Chapter 134
Chapter 134
saikunji aranku cewa inama da ace bakuyi ganganci ƙulla wannan haɗin ba, saina sanya baƙinciki acikin zuciyoyinku, kuma sannan saina saku danasani marar yankewa, badai dani kuke wasan ba, hmmm Wallahi zakusan kun taɓo cikakkiyar ƙaɓila Batangali da surkin bateriya, akan auren nan babu wanda zan ɗagawa ƙafa!!." Tana gama faɗin haka ta juya fuuuuu kamar kububuwa tafice daga cikin falon na Baba Malam. Tana shigowa falonta ta soma afkawa Zahira ƙira, da sauri Zahira ta fito daga cikin ɗakinsu tana cewa. "Na'am Mama." A harzuƙe tace. "Zo zonan mu kwashi ƴan iskan kayayyakin nan mu watsasu waje, Wallahi bazasu kwanar min a ɗaki ba gayyar tsiya!." Da sauri Zahira tace "To." Nan suka shiga cikin ɗakin, haka suka dinga ibo akwatunan nan masu kyaun gaske, suna watsasu a tsakiyar farfajiyar gidan, wai don ma kasancewar Mama ƙaƙƙarfar mace ce shiyasa kab ta iya jidon manyan akwatunan, tanayin waje dasu harda su gishiri da goron bata bari ba, ranta yakai ƙololuwa wajen tafasa, jin kanta take dai-dai da uban kowa, jira take wani yace mata cass tuni zata sullesa tas. Saida ta gama watsasu a tsakiyar gidan, sannan ta koma cikin ɗakinta tana haki tamkar wacce tayi dambe ta gaji. Al'wala tayi sannan tazo ta kabbara niyar sallan magriba, wanda tuni lokaci ya ƙure mata, don har an riga da anƙirayi sallan isha. Zaleeha kuwa daga ma'aikatan nasu gidan kakar tasu ta koma, don dama kwana uku ta roƙi Baba Malam daya barta tayi, kuma da yake gidan mahaifiyarshi ce sai bai hanata ba. Kafin ma ta dawo tuni Ziyada ta gama haɗa musu komai na girki, tuwon ɗanyar shinkafa da miyar kase, tana ganin haka tace. "Ziyada ina Zakariyya kuma da tsohuwar nan sukaje, suka barki ke ɗaya a gida?." Cikin yanayin nutsuwarta irin na Maryam sak tace. "Sun tafi gidansu abokinshi Hayatuddeen." Tana warware naɗin gyalen hijabin dake jikinta tace. "Sun daɗe da tafiya ne?." Kai ta gyaɗa mata tare da cewa. "Eh tun da akayi sallan la'asar suka tafi." kai ta jinjina kana ta zaro wayarta ta danna ƙiran number'n Zakariyya. Shi kuwa Zakariyya lokacin suna parlour'n Ummi shida Hayatuddeen da Raliya, sunata tsiya wa Hajja Inna, ita kuwa Hajja inna sai surfa musu boris takeyi, Ummi kuwa sai nan-nan takeyi da hajja Inna dan taji dad'in zuwan kakar abokin autan nata, sosai takejin son tsohuwar a ranta, musamman yadda ta nuna tana masifar son Saifuddeen ɗinta. Ta tasashi gaba tana yabo harda kukanta tana. "Allah sarki bawan Allah, yaro kyakkyawa, Allah ya jarabceshi da nakasa, ganshi kuwa kamar balarabe." Sai kuma ta juyo ta kalli Ummy tare da cewa. "Wannan yaron naki abin sone da tausayawa ga ko wanne mutum ɗan Adam me imani, ki godewa Allah daya azurtaki da samunsa a matsayin ɗa, wasu suna can sun haifi lafi yayyun yara amman sai ki samu yaran munanane kamar kashin dare, kinga ko gwara miki kyakkyawa fari ƙal nakasasshen." Hayatuddeen ne yayi dariya sosai tare da cewa. "Kai tsohuwar nan munana sun boni a wajenki." Zakariyya ne ya zaro wayarshi dake suwa, wacce take cikin aljihun wondonshi yana cewa. "Itafa sam bata son mummunan mutum, in taga kyakkyawan mutun kuma wai ji take kamar ta dawo dashi ɗanta." Dariya sukayi baki ɗaya, kana shiko Zakariyya ya amsa kiran Zaleeha tare da cewa. "Hello Adda Zalees ya akayi ne?." Sai ya kuma yafito Hayatuddeen tare da mishi alamun ga mutuniyarshi fa. amsar wayar yayi ya kara a kunne tare da cewa. "Adda Zalees nayi fushi dake muka dawo ko kizo ki duba kyakkyawan