Skip to content

Chapter 17

Chapter 17

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
Download Book

hankali ya koma ya zauna, rai a b'ace ya fara rubutu. "Meyasa kuka karb'a ne? Bappa Ali wancan karonma da ya kawo saida nace muku kada ku amsa! ai tunda muka rasa Ya Nuruddeen mgna ta k'are munce mun yafe mishi to me sa zayi ta d'awainiya damu, ko yana zaton abinda yake mana zaisa mu manta tabon daya zama sanadin samuwarshi a ah'linmu ne?." Gyara zama bappa Ali yayi kana ya fuskanceshi cikin sanyi yace. "Kana tuhumarshi kan shine ya kashe mana Seyo ne?." da sauri ya girgiza kansa alamar a a. Shiko Bappa Ali ido ya kuma zuba mishi tare da cewa. "To haushinsa kakeji ne? Kodai baka yafe mishi bane? Ko baka yarda cewa k'addara bace da tsautsayine ya rufta mishi?." cikin lumshe ido yake jujjuya kai, sai kuma ya bud'e idanun nashi da tuni sunyi jazir dan tuno d'an uwanshi da k'unar da yakeji a ranshi. murya a tausashe Bappa Ali yaci gaba da cemishi. "Nima da Umminka k'in amsar kayan mukayi, koda aka shigar da kayan su Mudassir nasa suka fara fitar da kayan, ganin ana fidda kayanne ya sashi cewa aiyi mishi sallama dani, niko sai blnace ya shigo daga ciki sabida lokacin akwai yara a wojen suna karatu." shiru Bappa Alin yayi tare da sharte guntayen hawayenshi kana yaci gaba da cewa. "Yana shigowa gaban Umminka dasu Rahma ya durk'usa duk da girmanshi da shekarunshi da arzik'inshi ga d'anshi Arabi wanda zai kai sa'an Seyoji yana ganin mahaifinshi ya rusuna a gabansu shima sai ya rusuna." Cikin zubda hawaye Bappa Ali yaci gaba da cewa. "Suna durk'usawa sai Alhaji Gid'ad'o yayi ta zubda hawaye cikin rawan murya ya kalli Umminku dasu Rahma hawaye na zuba yace. "Kuyi hak'uri ku gafarceni, nasan duk abinda zan muku bazaku tab'a farin ciki dashiba, nasan na cutar daku cuta mafi muni tunda na kashe muku Garkuwarku, wlh bawai dan in biyaku bane ko wani abu yasa nazo na kawo muku yan wannan kayan ba a a, sai dan nasan nine na kashe me ciyar daku kullum hankali na baya konciya in na tunaku saina rasa sukuni tunda na buge Nuruddeen dan Allah ku gafarceni ku dena k'in abinda nake kawo muku halal inkune tunda na kashe mai cidaku." cikin rawar murya da zubda Hawaye Ummi tace. "Ba kaine ka kasheshiba dan babu mai rayawa da kashewa sai Allah, nasan kwananshi ne ya k'are, amman in mun amshi kayan Saifuddeen zaiyi fad'a ranshi zai b'aci shiyasa bazamu amsaba." da sauri Arabi yace. "Dan Allah Ummi ku amsa ku bawa Saifuddeen hak'uri hankalin Abbana a tashe yake tunda ya buge Nuruddeen please Ummi ku amshi abincin nan wlh in baku amsaba zaiga kamar baku yafe mishi bane." rumtse ido Bappa Ali yayi kana yaci gaba da cewa. "Jin haka yasa ni cewa ba komai mun yafe musu mun kuma gode Amman kada ya k'ara kawo mana wani abun. haka yasa sukaji dad'i sukayi ta godiya suka tafi suna k'ara bamu hak'uri. To kaji yadda akayi dan haka ba laifin kowa bane fashe ni Aliyu in kuma na maka laifi sai in kwashi kayan in meda musu." da sauri ya jujjuya kai kana ya rubuta mishi. "Kayi hak'uri bappa Ali, duk abinda kayi ya zauna." to daga nan ya shaida mishi dama yau zai fasa asusunshi da niyar gobe in zai tafi yaje da kud'in ya sai musu kayan abinci mu samman cefenen ramadan da cin kud'i. bayan ya karanta ne ya kalleshi cikin gwarin guiwa yace. "Yanzu dai to kada ka fasa asusun ka bari sai azumi ya d'anyi nisa in yaso ka fasa kayi hidiman kayan sallah." cikin gamsuwa ya jinjina kai