Skip to content

Chapter 105

Chapter 105

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,203 words 0 views Progress saved
Download Book

turo kekensa har wajen, kasancewarsa bamai cin abinci da yawa bane hakan yasa tea kawai yasha sai kuma chips dayake ɗan tsakala yana sawa abakinsa kaɗan kaɗan, sosai zuciyar ƴan uwansa da Umminsa ke wanke fari ƙal, babu abun dake ɗawainiya dasu face farin ciki da jin daɗi, kasancewarsu da Saifuddeen awaje guda baƙaramin ƙara musu kuzari da karsashi yakeyi ba, basu jima da fara breakfast ɗinba Ahmad da Saminu suka shigo, nan suma suka zauna aka shiga cin abincin tare dasu, duk da cewa suɗin surukaine ga Ummi, amma su jin kansu suke matsayin ƴaƴa awajenta, don sunajin kamar yanda su Hayatuddeen ke ƴaƴa awajenta haka suma suke saboda haka babu batun wani nuƙu-nuƙu agabanta don mahaifiyace garesu a gabanta suka girma tun suna yara har zuwa samartansu sukanci abinci a gabanta a matsayinta na uwa a garesu shiyasa kuma, koda suka auri yaranta tafiyar bata sauya zani ba. Suna kammala cin abincin ne dukansu suka koma falo suka zauna, hira sosai sukeyi yayinda Saifuddeen ke binsu da idanu yana me karantar abun da kowannensu ke cewa, idan na dariyane yakan ɗan murmusawa, ana haka ne Ishaq da tawagar ƙungiyarsu ta Joint National association of persons with disabilities (Jonapwd) Gombe State Chapter. All the best! Suka ƙaraso, nanfa falon Ummi yacika tam da mutane, makafi, guragu, kurame, duk zuƙatansu suka cika da murnar ganin Saifuddeen, Ishaq kam ji yake kamar yamaida abokin nasa ciki saboda daɗi, duk da cewa baya gani amma zuciyarsa ta gamsar masa da cewa Saifuddeen ɗinsa aboki kuma ɗan'uwansa ya samu lafiya, haka Ummi tasa su Raihana suka ajiye abunci da abunsha ga kowanne daga cikinsu, baƙaramin daɗi Saifuddeen yaji azuciyarsa na ganinsu da yayi ba, haka suka kwashe tsawon awanni suna tare da juna, saida akayi Azahar ne Ishaq ya tattarasu duk suka koma. Adda Rahama da Dr Adnan da Baba Bello haɗi da goggo mahaifiyarsa ne suka zo, suna zuwa babu jimawa kuwa saiga mutanen dukku wanda suka kusa cika mota suma sunzo don duba jikin Saifuddeen ɗin da kuma taya Ummi murnar dawowarsa, nanfa gida ya ƙara ɗinkewa da jama'a. Da yamma kuwa Alhaji Sani da Alhaji Kabiru da kuma Alhaji Sulaiman mahaifin Hisham da Alhaji Adamu yayan Jabeer sukazo duba jikin Saifuddeen ɗin, sosai ƙwarai yaji daɗin ganinsu, suma sunji daɗi sosai da suka tararda jikin nasa da sauƙi, nan suka ɗan taɓa hira inda kowanni magana da body language sukeyi idan basu gane ba kuma yakan rubuta musu awayansa sai ya basu su karanta, sosai suka ɗansha hira kafun daga bisani sukayi masa sallama, koda sukazo tafiya al'khairi me yawa suka bawa Ummi don sunsan idan suka bawa Saifuddeen to ko sama da ƙasa zasu haɗe bazai amsa ba, awajen Ummin ma kuwa ba tsira sukayi ba don kafewa tayi tace bazasu amsa ba, da ƙyar Alhaji Sani yasanya Ummi ta amsa, inda yayi mata tuni da cewa bakyau maida hannun kyauta baya. Badon Ummi tasoba haka ta amsa kana tayi musu godiya. Wayar Hayatuddeen dake aje kan kujeran falonne kete tsuwa alaman shigowar ƙira saidai hartayi ta katse ba'a ɗauka ba, wani ƙiranne ya kuma shigowa, Hayatuddeen dake cikin kitchine ne yafito da gudu hannunsa ɗauke da wani dogon tsinke wanda jikinsa ke saƙale da gasashshen nama sai tiriri yake da'alama yanzu aka gasa naman, saura ƙiris wayan ta tsinke ya ɗauka tare da karawa akan kunnensa, cikin yanayi na ɗan faɗa tace. "Saikuma kaga dama ne kafun ka amsa wayana?" Dariya Hayatuddeen yayi tare da cewa. "Yi haƙuri Likita ina kitchine ne". Murmushi