Chapter 23
Chapter 23
d'in. da yawa cikin gida suka shisshiga, haka ma su Saifuddeen da Salisu tare da Mudassir da suka samu a masallacin, suna shiga Ummi suka gaida kana suka wuce d'akin Saifuddeen inda suna shiga wuta ta dawo, dan haka cikin farin ciki suka zauna Rahma da kanta ta kawo musu abincin suma tea sukace zasu sha dan haka ta kawo musu kana ta aika musu ruwan sanyi soyayyan doya da kwan sukaci suna korawa da ruwan tea da yaketa k'amshi, daga nan kuma cikinsu ya cika, suna cikin hira sukaji an kira sallan isha, kusan a tare suka mik'e sukaje suka sabunta al'wala a tsakar gidan kana suka nufi woje suna fita suka shiga sahu, bayan anyi isha sai kuma aka fara yin sallan asham. Suma su Ummi suka sabunta al'wala kana suka fara sallan. Bayan an idar duk an fiffito ne sai Bappa Ali yacewa Saifuddeen zasufa tafi masallacin fada yanzu zasu fara tafsir d'in dan takwas ta kusa. Mudassir ne ya kalllesu kana yace, "Bari inje in cewa Ummi tafa ajiye mana jolof d'innan in mun taso tabsir zamuci dan ni in nazo konciya sai naci abinci." dariya sukayi mishi kana Warisu dake bayansu yace. "Anya ko kai bafullatanine Mudassir dan gaskiya fulani basu da yawanci." Ahmad ne da shima yanzu ya iso yace. "Yoh ai shi iyamburi ne bakaga yadda yayi k'atoba." shiko Mudassir shafa cikinsa yayi tare da cewa. "Me yafi raina." dariya suka kumayi sai Saifuddeen da yaketa murmushi sai kuma Warisu ya kalli Saifuddeen kana ya kallesu tare da cewa. "Ni ai ko dan kar inyi k'aton ciki zan yiwa kaina k'aidar ci abinci, wlh da nasan yadda zanyi in koma kamar Saifuddeen da nayi na koma, kalleshi komai na jikinshi dai-dai da shekarunsa, shiyasa yake tafiya da kenshi da k'uruciyarshi, wlh koda namiji d'an uwanshi in ya ganshi sai ya kuma kallonshi in ka ganshi kamar balarabe ko ba indiye." cikin kauda kai Saifuddeen ya d'an shafa suman kanshi tare da mishi alamar. "Kai Warisu in naga wani kyau." daga nan suka shiga cikin gida bisa taburmar da Ummi ke zaune suka zauna bayan sun gaisane ta kallesu cikin kula tace. "Ya kamata ace iwar haka kuna wurin tafsir, ku rage yawon dare kun san wannan wata ta musammance ga musulmai." mik'ewa sukayi da sauri sai kuma Mudassir yace. "Yauwa Ummi a ajiye mana taliyar nanfa in mun taso zamuci." cikin jin dad'in had'in kan yaran tace. "Ba matsala sai kun dawo." daga nan suka juya har sunje bakin k'ofa tace. "Ahmad kwana zamuyi ko." cikin tsiya wasu Salisu yace. "No Ummi ba kwana zanyiba ai inada yan rakiya." yana fad'in haka sukayi ca a kanshi wai bazasu rakashi ba. ita kam Ummi da murmushi ta rakasu. Bayan sunje suka samu anata taruwa manya da yara da dottab'ai duk an cika can ta wojen gidan sarki kuma wani rumfane da mata ke taruwa a ciki. Suna shiga duk sukayi gefen da aka ajiye mazaunin malam, wuri d'aya suka zauna yayinda tuni, Saifuddeen kuma ya zagaya bayan Bappa Ali da alarammanshi Abdurahman gyara tsayuwarshi yayi gefen d'an agajin dake bayansu Bappa Alin. shi kuwa Bappa Ali da alarammanshi gyara abin sautin mgnar dake gabansu sukayi tare da d'an sunkuyawa kan Qur'anen dake bud'e a gansu inda bana zasuyi tabsir d'in ```suratul Maedah.