Skip to content

Chapter 51

Chapter 51

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
Download Book

Kabiru kafin su Ummi su k'auro. Shirye-shiryen k'aurafa ya kankama Bappa Ali ya kwashi d'alibanshi sukaje sukayi kwana uku a gidan suna sauk'an karatun Qur'an da sadaka maganin masifa, bayan sun gama suka dawo gida, sannan Adda Rahma kuwa ta fara shirya musu waliman k'aura. Raihana ma da Saminunta sun baro Kd zuwa gombe dan ayi k'auran a idansu, Imran kuwa shida kanshi yaje gidajen abokanshi ya gaggayacesu suzo tarban abokinsu ba dukke, Saifuddeen kuwa ya sanarwa abokanshi Jabeer, Hisham, Ibrahim da dai sauransu. A dukku kuwa Aunty Nina sai kuka takeyi dan tasan zatayi kad'aici dan rabuwa da Ummi da yaranta zai shiga jikinta, hakama goggo Dada maman Ahmad sai kukan k'auran sukeyi. Ranar k'auransu ya kama jumma'a , 'yan uwa da abokan arzik'i da mak'ota duk sunyiwa Ummi da ahlinta rakiya suna masu kewar rabuwa da juna. A nan Gombe kuwa sun samu taron iyayen abokan Saifuddeen da Hayatuddeen sai Adda Rahma da mak'otanta da 'yan sirarun k'awayen da ta saba dasu. iyayen Jabeer, Hisham, Ibrahim, Sulaiman, Kakar Zakariyya, da matan Alhaji Kabiru duk sun zo, anyi walima lfy, Ummi ta shiga ran matan dan tanada sakin fuska da mutunta mutane. Bayan kwana ashirin da biyu da k'auransu duk bak'i sun tafi sai Ummi da yaranta da sabon gida da sabuwar Rayuwa. Sauri-sauri Hayatuddeen ya fito daga cikin d'an k'aramin falonshi gaban Ummi ya zauna wacce Raliyya ke yanke mata farce. fuska ya d'an tsuke tare da cewa. "Ni wlh a matse nake a gidannan an wani lik'ani a wannan kurkukun side d'in kamar yaro, kuma ko share min d'akinma Raliya batayi sai a barmin komai a hargitse." tsaki Raliya taja tare da cewa. "Ai ni ba baiwarka bace da zaka hargitsa komai kace ni in gyara maka." harara ya watsa mata tare da cewa. "To ni macece ni da zanyi shara?." ita dai Ummi idanu ta zuba musu inda sabo ai ta saba da tsamar Raliya da Hayatuddeen da d'an korensu Faruq, murmushi tayi jin Raliya na cewa. "Eh baka iya kimtsa kanka da kayanka ba amman ka iya sabule wondo ka tsallake ka barshi a tsakiyar falo dan gaka isshashe kai kanada Raliya baiwa mai yi maka tattara." Faruq ne ya mik'e tare da cewa. "To ai yana jin bacci ne lokacin shiyasa." tura baki tayi kana ta sharesu, shi kuwa Hayatuddeen meda hankalin shi yayi kan Ummi cikin lallab'ata yace. "Ummi kin yiwa Hamma Saifuddeen batun sauyin makarantar da zai mana ne?." kai ta gyad'a mishi kana tace. "Eh na gaya mishi yace zai bincika makarantar data dace daku." ido ya kashewa Faruq sannan ya k'ara motso Ummi cikin sanyin lafazi yace. "Ba na gaya miki cewar akwai wata sabuwar makaranta MATRIX nan bayanmu kadan a kan hanya gab da kuros mai k'ollo nan hanyar F, C, E , makarantar tanada kyau kice masa ya samu nan kinga kusa da gidane koda k'afama zamuje ko Faruq." da sauri Faruq yace. "Eh mana kinga kun huta bamu kud'in machine." da sauri Raliya ta mik'e kalon tara saura kwata tayi musu tare da cewa. "Kan bala'i wannan makarantar da sai yaran manya makarantar da sai dai d'an talaka ya gani da ido shine zakuce shi kukeson Hamma Saifuddeen ya saku ko tausayin shima ku bakwaji kaji hegun yara da girman kai da son k'arya da papa, tab lallai aiki ya sameku yaseen Ummi karki yarda zasu talauta miki d'a dan sunga yana musu duk abinda suke so." da sauri ta kauce ganin Hayatuddeen ya kai mata duka, d'akinta dake fuskantar d'akin Ummi ta shige da gudu tana musu dariyar mugunta. shiko Hayatuddeen wayarshi ya zaro ya amsa kiran Imran wanda yazo dan d'aukan