Skip to content

Chapter 68

Chapter 68

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,205 words 0 views Progress saved
Download Book

officers d'in da ta samu a wannan ranarba ko guda ɗaya, shiyasa gaba ɗaya ta rasa tudun dafawa. Gudu take tsulawa kamar mai tashi sama, a hankali take bin sautin wak'ar still kuma hawaye na kwaranya a fuskarta har yana d'iga bisa tudun brest d'inta, fuskarta d'auke da murmushi daya tunzura hawayenta tace. "Ina kake wanne hali kake ciki me sunanka?." sai kuma tace. "Allah ya isanmin bazan yafe musuba, Allah zai saka maka zai taimaka maka fiye da yadda ka taimaka min." wayarta keta ringing tanaji tana gani bata kula kiranba, sai yanzu da taji an cire waqar daga can vision d'in ta d'an ja tsaki tare da d'ago woyarta ganin Abdussalam ke kiranta d'an minister, wanda yaketa nacin binta tun last week da suka had'u , Duwa plaza taje sayan burger, tsaki ta kuma ja tare da cewa. "Wannan wanne irin maye ne da baida zuciya, ko uwar me yakeso in mishi da bak'ar fuskarshi kamar an k'ona taya." aje woyar tayi dai dai lokacin data isa, bakin gate din (Jonopwd) d'in. tafiyar mai d'an tsawoce kafin ta isa gab da ofishin nasu, dan sai ka wuce farfajiyar court d'in, dake wurin, ido ta d'an lumshe kana tace kai. "Ya Habu ka cika naci dan kawai ka bani motarka kaketa nacin kirana kamar bazan dawo ba." haka nan har yanzu hawayenta sunƙi tsayuwa sai kuma ta amsa kiran tare da yin kasa da murya tace. "Ya Habu sai yanzu na dawo, kuma yanzu ma haka ina, jonapwd ne." sai ta kuma bud'e marfin motar kana ta zuro kyawawan k'afafunta woje, sannan ta kuma yi muryar shogoban da yanzu mai tushe takeyi dan cikin kwana biyun nan ta zama uwa wata lalatacciyar jiniya abi kaɗan tasa kukan da taketa son ɓoye, to yanzunma hawayen takeyi tare da cewa. "Kuma sai naje Vision dan gabatar da program na." A can gefen Ahmad ne ya amshi wayar Habu kana ya kara a kunne tare da gyara zamanshi kana ya rusunar da kai ya kalli mahaifin nasu kana yace. "Baba malam ke nemanki, yace maza in kiraki ki taho gida." fitowa tayi daga cikin motar, idanu ta lumshe still hawaye na tsiyaya jin wani sassanyan iska dake ratsa dukkan abin halitta dake wurin, a hankali ta bud'e idanun nata kana ta zuwaba jerin bishiyoyi da tsirran da sukayiwa harabar wurin k'awanya, a hankali ta fara taku ih zuwa cikin asalin harabar ofishin, kana cikin fargaba tace. "Dan Allah Ya Ahmad kace wayata bata shiga, nasan abinda Baba malam ke nemana dashi." cikin nitsuwa da kamala Ahmad yace. "Yana ma jinki dan ina gabanshi." ido ta zazzaro tare da dafe k'irjinta cikin kad'uwa tace. "Gani nan zuwa." tana fad'in haka ta katse kiran kana ta k'arisa bakin k'ofar ta shiga danna door bell. minti d'aya tsakani wani matashi yazo ya bud'e mata k'ofar, kana ta kusa kai ta shiga wani corridor tafiya kad'an ta bulla cikin wani tamfatsetsen office wanda aka k'awatashi da ababen buk'atar dan adam, wasu kujerenu ne masu kama da mazaunin lilo ke zagaye da wani babban table na bak'in gilashi wanda yaketa shek'i kana sai fankoki kusan guda biyar da sukabi layin tsawon table d'in, sai wani babbab firij dake can gefe kana, sai wani d'imemen TV sannan sai na'urar AC gudu biyu da suke fuskantar juna, sai kuma wasu k'ofofi d'aya k'ofar tana gab da k'ofar shigowa office d'in wanda bisa dukkan alamu bathroom ne, sai gefen dama da k'ofofi guda uku ke jere bisa dukkan alamu office din shugabannin k'ungiyar ce, kana gefen k'ofofin sai