Amina dake zaune akan kujera tayi tare da gyara zamanta cike da kulawa tace "Kwaɗayayye kawai, meya kaika kitchen?." hyyy yayi dan zafin da yaji lokacin da ya kai bakinshi kan sokan nama daketa tiriri, jin tana mishi dariya ne ya sashi cewa. "Nama ne Ummina ta gasa min, shine nake d'an tab'i." Kwaffa tayi tare da cewa. "Ni bawannan ba yajikin Hamma Saifuddeen?". "Eh dai naji, jikin Hamma Saifuddeen da sauƙi sosai, don yanzu haka ma muna gida, da jiya kika ƙira ma wataƙila da kinzo kin dubashi don muna Abuja" Idanu Amina tazaro tare da cewa. "Wai kana nufin ya tabbata kun dawo Nigeria? kuma ma wai har jiya kun sauƙa Abuja shine baka ƙirani kasanar dani ba?" Dariya Hayatuddeen yayi tare da cewa. "Ga zahiri kuwa muna mgna da number ta na Nigeria." Cikin jin haushi tace. "Tun shekaran jiyan can nake kiran number ka ta Indian bata shiga, sai kawai yanzu kamar da wasa nace bari in gwada mtn naka. kuma sai ya shiga, gsky Hayatuddeen baka kyauta min ba wlh." cikin tauna naman yace "Tuba nake Likita, ai bansan kina da buƙatar ganin kyakkyawan Hamman nawa ba!" Cikin haushin rashin sanin dawowarsu da batayi ba tace "Harsai na faɗa mane sannan zaka sani, nidai ba wani nan munyi faɗa". Dariya sosai Hayatuddeen yayi tare da cewa. "Kiyi haƙuri bokan turai!". "Nidai ai nace maka munyi faɗa ko". tana gama faɗan haka ta kashe wayarta, dariya sosai Hayatuddeen yayi, Ummi dake tsaye abayansa ne ta ƙaraso cikin falon, dubansa tayi tare da cewa. "Kai kuma kaida waye kake waya haka?" Murmushi yayi tare da cewa "Amina ce fa Ummi wannan nurse ɗin da ta kula da Hamma Saifuddeen lokacin da muke Abuja, to shinefa yanzu da ta ƙira nake shaida mata dawowar mu shine wai ita tayi fushi da har jiya muka sauƙa a Abuja ban gaya mata ba taje ta duba jikinshi". Murmushi tayi cikin tsananin jin dad'i tana matuk'ar son duk wani maison Saifuddeen d'inta, murmushin kawai Ummi ta kumayi tare da zama akan kujera kana ta maida hankalinta ga TV inda sunna tv ke haska wa'azin Malam Isah Ali Pantami. Yau tunda tazo wajen aikin nasu fuskanta aɗaure yake tamau, sam takasa sakin fuska ga kowa wanda hakan ya matuƙar bawa abokan aikinta mamaki, don kuwa sunsan bahaka take ba ita takowace sannan itaɗin me yawan fara'a ce saɓanin yau da suka ga ta tsuke fuska, fitowarta daga ɗakin gabatar da shirye-shirye kenan inda ta gabatar da shirinta na mushaƙata, kaitsaye ɗakin hutawansu ta nufa inda anan tabar jakarta harma da wayarta. Koda ta shiga cikin ɗakin kan wata kujera ta zauna tare da ɗaukan jakarta, zip ɗin ta zuge kana ta ciro wayarta, 4 missed call ta iske acikin wayar wanda kuma duk daga Abdussalam ne, tsuka tayi tare da kunna data'n wayarta ta shiga Instagram, Raveel ne ya turo ƙofar ɗakin ya shigo bakinsa ɗauke da sallama, can ƙasan maƙoshi ta amsa masa sallaman batare da ta ɗago kanta ta kalleshi ba, asanyaye ya tako ya ƙaraso zuwa inda take, kan wata baƙar kujera dake facing wanda take ya zauna murya asanyaye yaƙira sunanta "Zaleeha!" Bata amsashi ba haka kuma bata ɗago kai ta kalleshi ba, ganin haka yasanyashi sauƙe ajiyar zuciya, kansa ya ɗan langwaɓar gefe guda cike da tsananin shauƙin mayen soyayyarta yace. "Dan Allah M B S Dukku ki saurareni mana, ashe shikenan don zuciyata ta kamu da soyayyarki tayi laifi? Dan Allah Zaleeha kiyi haƙuri ki fahimci irin sonda nake miki, wallahi inasonki ina miki son da nikaina bansan adadinsa ba, rasaki dai-dai yake da daiɗaicewar tunanina Inasonki Zaleeha, dan Allah ki Amshi soyayyata!!" Tsananin rauni da damuwar dayake cikine ya bayyana

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148