``` shi kuwa Saifuddeen ta cikin glass d'in table d'in gabansu yake ganin fuskar Bappa Ali ras har yadda zai gane motsin bakinshi da abinda yake fad'in. dan haka ya maida hankalinshi bisa bakin bappan nashi. Bayan anyi addu'a an bud'e taro kana ya kuma jero addu'o'i. gyara zamanshi yayi kana cikin sakekken sauti yace. "Alhamdulillahi Allah ya kawomu watan Ramadan tun kafin mu shiga cikin tafsirin namu zan d'anyi tsokaci ga yan kasuwanmu." sai ya kuma d'ago kanshi ya d'an kalli taron jama'ar dake cike da masallacin ido ya d'an zuba musu tare da ci gaba da cewa. "Shi watan Ramadan wotan rahama ne da jink'ai da kuma tausayin juna. Amman abin takaici abin haushi tun gabanin zuwan watan zakaga wasu musulman suna k'arawa kayayyakin sana'arsu kud'i domin suyi tsada, maimakon su rage musu k'ud'in domin tausayawa juna da tallafawa tallakawa." sai ya kuma tsagaita. shi kuwa Saifuddeen tuni yake fassara abinda yake fad'in da body language yadda masu matsalar ji zasu iya gane komai a sau k'ak'e. cikin nitsuwa Bappa Ali yaci gaba da sharan fage akan bayanin Ramadan inda yake cewa. "Yana daga cikin fa'idojin azumi, Azumi na sanya bawa godewa ni'imomin Allah mad'aukaki. Azumi na taimaka wa bawa gurin barin abinda Allah ya haramta. A cikin azumi akwai tsanani ga shaid'an da raunatashi. Sannan Azumi na karya k'arfin sha'awa mu samman ga matasanmu. Azumi na gadar da samin rahamar Allah da jin k'ansa. Azumi na koyarwa bawa tsoron Allah, da tausayin na k'asa dashi. Azumi na tafe da wasu falaloli na musamman, da yawa sai a azumi suke samun dama da k'arfin guiwar shiga itikafi. Itikafi shine keb'ewa ko zama cikin masallaci domin ibada. Mafi falalan itikafi lokacin goman k'arshe, yin itikafi sunnace mai k'arfi yin itikafi a masallacin jumma'a idan kwanakin da za'ayi sun had'a da jumma. Idan zaka shiga itikafi zaka shiga kafin fad'uwar rana a daren da kake son fara itikafin. Mustahabbi ne ga maiyin itikafi ya keb'ance da ibadu yawan salloli, zhikiri, addu'a, karatun Qur'an, tuba, istik'afari, salatin annabi, da dai sauransu domin nemar kusanci da yardar Allah. Mai itikafi idan ya gama kwanakin da yayi niya zai fitane bayan fad'uwan rana. Baya halatta ga mai yin itikafi ya fita zuwa duba mara lfy da kusantar iyali. Amman mai itikafi zai iya fita domin abinda ya zama dole kamar buk'atu irin na d'an adam, kamarsu zagayawa bayan gida da neman abinda zaici. Idan rashin lfy ko jinin haila suka zowa mai itikafi, zasu fita idan ya samu sauk'i ko ta samu tsarki sai a dawo." gaba d'aya wurin anyi tsit ana sauraron bayanin malam Alin. daga nan ya d'anyi k'arin bayani game da azumin kanshi inda yake cewa. "Abubuwan k'i ga mai azumi, Kaiwa matuk'a gurin kurkuran baki da shak'a ruwa. Sumbatar iyali da makamancin haka ga wanda baya iya mallakar kanshi. D'andanon abinci badon buk'ata ba. B'ata lokaci kawai wasannin banza da surutai marasa amfani. Zarcewa da azumi kwana biyu zuwa sama." A k'arshe yace a tak'aice abinda ya kamata ga mai azumi ya kiyaye harshensa daga dukkan maganganun banza zagi annamimanci giba isgilanci da sauransu kodako a social media ne. Daga nan suka shiga cikin tafsir d'in nasu gadan-gadan, mutane sun nitsu wurin jin fad'in allahu subahanahu wata ala. K'arfe tara dai-dai aka tashi, Saifuddeen ne ya karb'i d'an jakar Quran d'in bappan nashi kana suka wuce gida da abo kanshi, suna shiga su suka wuce d'akinshi shi kuwa ya bi bayan bappa Ali da jakarshi saida suka shiga ya bashi sannan ya juyo ya nufi side insu, murmushi yayi ganin suna fito daga d'akinshi suna zuwa tsakar gida Ummi kuwa taburma ta shimfid'a musu kana ta zuba musu zazzafan colof d'inan a tire tare da basu forks Mudassir ne ya amshi cokulan ya raba musu kana suka fara ci, Raliyya kuwa babban kofi ta d'auka ta d'ebo musu ruwan randar d'akinshi ta kawo musu, shi kam bai kula abincinba suma basubi ta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148