Chapter 76
Chapter 76
Umur sai shi Malam Bashir sai k'anwarsu Goggo Maryam wacce itace akayiwa mai suna da Maryam yayar Zaleeha, Malam Umar yanada matashin hud'u reras Allah ya azirtashi da tarin yara sama da talatin, Malam Umar mutum ne mai tsananin zafi da fad'a yanada tsananin kafiya shi kaifi d'aya ne in yace eh tofa eh dince har gaban abadan babu wanda ya isa ya karya mishi doka muddin ya kafa dokarshi, mutun ne wanda in yayi gyaran murya koda kajin gidanshi suke nitsuwa, Allah ya shirya mishi yaranshi yayinda Aminu shine babban d'anshi kuma shine ya gado zafin zuciyar Malam Umar da kafiyarsa kab, sabanin Baba Malam shi kuma yanada tsananin nitsuwa da kauda kai da hak'uri ammanfa in aka k'ureshi yafi Malam Umar zafi da tsanani, Mahaifinsu ya rasu, shiyasa suka k'auro suka dawo Gombe sun dawo gombe ba juyama Allah yayiwa Malam Umar rasuwa daga nan komai na kula da gidan ya dawo hannun Aminu da baba malam da Ahmad. Goggo Maryam kuwa tana dukku gidan mijinta. Hajia Aisha Mamy kenan itace matar Malam Bashir ta forko wacce sukayi auren lalle da lalle, wacce Allah ya azurtasu da d'ansu Ahmad daga shi kuma bata sake samun haihuwaba. Ahmad nada shekaru goma a duniya, lokacin su Malam bashir suna shiga k'auyukan k'abilun gombe da kewaye suna da'awa, kuma Alhamdulillahi kafurai sunata musulunta suna shiga addinin musulunci sosai, a cikin hakane sukaje wani yanki kaltingo na k'abilun tangalu nan suka musuluntar da mutane da dama maza da mata a cikinsu akwai wacce ta musulunta da sunata Soro data musulunta ta zab'i a saka mata Halima, sosai iyayen Halima suka tada hankalin kan musuluntar da tayi daga bisani sukayi mata barazar zasu kasheta, ganin ta kafe ne kuma bata tsorita ba sai suka koreta, to daga ranar tayi ta bibiyar malamai mata dasu Malam Bashir Sulaiman Dukku ke zuwa dasu yin da'awa, dole suka d'auketa suka dawo da ita cikin Gombe suka ajiyeta cikin gidan da aka gina da isilamiya domin irinsu, nan ta zauna tayi ta karatunta daga bisani akazo batun aure nan ta kafa ta tsare tace ita Malam Bashir takeso. Allah yayi da rabo a tsakani cikin k'ank'anin lokaci Malam bashir ya sanarwa iyayenshi da matarshi Hajia Aisha duk sai suka bashi k'arfin guiwa dan dama ita Mamy tana buk'atan ya k'ara aure. Nanfa akayi auren Baba Malam da Halima Mama kenan, inda ya sai gida a ceceniya ya ajiyeta a nan sabida lokacin suna Dukku ya zama matanshi biyu, in yazo Gombe ga Halima amarya in ya koma dukku ga Mamy uwar gida mace mai tarin hak'uri da tawakkali. Zuwan Halima gidan keda wuya Allah ya azurtasu da haihuwa yau da gobe jibi da gata. saida ta haifi 'yara shida Habu, Maryam, Zaleeha, Zakariyya, Ziyada , kana autarsu Zahira . Zaleeha na yawan bin Baba Malam suje Dukku dan Mamy na matuk'ar sonta da kula da ita shiyass Zaleeha da Habu da Maryam sun zauna a Dukku sosai sun samu inƙantacciyar tarbiya a wurin Mamy kasan cewar haihuwar kunika Mama takeyi sai hakan ya zame mata kamar hutune da sauk'inta, Mamy kuwa tasha wuyan yaran nan tamkar itace ta haifesu da cikinta dan ko Ahmad bata sha wuyan rainonshi ba kamarsu Habu Maryam Zaleeha kuma yaran suna masifar sonta hakan itama take matuƙar sonsu, Zakariyya nada wata biyu ta samu cikin Ziyads, so randa ta haifi Ziyada a ranar aka yaye Zakariyya daga nan Baba Malam ya d'auki Zakariyya ya kaiwa Innanshi, lokacin babansu ma na raye daga nan Zakariyya ya zama tamkar d'ansu gata da sakalci dai na goyon kaka yana shanshi, sai