akayi wani dan steps guda biyar in ka haura wani d'an madaidaicin table ne na farin gilas mai ruwan garai-garai sai kujera d'aya rak a gaba kana sai d'aya a bayan table d'in sai tarin na'urai wanda sun kai bakwai. sai gefen hagu nanma haka tsarin yake sai dai shi sai ka d'an ratsa cikin wani corridor mai d'an fad'i. Tana shiga wannan mutumin daya bude mata k'ofar yace. "Barka da zuwa Zalihan nakasassu." murmushi tayi kana taja kujera ta zauna tare da cewa. "Ya Ishaq fa baya nanne?." ba tare data jira amsarshi ba taci gaba da cewa. "Ya naji ma'aikatan naku shiru yau ba mutane?." bisa kujerar gefenta ya zauna tare da cewa. "Ishaq yana Abuja, mutanen mu kuma duk suna fad'ar jiha sunje kai gaisuwa ga mai martaba." mik'ewa tayi taku biyu zuwa uku ta nufi gaban firij, tsayawa ta yi jin abinda Sani ke fad'in. "Ayyah kiyi hak'uri ban kawo miki abin shaba, sorry dawo ki zauna zan kawo miki." cikin yanayin sabo dasu tace. "Wai ku anya kuwa ku makafi ne? yanzu ya akayi kasan gaban firij na nufa?." murmushi yayi tare da d'an kaikaice kunnenshi irin yadda makafi keyi kana yace. "Motsinki da takun tafiyarki ne ya ganar dani inda kika nufa, ke har yau kin kasa barin mmki kan lamarinmu, abinda baku saniba ku. Mu nakasassun munada experience sama daku masu gadara da cikekkiyar halitta." murmushi tayi bayan ta dawo ta zauna, robar faron ta bud'a bayan ta sha kana tayi hamdala dan ta ɗanji tafasar da zuciyarta keyi ya ɗan ragu aje goran tayi sannan tace. "Toh Ya Sani ni zan wuce tunda ciyaman bainan, wata k'il sai next week, zan shigo, dama zan tattauna da sune a shirin da za'a haska a tasharmu na Farin Wata, dan yace min wannan karon da kurame zan tattauna, to gashi Malam Ishaq bai sanarmin bama a kan baya nan da ban zoba." "To ba matsala, Allah ya kaimu lokacin, wannan karon kam hirar da kurame za'ayita?." ya k'arishe mgnar cikin neman k'arin bayani tare da mik'ewa yabi bayanta kana suka fito tare har gaban motarta, sannan tace mishi. "Eh shiyasa dole su sai a tasharmu ta TV za'ayi hira dasu. Yace min da wani babban abokinshi zamu zanta wanda shine Garkuwar asusunku, da nike ta cewa ku fasa ku bani in canza mota, kukak'i, saida kuka bari yan kalare suka fasa min glass, sannan Ya Ahmad na ya canzamin, kuma a kanku motata ke mutuwa kullum ina yawon binku da k'wak'ulo baiwarku." dariya yayi sosai kana yace, wannan asusun namune mu yamu." itama murmushi tayi kana ta shiga mota sannan suka sallami Juna. Daga nan ya koma ciki. Ita kuma ta ja mota, kai tsaye hanyar Vision fm Gombe ta nufa, sanin ana jiranta yasa take sharara gudu kamar babu gobe kana dama d'abirta ne bawa mota wuta, tana isa harabar maikatar tasu tayi parking kana ta fito sauri-sauri gudu-gudu ta shiga cikin ainihin wurin kai tsaye d'akin tace murya ta nufa, tana shiga tazo dai-dai masauk'in bakinsu, taji abokin aikinta Rabeel na cewa. "M.B. S Dukku, sai yanzu ne, ya mutanenki?." bata kai ga amsa mishiba taji muryar d'aya daga cikin abokan aikin nata ta bayanta tana cewa. "M.B Dukku, sai yanzu tun d'azu Abdulsalam da tawagarshi ke nan ya kasa ya tsare sai raba ido yake ta ina zaki fito bai saniba kina can cikin mutanen ki Nakasassu." tsaki taja tare da cewa. "Na damu dashi, in yayi ya haƙura ya bari d'an marasa zuciya kawai." jin wani ya kuma kiranta yasa tace. "Kai dan Allah ku barni in huta ni dai ba dama ku barmin suna ya huta, daga mai cemin Zalee sai

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148