Skip to content

Chapter 97

Chapter 97

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,202 words 0 views Progress saved
Download Book

cewa. "Baki isaba in sha Allah sai na aureki, sai na zama mijinki." wani irin zafi taji kalamanshi na gasa zuciyarta cikin hatsala ta d'ago hannu ta yarfa mishi mari tare da tureshi gefe ta wuce tayi cikin gida. Ya Ameenu kuwa yana sama yanaji da ganin duk abinda sukeyi. Ganin ta zubawa Raveel marine ya sashi fitowa ya nufi parlour k'asa da tsananin sauri har yana take steps d'in bibbiyu uku-uku dan azabar zuciya da zafin raina, tabbas yanzu ya yarda muddin akabar Zaliha zatayi abinda taga dama. Tana isowa parlour yana sauk'owa, Da sauri ta tsaya tare da zaro ido ganin ya nufeta gadan-gadan. Yana isa inda take ya ware tafin hannunshi cikin zafin rai ya fara yayyarfa mata wasu gigitattun tagwayen marukan da suka sata ganin start's suna yawo kana kunnenta ya bada sautin kauuuu. kafin ta dawo daga gigicewar data shiga ta kuma jin wasu tsinannun marukan da suka sata cilla wani irin zazzafan k'ara mai gigita duk wanda ya jita. "Wayyo Maryam Ya Ameenu zai kasheni." shi kuwa Aminu cikin haki yake ci gaba da yayyarfa mata mari yana mai cewa. "Ae gwara ki mutu kowa ya huta, tunda fand'arewa kikeso kiyi, Yanzu kinfi k'arfin mata sai maza. Ashe har kin kai matsayin da zaki d'aga hannunki ki mari d'a namiji, dan yace yana sonki." Raveel kuwa tunda ta kwad'a mishi mari ya sunkuyar da kanshi k'asa, saida yaji ta saki ihunne yayi sauri ya kutsa kai cikin gidan. Maryam kuwa tana isowa parlour sai ta koma gefe ta zuba musu ido. Raveel d'inne yayi k'arfin halin kamo hannun ya Ameenu tare da cewa. "Dan Allah dan darajar iyayenmu kayi hak'uri ya Ameenu mu bita a hankali please kada ka daketa." Ita kam Zaliha tuni tayi bedroom d'in Maryam a guje tana shiga tayi fad'uwan 'yam bori bisa gadon kana ta saki wani marayan kuka. Shi kuwa Ya Aminu bisa kujera ya zauna tare da nunawa Raveel kujera alamun ya zauna. Bayan sun zaunane ya kalli Raveel cikin sanyi da tafasan zuciya yace. "Raveel kayi hak'uri da abinda Zaleeha tayi maka, In sha Allah daga kanka bazata sake gigin marin wani d'a namiji ba." Cikin sanyin Raveel yace. "Ba komai ya Aminu, Allah ya tabbatar mana da al'khairi." Amin Amin yace kana yayiwa Raveel rakiya har bakin gate. Ita kuwa Maryam ganin mijin nata ya fitane yasa ta juya a hankali tabi bayan k'anwar tata, tana shiga ta maida k'ofar ta rufe. Da sauri ta haura kan gadon cikin tausayawa tace. "Zaleeha, kiyi hak'uri kiyi shiru kukan ya isa haka please kinga ga Ayman ma ya fara kuka, Gaya min make faruwa?." A hankali ta mirgino tare da kife kanta bisa cinyar maryam cikin tsananin kuka tace. "Raveel ne ya tura iyayensa wurin Baba malam wai suna neman izinin zance. yau tunda safe ya aika ya Habu ya kirani ina shiga ya hauni da fada. Wai zan maidashi mutumin banza ya za'ayi inyi ta turo mishi dattawan mutane. A karshe yace dole cikin manema in fidda goni ko shi yamin zabi, yace min wai karfa inga yayi shiru yana sane k'a'idar da ya bani saura wata d'aya". Numfashi ta sauk'e a hankali tace. "To ke Zaliha auren ne bakya so?." cikin shesshek'a da miryar tausayi tace. "A a ni bance bana son aureba." Cikin kula tace. "To bakida masoya ne?." Still hawaye na zuba tace. "Ina dasu amman ni bana sonsu." Gyara zamanta tayi tare da cewa. "To wa kike so?." hannunta tasa duka biyu ta matse kanta da k'arfi cikin rauni da tashin hankalin dan a duniya tasan wannan amsar itace tafi