisu a saukeshi a asibitin. K'arfe bakwai dai-dai suka isa cikin d'akin da Saifudden yake. Konce suka sameshi kamar ko yaushe yana tsabtace dan masu gyarashi na fita ne su kuma suka shigo. Hannu ya mik'o ya kama na Ishaq tare da rubuta mishi text. "Please Ishaq ga Ummi na dan Allah kake yawan zuwa gida kana kontar mata da hankalin, kaga tare da Hayatuddeen zamu tafi, Raihana kuma itama in sunzo kawai ta koma d'akinta kada tace zata koma gombe, dan Saminu yace min shima ya kusa dawowa, sannan akwai system na a motar Sule da k'aramar wayata, duk a bawa su Raliya su kawo min su." cikin nitsuwa Ishaq yace. "In sha Allah ba damuwa nima da Ummin zamu zo ai mu dubaka, ba matsala zasu zo maka dasu." Ita kuwa Ummi cikin sanyi ta shafa kan Saifuddeen har zuwa goshinsa, cikin sanyi tace. "Babana zan tafi yanzu zamu koma gombe sunce ku kuma gobe zaku tafi india,." sai ta kuma share hawayenta tare da ci gaba da cewa. "Zan tafi badon na soba sai dai kada suce na raina musu ne, Allah ya k'addara saduwarmu kan al'kairi Allah ya baka lfy babana Allah yasa da akwai sauran ganawa a tsaka ninmu, Allah ya baka lfy." da sauri ya jawo tafin hannunta ya mannashi bisa hab'arshi yana mai zubda wasu zazzafan hawaye wanda ganin hawayen mahaifiyar tashi ne yasa nashi zubowa. Hayatuddeen kuwa hannu yasa yana share mata hawayenta, dai-dai lokacin Nurse d'in nan Amina ta shigo, gefensu can ta tsaya tare da kallon Ummi dake kuka cur-cur da hawaye, da sauri ta sunkuyar da kanta dan itama idanunta sun cicciko da hawaye cikin danne rawan muryarta ta kalli Ummi tare da cewa. "Kiyi hak'uri Mama ki daina kuka in sha Allah zai samu lfy." kai ta gyad'a tare da kamo hannun Saifuddeen d'in tace. "Allah ya baka lfy." sai kuma tasa hannunta ta share hawayen fuskarshi dana Hayatuddeen kana ta juya da sauri ta fita. jin motsin ta fitane yasa Ishaq yabi bayanta, kai tsaye inda Ayuba yayi parking suka nufa, suna shiga yaja mota suka fita daga asibitin suka nufi kama hanyar gombe. A cikin room d'in da Saifuddeen ke ciki kuwa Ummi na fita Hayatuddeen ya zauna kan kujerar data tashi, ya kife kanshi gefen pillow Saifuddeen yana mai shesshek'an kuka a hankali, shi kuwa Saifuddeen rumtse idanunshi yayi yayinda wasu hawayen ke zubo mishi, a hankali Amina ta matso kusa dasu cikin nitsuwa ta iso gabansu, ido ta zubawa fuskarshi Hayatuddeen tana kallonshi tamkar Aminu k'aninta mai binta kusan komansu dai-dai da Aminunsu. a hankali tasa hannu ta tallabo fuskarshi, ido ya bud'e jin an d'ago kanshi, kai ta jujjuya mishi alamun ya bar kuka, sai ta kuma zaro hankicib d'inta dake cikin al'jihunta ta mik'a mishi, hannu yasa ya k'arba sannan ya shinfid'eshi bisa fuskarshi, ita kuwa Amina a hankali ta juyo kan Saifuddeen wanda idanshi ke lumshe hawayenshi na zubowa suna gangarowa har cikin kunnenshi kasan cewar konce yake a rigingine. K'ara matsowa tayi gab dashi, yayinda shi kuwa yake kallonta ta tsakankanin gashin idanunshi. hannu tasa dai-dai bisa hab'arshi sai kuma tayi saurin janye hannun tare da zuba mishi idanu, ganin idanshi a rufene yasa ta sake kai hannunta duka biyu a hab'arshi na gefen dama da hagu, manyan yatsunta tasa can k'asa idanshi sannan tasa sauran yatsunta hud'un ta tare tsakanin hab'arshi da kunnenshi sai ta jawo manyan yatsun tannan a hankali tana koro hawaye suna gangarowa tsakiyar tafin hannunta. Shi kuwa Saifuddeen wani irin razanennen bugu heart beat nashi yakeyi so fast, shiru yayi tamkar baya numfashi, hakan ya bata damar share mishi hawayen kab ta tarasu cikin tafin hannunta, sai ta had'e hannunta wuri d'aya ta murza ruwan hawayen nashi tare da shafa hannun nata a fuskarta kamar mai shafa mai. idonshi ya bud'e tare da tsareta dasu, ita kuwa da sauri ta juya ta fuskanci Hayatuddeen, sai kuma tayi saurin kauda kanta ganin Hayatuddeen yana d'aga mata girarshi tare da cewa. "Kin yi sa'a kin samu tabarrakin hawayen hammana." allura ta ciro ta had'a kana ta mishi allurar sannan tasa hannu zata b'allo mgnin ta bashi sai kuma ta tsaya jin Hayatuddeen na cewa. "Kada ki b'are mgnin bazai sha abin hannunkiba in ba wonke hannunki kikayi ba." ba tare da tace komaiba ta juya ta d'au goran ruwan dake gefenshi sannan ta d'an matso jikin

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148