Hayatuddeen suje gidansu Zakariyya dan gaida kakarshi ta fad'i ta gurd'e a hannu. bayan Imran ya shigo sun gaisa da Ummi, sai suka sallameta suka fito. A bakin gate suka d'an tsaya wurin Baba buzu, cikin yanayin sun fara sabawa dashi sukace. "Baba bari muje gidansu Zakariyya." murmushi yayi tare da cewa. "Auho kuce wanda yace zai bani kakarshi in aura in inaso ko?." Cikin shek'iyamci Imran yace. "Yauwa to ita zumuje dubowa, me zaka kawo mu kai mata?." goro ya fiddo cikin aljihun rigarshi irin gara ga nakan nan na buzaye, ya mik'awa Hayatuddeen su tare da cewa. "To gashi ku kai mata wannan." aifa dariya suka sa sannan suka amsa suka tafi. gidansu Isma'il suka biya sannan suka nufi hanyar da zai sadasu da ceceniya kasan cewar ba nisa sosai tsaka ninsu. Suna isa, Zakariyya na jin muryarsu ya fito da sauri yana isa inda suke ya basu hannu suka tafa tare yin murmushi suna cikin haka sukaji wata zazzak'ar murya mai dad'in sauraro tana cewa...! By *GARKUWAR FULANI* 8/18/20, 7:52 PM - Ummi Tandama: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *NAKASA BA KASAWA BACE* *PAGE 12* NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Cikin d'an d'aga murya take cewa. "Zakariyya! Zakariyya!! Zakariyya!!! wlh bana son raini kazo ka bani wayata." cikin d'aga murya Zakariyya yace. "Ank'i a bada d'in uwar masifa k'arfinki ya kwata miki aikin kawai ke ba dama mutun ya tab'a woyarki sai kiyi ta rashin mutunci." dariya Imran yayi tare da cewa. "Yaseen yau sai mun zuk'e cajinki." dai-dai lokacin ta fito daga ganinta yayar Zakariyya ne dan suna d'an kama kekyawace ajin forko tanada cikar sura, idanu ta zubawa Hayatuddeen da yake kallonta tare da cewa. "Wannan itama irin Raliya ce ko sai hegen masifa." Zakariyya ne yayi dariya tare da cewa. "Haka suke dan sun samu sun fimu da sharu uku zuwa hud'u kacal sai sukeji kamar sune suka haifemu." da sauri ta iso ta wabce wayarta dake hannun Imran kana tace. "Hegu kawai masu jajayen fuskoki." cikin tsiya Zakariyya yace. "Shima samune kina bak'in cikin jar fatanmu." tsaki taja tare da cewa. "Hauka kawai me abin jin haushi duk kunyi kalar zabiya kuma dai baku fini fari ba." dariya Imran yayi sannan yace. "Ke dai dama kina bak'in ciki ace Zakariyya ya fiki kyau." juyawa tayi tana cewa. "A ina ka tab'a ganin namiji yafi macce kyau." cikin sauri Hayatuddeen yasha gabanta tare da cewa. "Yaseen na miji nafin mace kyau kin ganki duk da kyanki Hamma Saifuddeen d'ina ya fiki kyau, in kin ganshi keda kanki zaki shaida hakan." bata bi ta kansuba ta shiga cikin parlour inda kakarsu ke kwance tanata raki, bayanta sukabi da saurinsu suna shiga suka gaida Kaka sannan suka zauna gefen ta. Cikin kula tace. "Imarana ya gida?." ba tare da ya juyo ya kalletaba yace. "Lfy lau Alhamdulillahi Mama tace in gaidaki da jiki." "Ina amsawa." ta bashi amsa tare da juyawa tana kallon Hayatuddeen da yake nunawa Zakariyya abu a wayarshi tace. "Kai Hayatu hankalin ka duk yana kan waya, Umminka tana lfy ko." still idanunshi na kan wayar yace. "Nace miki ki dena cemin Hayatu, ki cika min sunana Hayatuddeen ko kuma kice min Deen in kuwa Hayatun kike son fad'i to kice Hayat." dariya budurwannan tayi ganin yadda Tsohuwar taketa buga mishi harara, Isma'il ma da babu bakin mgna sai murmushi yakeyi Imran ma dariyar yayi dan da yaji dariyar Budurwar ne yasashi kallon inda take kallo, d'ago kansu sukayi suma suka kallesu jin dariyar tayi yawa, Zakariyya ne ya kad'a baki yace. "Haba dai Inna ai wannan kallo sai ya razanamu,

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148