komai wahal da ita cikin muryar kuka tace. "Adda Maryam ya kike min tambaya kamar bakisan komai a kanshi ba?." cikin sin cire mata wannan tunanu Maryam tace. "Shi waye ɗin kenan?." Kai tajujjuya kana tace. "Shi nakeso! Shine farin cikin rayuwata, in dai ba shine yace baya sonaba to bazan auri kowaba, ya sadaukar da rayuwarshi a kaina, ya kareni a lokacin da nafi tsananin buk'atar neman kariya, Ya zama garkuwata ya tsare min kimata ya bada ranshi da lfyarshi a kaina, ina sonshi." Sai kuma ta tashi zaune ta rik'o hannayen yayar tata cikin zubda k'walla murya na rawa tace. "Ina sonshi, wlh ina sonshi bazan iya son wani d'an namiji ba in ba shiba." Cikin kad'uwa maryam tace. "Wai waye ne?." Da k'arfi tace. "Ban saniba." Cikin mmki Maryam ta zaro ido woje kana tace. "Me sunanshi? Ina gidansu yake? Me sana'arsa?." Nanma kuka tasa tare da cewa. "I don't know." Zuwa yanzu abin ya fara bawa Maryam tsoro cikin tsoro tace. "To ina yake?." Da k'arfi tasa hannunta tana dukan kanta tare da cewa. "Ban sanshi ba, bai sanniba bansan ina yakeba bansan sunanshi ba. daga sau d'ayan dai dana tab'a ganinshi nanma gabanin magriba ne, to ban sake ganinshi ba." Nan ta k'ara bawa Maryam labarin had'uwarta da Dalla da yadda Saifuddeen ya taimaketa, dan ganin yadda Maryam ta nuna mata kamar bata gane waye take nufi ba, ta k'arishe mgnar cikin tsananin kuka tace. "Bansan ina zan sake ganinshi ba, ina sonshi, shine nakeso ya zama mijina wlh in ban aureshi ba bazanyi aureba, wlh in ban sake ganinshi ba zan haukace." Tsorone mai tsanani ya rufe Maryam, cikin zubda hawaye muryarta a sanyaye tace. "Innalillahi wa Inna'ilaihi rajiun, Zaliha ko dai kinyi gamone, kodai al'janine ba mutun ba?." da sauri ta durk'usa gaban yayartata cikin kid'ima da jujjuya Kai tace. "Mutum ne shi kamar ni, wlh ba al'jani bane shima d'an adam ne, na tabbata da al'janine da ya sake zuwamin koda a mafarki ne. Ni tsorona bansan wani hali yake cikiba, yana lfy ko sun illatashi." Wani nannauyan ajiyan zuciya Maryam ta sauk'e sannan tasa hannu ta share hawayenta kana ta sharewa Zaliha nata cikin fuskantarta da kyau a hankali tace. "Wannan zancen naki ba'ak'i ce dashi gaibuba, domin tatsuniya ce mai zaman kanta, zancene da hankalin bazai kamaba, Zaliha ki yarda al'janine ya taimaka miki, in ko mutunne to ya mutu." Wani irin zabura tayi tare da rushewa da kuka tana jujjuya kai tare da yarfa hannu take cewa. "Bai mutuba yana raye mutun ne ba aljanba ki gane mana ina jinshi a cikin duk wani bugun da zuciyata keyi." Ganin yadda ta gigicene yasa Maryam cewa. "Na game mutum ne kuma yana raye." Jin haka sai ta koma ta konta rubdaciki tana mai ci gaba da kuka. Ita kuwa Maryam da sauri ta d'iro daga kan gadon ganin Ya Ameenun yana tsaye a bakin k'ofa bisa dukkan alamu yaji duk batun da sukayi. tana isa inda yake kawai sai ta fad'a jikinshi tare da sakin sassanyan kuka. Da sauri ya tallabota dan a duniya Ameenu duk zafinsa baya son abinda zai tab'a mishi salihar matarshi mai tarin hak'uri da biyeyya. parlour ya fito da ita inda ya ruggumeta da kyau a jikinshi, jin haka yasa rauninta k'aruwa cikin rawar murya take cewa. "Shi kenan Ya Ameenu Zaleeha tayi gamo, al'jani ya shiga jikinta. Zai haukata min k'anwata ya Ameenu kuyi mata Ruqyah kada ya haukatata." ganin sosai take kukanne ya sashi d'ago kanta bakinsu ya had'e wuri d'aya wani irin zazzafan kiss yake mata wanda dole yasa tayi shiru, har saida yaga

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148