dai duk jikokinsu sunfi son Ahmad da Aminu sai Zakariyyan da Maryam . Ziyada nada wata sha uku aka aihi Zahira auta daga nan ita itama haihuwar ta tsaya taci gaba da rainon Zahira da Ziyada wacce takeda nitsuwa irinta Maryam, daga baya ta kafa nacin a dawo mata da su Maryam shi kuwa baba malam yace takau bazai d'aukosu ba, amman zai kawo mata Habu tunda ba d'a namiji a gabanta ko d'aya, to fa shine mafarin fara gane halin Halima dama inkiyarsu ce Halima hali dubu babu na zab'e. bayan shekaru kad'an babansu Malam Bashir ya rasu daga nan Malam Umar ya k'auro ya dawo cikin gombe a gidanshi daya gina a Fantami yaso ya d'auko inna amman sai tak'i a cewarta bata son tayi nesa da d'iyarta Goggo Dada, lokacin kuwa tuni Ahmad baya k'asar yana k'asar Italy inda nan yayi karatunshi har ya zama cikekken pilot Aminu kuwa kuwa zama babban soja, koda Baba malam ya sanarwa innansu cewa zai k'aura shima zai koma cikin gombe fir tak'i da kyar dai da sud'in goshi ya lallab'ata suka k'auro suka dawo gombe nan suka zauna a nan gidanshi na ceceniyan bayan shekaru kamar biyar lokacin tuni Ahmad ya taka k'asa yayi kud'i sosai, Ahmad yana tsananin son mahaifinshi da k'annenshi baya son duk wani abu da zai tab'a mutuncin mahaifinshi yana tsananin tausayawa da son Mamynshi su Zaleeha kuwa jinsu yakeyi har cikin k'ok'on ranshi kusan shine yake musu komai na karatunsu. To sanadin hakane Halima ke d'an ragarwa Mamy kisan mummuk'en da takeyi mata, musamman da taga Ahmad ya sayi k'aton fili a New G. R. Aka tsantsara musu gida na gani na fad'a suka koma can kuma yana yiwa yaranta hidima. Inna kuwa tace ita dai a barta a ceceniya ita da Zakariyyanta a kuma bata Ziyada acewar yanayin unguwar yana tuna mata k'auyensu badon Mama tasoba sai dan Dole Zoyada ta koma gaban fitinanniyar tsohuwar injita da faɗi. Ana cikin haka Baba Malam ya had'a auren Aminu da Maryam dan lokacin Malam Umar ya rasu to yana son k'ulla igiyar zumunci tofa anan Halima ta fito da asalin halinta. Gashi zuwa lokacin iyayenta duk suna ji da ita tunda yanzu tanada wadata sanadin Ahmad kuma tana kasuwanci in zataje garinsu zai bata kud'i ta musu ihsani. Sosai taso ta zuga Maryam sai kuma tayi rashin sa'a Maryam rainon Mamy ce sai tabi umarnin mahaifinta. Daga nan kuma ta tsananta bak'in halinta Yanzu su Zakariyya da Zahira da Ziyada ne suka rege suke karatu Habu da Maryam da Zaleeha duk har aiki sukeyi. kab cikin yaran kuma Zahira ce munafukar da ta gado bak'in halin uwartasu da k'abilancin ta. to kuma Zaleeha na shiri da Zahiran fiye da Ziyada dan ita Ziyada irin masu shiru-shiru d'innan ne sosai, kasan cewar duk yaran da gefen babansu suke kama shiyasa sukayi kyau mai d'aukar hankali. Shiyasa kuma Halima take jin kanta da yaran take nunawa Mamy rashin d'a'a dan ma yaran basu biye mata. To yanzu kuwa Zaleeha ce kan ganiyar budurci tana shawaginta son ranta, tana had'a gwara kan maza a cewarta sai ta duk mai nuna mata barazana da kuɗi ko wani matsayi baya ranta duk kud'in na miji baya gabanta. Tace ita soyayyar gsky zatayi duk wanda zata aura take kuma son ya mata tafi son miji jarumi mai tausayi da taumakon na ƙasa dashi kana har ranta tana son kekyawan miji bata son mummunan miji a ranta Wannan kenan sune ahlin Zaleeha... *** Ita kam Zaleeha sam bata wani damu da k'a'idar da aka bataba don ganin tsawon lokacin da aka bata takeyi kamar bazai zoba, so
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148