Skip to content

Chapter 23

Chapter 23

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,203 words 0 views Progress saved
Download Book

d'in. da yawa cikin gida suka shisshiga, haka ma su Saifuddeen da Salisu tare da Mudassir da suka samu a masallacin, suna shiga Ummi suka gaida kana suka wuce d'akin Saifuddeen inda suna shiga wuta ta dawo, dan haka cikin farin ciki suka zauna Rahma da kanta ta kawo musu abincin suma tea sukace zasu sha dan haka ta kawo musu kana ta aika musu ruwan sanyi soyayyan doya da kwan sukaci suna korawa da ruwan tea da yaketa k'amshi, daga nan kuma cikinsu ya cika, suna cikin hira sukaji an kira sallan isha, kusan a tare suka mik'e sukaje suka sabunta al'wala a tsakar gidan kana suka nufi woje suna fita suka shiga sahu, bayan anyi isha sai kuma aka fara yin sallan asham. Suma su Ummi suka sabunta al'wala kana suka fara sallan. Bayan an idar duk an fiffito ne sai Bappa Ali yacewa Saifuddeen zasufa tafi masallacin fada yanzu zasu fara tafsir d'in dan takwas ta kusa. Mudassir ne ya kalllesu kana yace, "Bari inje in cewa Ummi tafa ajiye mana jolof d'innan in mun taso tabsir zamuci dan ni in nazo konciya sai naci abinci." dariya sukayi mishi kana Warisu dake bayansu yace. "Anya ko kai bafullatanine Mudassir dan gaskiya fulani basu da yawanci." Ahmad ne da shima yanzu ya iso yace. "Yoh ai shi iyamburi ne bakaga yadda yayi k'atoba." shiko Mudassir shafa cikinsa yayi tare da cewa. "Me yafi raina." dariya suka kumayi sai Saifuddeen da yaketa murmushi sai kuma Warisu ya kalli Saifuddeen kana ya kallesu tare da cewa. "Ni ai ko dan kar inyi k'aton ciki zan yiwa kaina k'aidar ci abinci, wlh da nasan yadda zanyi in koma kamar Saifuddeen da nayi na koma, kalleshi komai na jikinshi dai-dai da shekarunsa, shiyasa yake tafiya da kenshi da k'uruciyarshi, wlh koda namiji d'an uwanshi in ya ganshi sai ya kuma kallonshi in ka ganshi kamar balarabe ko ba indiye." cikin kauda kai Saifuddeen ya d'an shafa suman kanshi tare da mishi alamar. "Kai Warisu in naga wani kyau." daga nan suka shiga cikin gida bisa taburmar da Ummi ke zaune suka zauna bayan sun gaisane ta kallesu cikin kula tace. "Ya kamata ace iwar haka kuna wurin tafsir, ku rage yawon dare kun san wannan wata ta musammance ga musulmai." mik'ewa sukayi da sauri sai kuma Mudassir yace. "Yauwa Ummi a ajiye mana taliyar nanfa in mun taso zamuci." cikin jin dad'in had'in kan yaran tace. "Ba matsala sai kun dawo." daga nan suka juya har sunje bakin k'ofa tace. "Ahmad kwana zamuyi ko." cikin tsiya wasu Salisu yace. "No Ummi ba kwana zanyiba ai inada yan rakiya." yana fad'in haka sukayi ca a kanshi wai bazasu rakashi ba. ita kam Ummi da murmushi ta rakasu. Bayan sunje suka samu anata taruwa manya da yara da dottab'ai duk an cika can ta wojen gidan sarki kuma wani rumfane da mata ke taruwa a ciki. Suna shiga duk sukayi gefen da aka ajiye mazaunin malam, wuri d'aya suka zauna yayinda tuni, Saifuddeen kuma ya zagaya bayan Bappa Ali da alarammanshi Abdurahman gyara tsayuwarshi yayi gefen d'an agajin dake bayansu Bappa Alin. shi kuwa Bappa Ali da alarammanshi gyara abin sautin mgnar dake gabansu sukayi tare da d'an sunkuyawa kan Qur'anen dake bud'e a gansu inda bana zasuyi tabsir d'in ```suratul Maedah.