Skip to content

Chapter 135

Chapter 135

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,202 words 0 views Progress saved
Download Book

A can New G.R.A kuwa kasan cewar yau girkin Mamane dan Mamy yau ta ƙare kwana biyunta. Suna dawowa sallan isha Ahmad da Habu sukayi cikin gida. Da sauri Habu ya tsaya, cikin mamaki yace. "Ya Ahmad kalli can." Da sauri Ahmad ya isa wurin da Habu ke nuna mishi, ganin kayan lefen Zaleeha ne da aka kawo jiya watse aƙasa, setin gaba ɗaya akwatuna 30 dasu tarkacen gishiri da goro duk an watsosu waje, cikin tsananin Al'ajabin halin Mama da tsaurin ido irin nata yace. "Innalillahi! Habu tayani mu kwashesu, tunkan Baba Malam yazo yagani, nasan bazaiji daɗi ba aransa ba." Da sauri suka fara tattara kayan, sai kuma duk suka tsaya tare dayin shiru, sakamakon jin muryar mahaifinsu ta window parlour'n shi. "Ku barsu a wurin ko tsinke kada ku ɗaga, ku wuce ku bar wurin." Shiru sukayi cikin tsananin tarin damuwa dan dagajin muryar Baba malam yana cikin tsananin baƙin ciki, muryarshin ce ta katse musu tunanin da sukeyi. "Ku bar wurin ko nace!." ya ƙarishe maganar cikin bada umarni irin na fusata. Da sauri sukace. "Toh". sannan suka juya, kowa ya nufi ɗakin mahaifiyarshi. Gefen Mamy Ahmad ya zauna cikin ƙunan rai yace. "Please Mamy kije ki bawa Baba malam haƙuri, naga ranshi ya matuƙar ɓaci, kice yayi haƙuri ya barmu mu kwashi kayan, in yaso mushigo dashi nan ɗakinki." Murmushi Mamy tayi tare da cewa. "Hmmm Ahmad ai wannan ba hurumi na bane, ku bar kayan kamar yadda ya umarceku, Mamanku ta zauna da Malam kusan tsawon shekaru 30 kenan yau, amman har yau bata san waye Malam ba, bata taɓa ƙureshi ba, amman da dukkan alama yau zata san kaɗan daga cikin halaiyarsa, idan ransa ya ɓaci, shi acikin ruwan sanyi zai dafata." Jin haka yasanya Ahmad cewa. "Hmmm kai Mama tanada matsala Wallahi, mutum duk haƙurinshi sai ta ƙureshi." "Kaje kaci abinci ka dena zama da yunwa." Mamy ta umarceshi cikin son kauda zancen, kasancewar bata son tayi mgnar kishiyarta, dan wannan shi ke ɓata alaƙar zuciyar yaro da matar ubanshi. Ƙarfe tara dai-dai Mama ta shiga parlour'n Baba Malam, tare da yin sallama can ƙasan maƙoshi, ta yadda shi baima jitaba. A kan kujera ta sameshi zaune ya zubawa TV idanu yana kallon BBC News. Kan dinning table ta kai dubanta, gani tayi yanda ta ajiye abinci, yana nan ayanda yake, da alama babu wanda ya taɓa ko food flask ɗin bare akai ga ci, juyowa tayi ta maida kallonta kan fuskarshi da ta ɓoye ɓacin ransa, ta sani koda bazaici abinciba to tabbas zaisha tea, dan haka taku uku zuwa biyar ne yakaita gaban dinning area, cup ta ɗauka sannan ta haɗa mishi tea kamar yadda ta saba, a hankali tazo ta ajiye mishi cup ɗin a kan table ɗin dake gabanshi, wanda yawanci nan yake miƙe sawunshi idan yana zaune akan kujera. danne ɓacin ranta tayi dan yanzu so take ta gwada kirsa tunda taga hayagagar bata kamashi, gefenshi ta zauna tare da cewa. "Ga tea ɗinka nan nahaɗa ma kada yayi sanyi." shiru yayi baice ƙala ba, ganin yadda yayi kamar babu wani mahaluƙin dake kusa dashi, yasanya cikin tsareshi da ido taƙira sunanshi. "Malam!." Baima juyo ya kalleta ba bare tayi zaton ko zai amsa mata, saima kaɗa ƙafafunshi da ya farayi a hankali. shi kuwa wani irin tafarfasa zuciyarsa keyi, yadda tazo tayi ta mishi ihu da haushi a kanshi gaban yaranshi da uwar gidanshi, shine ke ƙara ɓata masa rai, sam bata sa hankali da nutsuwa cikin lamuranta. Kusa dashi ta kuma matsowa tare da