hammana da jiki ko." Murmushi tayi tare da cewa. "Afwan autan gidansu." da sauri yace. "No autan Ummi dai zakice, gidanmu kam ai kwanannan ma Hamma na zai fara ƙenƙesa mana yara sabbin zubi, ƴan yayi kuma kyawawa, irin yaran da Hajja inna ke masifar so." Ƴar dariya tayi tare da cewa. "To aku sarkin zance, please ka cewa Zakariyya su biya Abba bakery ya saya min pizza dan Allah." Da sauri yace. "To ba matsala karki damu zan bashi abin daɗi ma ya kawo miki, cikin na Hamma na zan ɗiba miki." Da sauri tace. "A a ni dai pizza kawai nake so." Bai kulataba ya katse ƙiran. sannan ya amshi kular da Raliya ta haɗa musu tsarabar Kai kayan lefen jiya." Daga nan suka miƙe zasu tafi, har sun kusa fita daga parlour Hajja Inna ta juyo ta kalli Saifuddeen murmushi ya mata, haka itama murmushin tayi mishi sannan ta kalli Ummi cikin halin tsufa tace. "Kin ga ƴata kada ki yarda ki bari wannan kyakkyawan ɗan naki ya auro miki mummunar surka, in kuwa kika bari ya auro miki mummunar surka, to shike nan ya ɓata miki wannan kyakkyawar zuriyar taki, dan tabbas dole wata rana sai ta haifo muku mai kama da ita, dan ni dai anmin na gani, yanzu in kika kalli Zahira zakice ba jinin ahlina bane dan ita kamannin dangin uwarsu tayi yo." Zakariyya ne ya tura baki tare da cewa. "Kefa kince baki da goni a duniya sai mai kyau, to sam gigin tsufarki baya gaya miki gsk, ya zaki rinƙa sarata ina ji, aikin kawai." Dariya sukayi dukansu ganin yadda ta kamo hannun Zakariyya tana cewa. "A a kada kaji haushi shalelena, ai kai sak da kakanka baban babanka kakeyi, shiyasa kai da Ahmad kuke tsananin kama, Zaleeha da Ziyada kuwa dani suke kama, bakaga Zaleeha ko gashi irin nawa ta gado ba?." Janye hannunshi yayi tare da kunna machine ɗinsa, kana ya amshi kular da Hayatuddeen ke miƙo mishi ya saka a cikin ɗan kondon dake gaban machine ɗin. Sai ya kuma kallon Hayatuddeen dake miƙo mishi 10k kana yace. "Ga tukuicinmu na jiya." Dariya Zakariyya yayi tare da cewa. "Kace abin namu ne babu ƙaranci, ashe ko zamuyi casu a bikinga." Sosai Ummi ke murmushi dan Zakariyya sak autan tane da shirmensa. Sosai hajja Inna ta ɗale saman machine ɗin na Zakariyya, kamar ba tsohuwa ba, da sauri Ummi ta riƙe kai ganin yadda Zakariyya ya figi machine ɗin ya fita a guje. Hayatuddeen ne ya kece da dariya tare da cewa. "Hege Zakary namu, wata rana zai ɓarar da hagwaran tsohuwar nan a titi yaseen." Dariya Raliya tayi tare da cewa. "Ai harda karya mata ƙafa." Daƙuwa Ummi tayi musu tare da juyawa tayi cikin gida sannan suma sukabita a baya. Su kuwa Zakariyya na isa ya miƙawa Zaleeha kular da Hayatuddeen yabasa yayi, dan tuni shi yaci a can yayi haniƙan, ita kuwa Zaleeha kamar bazata buɗe kularba sai ta kuma buɗe, ganin abinda ke cikine ya sata yin murmushi sannan ta miƙe tsaye, lemon exotic ta ɗauko acikin fridge kana ta dawo ta zauna, haka ta fara cin pepper chicken ɗin dayaji onion, tanaci tana latsa wayarta, Ziyada kuwa tuni tabi bayan Hajja inna da ta kirata wai tazo ta cire mata sarkan da ta sanya awuyanta, kasancewar idanun tsufa gareta bazata iya cirewa kanta ba. Ƙarfe tara dai-dai Zaliha Ziyada da Zakariyya dukansu suna zaune parlour'n Hajja ina sunata hirarsu irin ta ƴan uwan juna, yayinda kakarsu ke tsakiyarsu, tana kallon kyawawan jikokinta da take matuƙar so arayuwa, dan duk cikin jikokinta tafi son Ahmad da kuma Zakariyya. Sam bata shiri da Habu a cewarta wai shi baya dariya.
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148