tare da cewa. "Ba matsala hakan zanyi." daga nan suka d'an tattauna shirye-shiryen Ramadan, nan Bappa Ali yake sanar mishi an gayyaceshi cewar zaiyi tafsir a masallacin Fada har zuwa saba'an watan ramadan d'in. nan kuma yace Saifuddeen d'in zaike fassarawa kurame kuma da hannu tunda da dare zaike yin tafsir d'in zai fara k'arfe 8 a tashi 9 nan dai suka gama tsara komai yadda zai tafi. Daga nan wurinshi kai tsaye woje ya fita wurin abokanshi Mudassir k'anin Ya Adnan sai Salisu da Saminu dan gidan sarkin Dukkun sai kuma Warisu, duk su lafiyayyune sai dai sun matuk'ar iya body language sabida abokanshi ne tun na yarinta, bakin titi sukaje suka zauna iska na kad'awa suna tsaka da hira Ahmad yazo d'an Goggo Dada cikin body language Saifuddeen yace mishi. "Kai a daren nan ka ratse wannan dajin naku, to ni dai bani raka." sai ya kuma duggure kan Ahmad dake dariya tare da cewa. "Yaseen sai kun rakani, yo kewarkuce ai ta sani zuwa, tunda ka fara zuwa Gombe ka rage zuwa Shabewa Dada ma sai cekiyarka takeyi." Sai ya kuma harari su Warisu da Saminu yace. "Su dama wad'annan al'barkacinka suke zuwa, shine wai Dada tace ai dama saida karenka kake ganin karen wani, ba gashi yanzu tunda ya Seyo ya rasu bata kuma ganin abokanshi ba." sai kuma yayi dariya kana yaci gaba da cewa. "Shine yanzu da zan fito nace to Dada bari inje in cekinta miki karnukan naki tunda kice saida karenka kake ganin karen wani." dariya sukayi baki d'aya kana suka kai mushi bugu, Mudassir ne yace. "Hege Ahmad d'an iya juya mgna, ai hausace haka ba wai tana nufin mune karnukanba." shi kuwa Saifuddeen mik'a yayi tare da lumshe ido kana ya amshi wayar Saminu rubutu yayi kana ya bawa Warisu karantawa ya farayi da d'an sauti. "Hege mai dogon k'afa yau zamuyi mgnaninka yaseen bazamu rakaka ba, dan ni baccima nikeji." suna jin haka duk sukayi dariya. Nan dai suka zauna sukayi ta hira, daga bisanu dole suka raka Ahmad har shabewa suna tafe suna hirarsu ta abokai tamkar ba dareba. So koda suka dawo dare ya d'anyi nisa basu wani tsayawa ba kowa ya nufi gida. Shiko Saifuddeen yana shiga gida ya samu Umminshi da Rahma suna hira inda Rahma take goge mishi kayanshi data wonke mishi tsakiyarsu ya zauna ita Rahma tana k'asa ita ko Ummi tana kan kujera, haka yasa ya zauna k'asa kusa da Rahma sannan ya jingina kanshi kan cinyar Ummi wanda take rik'e da k'afafun Hayatuddeen tana yanke mishi farce. numfashi ya furzar kana ya d'ago ya kalli Umminshi dake shafa kanshi, murmushi yayi kana ya lumshe ido tare da bud'esu ya zuba matasu alamun yana sauraronta Cikin kula tace. "Yau Alhaji Gid'ad'o yazo." ga mmakinta sai taga ya gyad'a mata kai kuma fuskarshi ba fushi, sai ta kuma sa yar yatsarta manuniya ta shafa gashin girarshi ta kontar dashi kana tace. "Na k'i amsar kayan nida bappanku, to kuma sai yayi ta kuka yana bamu hak'uri dole bappanka yace mu amshi kayan." murmushi yayi kana ya gyada mata kai sannan ya amshi rezar hannunta ya juya ya fuskanceta da kyau kana ya kamo hannunta ya fara yanke mata farcen hannunta, saida ya yanke na yatsu biyu kana ya kalleta tare da dungule hannunshi ya mik'ar da babbar yatsarshi yayi alamun jinjina, sannan ya jujjuya mata kai alamun karta damu ba matsala. sai ya kalli Rahma ya lumshe ido ya d'aga hannu yasa bisa goshinta ya sharte mata zubafar data tsastsafo mata sabida zafin anyon. Murmushi tayi tare da zare

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148