cewa. "Malam magana nake so muyi da kai fa." Bai bi ta kantaba bare ya saurareta saima ƙara volume ɗin TV da yayi. Cikin takaicin abin tace. "Ya kamata muyi magana ta fahimtar juna, a bani matsayina da damata a matsayina na uwar yarinya, ni nasan Zaleeha bata son wannan nakasasshen, ta tsaida gwaninta, harma ta bashi daman ya turo komai na aure, tunda dama iyayenshi kam sun zo kuma ka sansu ba baƙin fuska bane, d'an manya ne gaba da bayansa." Gum yayi mata tamkar dutse, ita kuwa sai surutai takeyi uwa aku, ganin an gama labaran ne ya sashi, miƙewa tare da kashe TV sannan ya nufi bedroom ɗinsa, da sauri tabi bayanshi tana Magana, bai kulata ba, haka ya shiga bathroom, ruwa ya watsa sannan yayi al'wala kana ya fito. A bakin gado ya sameta tana zaune, shi kuwa shirin bacci yayi kana yazo ya tsaya gefenta, da hannu ya nuna mata hanyar fita alamun ta fice mishi daga ɗaki, fuska a tsuke tace. "Muyi maganar tukun!." Fuska ya kuma tsukewa wanda saida taji gabanta ya ɗan faɗi, yayinda zuciyarta kuwa ta buga da ƙarfi, hanyar fita ya kuma nuna mata, da sauri tace. "Dan Allah, dan darajar ma'aiki kayi haƙuri ka buɗi baki muyi magana." Ido ya rumtse dan ya rigada ta haɗashi da Allah. Itama sanin in dai ta haɗashi da Allah zai saurareta ne ya sata yin hakan. cikin kaushin murya da haɗe fuska zuciya na tafasa murya a zafafe yace. "Kije ki kwashi kayan da kika watsar ɗin ki maidasu ɗakinki ki ajiyesu yadda kika samesu." da sauri tace. "Dare yayi fa." A kausashe yace. "Baza kuma su kwana a waje ba." Cikin sanyin jiki tace. "To bari in ƙira Habu yazo ya kwashesu." A ƙufule yace. "Waya fito dasu?." Kai ta juya tare da cewa. "Ni ce." Cikin bada umarni yace. "To kije ki maidasu kizo muyi maganar." Bata da zaɓi dan ta san kaɗan kenan daga halinshi dole taje a daren ta kwashi kayan, ta maidasu cikin ɗakinta, tana gamawa a gajiye ta koma ɗakin nashi, a kwance ta sameshi cikin maida numfashi tace. "Na maidasu. Ka tashi muyi maganar." Kai ya jujjuya tare cikar haiba da isa da gidanshi yace. "Maganar ai na gamata babu wani wanda zan aurawa ɗiyata Zaleeha sai Saifuddeen, kuma babu wani mahaluƙin da ya isa hanani sai ubangijin daya halicceni!." Yana faɗin haka ya gyara kwanciyarshi tare da rufe ido alamun bacci zaiyi. Cikin tsananin takaici haɗi da ƙunci tace. "Ni kuwa Wallahi ƴata bazata auri gurgu kuma kurma ba, ɗiyata bazataje ta zama majinyaciya ina kallo da idona ba, sannan bazan taɓa bari takashe rayuwarta wajen kula da nakasasshe ƙaskantacce ba, Allah ya sauwaƙa ma, ni dai ajinina ban haifawa nakasashshe matar da zai aura ba ehe!!." Tana gama faɗin haka ta juya ta fita a fusace. Gyara kwanciya Baba Malam yayi tare da rufe idanunsa, sunayen Allah Kawai yake ambata acikin ransa. *** Washe gari kuwa Zaleeha daga gidan hajja Inna ma'aikatarsu ta nufa, bayan ta gabatar da shirinta na mushaƙata kai tsaye gidansu kuma ta nufa. A harabar gidan tayi kiciɓis da ya Ahmad, cikin shaƙuwarsu ta nufi inda yake, da alamun cewa shima yanzu shigowarsa cikin gidan. hannunshi ta kamo tare da cewa. "Ya Ahmad nayi kewarku kwana biyu bana nan ko kuyi cikiyata." murmushi yayi tare da cewa. "Muma munyi kewarki, kin san inata shirin tafiyarmu ne, naso in wuce da Lubna amman Mamy tace wai in bar miki ita." tsalle tayi cikin jin daɗi tace. "Yessss! My mamy kai amman ko naji daɗi sosai!!." Murmushi yayi tare da cewa. "Ato ai dama amare yan jin daɗine." Sam bata kawo komai

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148