``` shi kuwa Saifuddeen ta cikin glass d'in table d'in gabansu yake ganin fuskar Bappa Ali ras har yadda zai gane motsin bakinshi da abinda yake fad'in. dan haka ya maida hankalinshi bisa bakin bappan nashi. Bayan anyi addu'a an bud'e taro kana ya kuma jero addu'o'i. gyara zamanshi yayi kana cikin sakekken sauti yace. "Alhamdulillahi Allah ya kawomu watan Ramadan tun kafin mu shiga cikin tafsirin namu zan d'anyi tsokaci ga yan kasuwanmu." sai ya kuma d'ago kanshi ya d'an kalli taron jama'ar dake cike da masallacin ido ya d'an zuba musu tare da ci gaba da cewa. "Shi watan Ramadan wotan rahama ne da jink'ai da kuma tausayin juna. Amman abin takaici abin haushi tun gabanin zuwan watan zakaga wasu musulman suna k'arawa kayayyakin sana'arsu kud'i domin suyi tsada, maimakon su rage musu k'ud'in domin tausayawa juna da tallafawa tallakawa." sai ya kuma tsagaita. shi kuwa Saifuddeen tuni yake fassara abinda yake fad'in da body language yadda masu matsalar ji zasu iya gane komai a sau k'ak'e. cikin nitsuwa Bappa Ali yaci gaba da sharan fage akan bayanin Ramadan inda yake cewa. "Yana daga cikin fa'idojin azumi, Azumi na sanya bawa godewa ni'imomin Allah mad'aukaki. Azumi na taimaka wa bawa gurin barin abinda Allah ya haramta. A cikin azumi akwai tsanani ga shaid'an da raunatashi. Sannan Azumi na karya k'arfin sha'awa mu samman ga matasanmu. Azumi na gadar da samin rahamar Allah da jin k'ansa. Azumi na koyarwa bawa tsoron Allah, da tausayin na k'asa dashi. Azumi na tafe da wasu falaloli na musamman, da yawa sai a azumi suke samun dama da k'arfin guiwar shiga itikafi. Itikafi shine keb'ewa ko zama cikin masallaci domin ibada. Mafi falalan itikafi lokacin goman k'arshe, yin itikafi sunnace mai k'arfi yin itikafi a masallacin jumma'a idan kwanakin da za'ayi sun had'a da jumma. Idan zaka shiga itikafi zaka shiga kafin fad'uwar rana a daren da kake son fara itikafin. Mustahabbi ne ga maiyin itikafi ya keb'ance da ibadu yawan salloli, zhikiri, addu'a, karatun Qur'an, tuba, istik'afari, salatin annabi, da dai sauransu domin nemar kusanci da yardar Allah. Mai itikafi idan ya gama kwanakin da yayi niya zai fitane bayan fad'uwan rana. Baya halatta ga mai yin itikafi ya fita zuwa duba mara lfy da kusantar iyali. Amman mai itikafi zai iya fita domin abinda ya zama dole kamar buk'atu irin na d'an adam, kamarsu zagayawa bayan gida da neman abinda zaici. Idan rashin lfy ko jinin haila suka zowa mai itikafi, zasu fita idan ya samu sauk'i ko ta samu tsarki sai a dawo." gaba d'aya wurin anyi tsit ana sauraron bayanin malam Alin. daga nan ya d'anyi k'arin bayani game da azumin kanshi inda yake cewa. "Abubuwan k'i ga mai azumi, Kaiwa matuk'a gurin kurkuran baki da shak'a ruwa. Sumbatar iyali da makamancin haka ga wanda baya iya mallakar kanshi. D'andanon abinci badon buk'ata ba. B'ata lokaci kawai wasannin banza da surutai marasa amfani. Zarcewa da azumi kwana biyu zuwa sama." A k'arshe yace a tak'aice abinda ya kamata ga mai azumi ya kiyaye harshensa daga dukkan maganganun banza zagi annamimanci giba isgilanci da sauransu kodako a social media ne. Daga nan suka shiga cikin tafsir d'in nasu gadan-gadan, mutane sun nitsu wurin jin fad'in allahu subahanahu wata ala. K'arfe tara dai-dai aka tashi, Saifuddeen ne ya karb'i d'an jakar Quran d'in bappan nashi kana suka wuce gida da abo kanshi, suna shiga su suka wuce d'akinshi shi kuwa ya bi bayan bappa Ali da jakarshi saida suka shiga ya bashi sannan ya juyo ya nufi side insu, murmushi yayi ganin suna fito daga d'akinshi suna zuwa tsakar gida Ummi kuwa taburma ta shimfid'a musu kana ta zuba musu zazzafan colof d'inan a tire tare da basu forks Mudassir ne ya amshi cokulan ya raba musu kana suka fara ci, Raliyya kuwa babban kofi ta d'auka ta d'ebo musu ruwan randar d'akinshi ta kawo musu, shi kam bai kula abincinba suma basubi ta

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148