Skip to content

Chapter 7

Chapter 7

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,205 words 0 views Progress saved
Download Book

hawaye, hakan mutumin nan tunda aka gaya musu ya zame a wurin ya zauna bisa kujera yana kuka mai ban tausayi yanayi yana tasbihi da hailala, sabida hankalin shi yayi matuk'ar tashi tunda yasan shine sanadin mutuwarshi. Bayan an d'auki gawar an kaita macuwari, su kuwa duk su uku sai suka nufi masallacin dake cikin asibitin bayan sunyi al'walane suka fara nafifili da k'auna Qur'an tare da yimishi Addu'a. Koda gari ya waye mutumin nan yayi duk kan abinda ya kamata kafin a basu gawan, Aka yi mishi wonka aka shiryashi kamar yadda musuluncin ya tanadar mana, bayan an gama kimtsashi ne, suka barshin nan cikin asibitin tare da Adnan kana shi kuma ya d'auki bappa Ali ya nufi gidanshi dake Fantami, nan ya sanar musu abinda ke faruwa, kana ya fara gaiyatar jana'izar, bayan ya gama abinda ya sauwaqa sai kuma suka nufi Dukku. Suna isa sukayi cikibus dasu Saifuddeen da Ummi da suke shirin tafiya yanzu. ganin Bappa Ali da wani mutum a cikin zazzafar mota yasa zuciyar Ummi karaya, sai tayi maza ta koma cikin gida, yayinda Saifuddeen kuma ya zubawa Bappa Ali idanu tamkar zai mannasu a jikinshi duk sun kasa yin Magna tuni mak'ota sun taru a wurin anata tambayar jikin Nuruddeen, amman ba mgna Bappa Ali sai jujjuya kai yakeyi yayinda mutumin nan kuwa yaketa zubda hawaye, ganin haka duk aka gane cewa Nuruddeen baya raye. Ita ku Ummi tana shiga cikin gida da sauri Rahma dasu Raihana sukace. "Ummi meya faru." duk da taji abinda sukace amman ta kasa mgna sai nufar inda Abba ke zaune tayi yayinda shi kuwa yayi mutuwar zaune, cikin rawar murya tace. "Bappan Saifu ne ya dawo shida wani mutum." wani irin zabura Abba yayi sai ya kuma koma ya zauna da sauri sabida azabar da yaji mak'ogoronnshi na mishi. Dai-dai lokacin kuma Bappa Ali da mutumin nan suka shigo, gefen Abba suka zauna kana Ummi kuwa ta matsa can gefe ta zauna bisa kujera yar tsuguno gaba d'aya jikinta tsuma yake zuciyarta na harbawa da sauri-sauri, shi kuwa Abba ido ya zubawa mutumin da ya tasashi gaba yana kuka da shesshek'a a hankali, cikin firgita da rauni murya can k'asa Abba ya kalli k'anin nashi da matarshi da yaranshi baki na rawa yace. "Innalillahiwa Inna'ilaihi rajiun." sai ya kuma rumtse idanunshi wasu zafafan hawaye ne suka kwaranyo mishi masu tsananin k'una murya can k'asa yace "Mutuwa ta barni ta d'auke Seyo na ko?." cikin zubda kolla bappa Ali ya gyada mishi kai, ido ya rumtse kana yayi murmushi tare da cewa. "Hmmm Seyo na ya tafi ya barni! nasan nima bazan kai bad'i iwar hakaba, zan bishi zanbi bayanshi, Aliyu na tausaya maka zan tafi in barka da nauyi, Saifuddeen zai d'auki nauyin da shekarunsa basu kai ya d'aukaba." kawai sai suka had'e kai suna kuka, hakama su Raihana da Raliyya da Hayatuddeen Amman Ummi da Saifuddeen da Rahma sun gaza kuka domin ance wani zafin ya wuce inda hawaye yake. Mutumminan kuwa shima kuka yakeyi cur-cur da hawayenshi yana basu hak'uri. Ita kuwa Ummi wani abu mai tsananin k'arfin taji ya tsoki k'afon zuciyarta ya danne kukan da takeji tana son yi, hakama Rahma sai d'anta Faruq daya tasa a gaba yana kuka ita kuwa sai dafe zaciyarta dake barazanar tarwatsewa tayi kana zuba musu idanu tamkar zautacciya. Aunty Nina kuwa matar bappa Ali fargaba yasa cikin jikinta b'arewa. Saifuddeen kuwa Allah ne kad'ai yasan abinda yakeji a ranshi, in ya kalli Ummi da Rahma ji yakeyi tamkar zai fad'i ya mutu dan tsananin zafin da k'una da zuciyarshi ke mishi. shi ko Abba yunk'ura yayi a hankali ya tashi kana ya kalli k'aninshi yace. "Ina gawar take?." cikin tausayawa mutumin nan ya mishi bayani kana duk masu zuwa jana'iza a dauko motocin a tasha ya biya kudinsu, nan aka dugguzuma aka nufi Gombe. bayan sallan azahar aka sallaci gawar, sannan akaje aka binneshi, motocin nan suka jidi mutanen Dukku suka meda su, kafin su dawo duk yan uwa da abokan arzik'i an hallara tuni Goggo Dada ma da tazo, dama Ahmad da babanshi kam dasu akaje gombe. Nan sukayi zaman makoki na kwana bakwai, mutumin nan shima yayi zaman makoki a gidanshi na tsawon kwana uku,randa akayi sadakan bakwai yaje Dukku ya k'ara basu hak'uri, nan sukace sun yafe, domin k'addarace ta rigayi fata sannan shi kuma yayi musu al'khairi sosai dan harda kayan abinci ya kawo musu tuni kuma ya fara azumi settin d'in da zaiyi. Rayuwa dai taci gaba da tafiya a haka. Yau da dad'i gobe akasin haka. Abu da dama ya faru cikin watanni ukun nan. Bayan wata uku Ranar wata asabar bayan sallan magrib, duk suna tsakiyar gida, Ummi ta tasa Rahma dasu Raihana da Raliyya suna d'an hira, Saifuddeen kuwa da Hayatuddeen suna gaban Abba. mik'ewa Abba yayi kana ya kalli Ummi da yaranta da suke shawarar a saida kayan d'akin Rahma a kaishi asibiti ai mishi aikin mak'ok'on . murmushi ya d'anyi kana ya d'auki butar dake gefenshi tare da nufar hanyar ban d'aki yana mai ce musu. "Uhumm Rahma kenan, kada ku yarda ku saida wani abunku a kaina fa, domin wannan ciwon nawa tabbas wata rana shine ajalina." d'an tsayawa yayi jin Rahma na cewa. "Dan Allah Abba kayi hak'uri mu kaika asibiti, bazamu iya ganinka hakaba." murmushi ya kumayi kana yace. "Rahma iyayena mafa haka sukayi ta nema min mgni k'arshe har suka rasu ban samu lfy ba, hakama k'annena gaba d'aya Ali ya saida gonakinmu da filayanmu na gado, a kan nema min mgni yanzu du-du du gonaki ukune suka rage sai wannan filin da ke can bayanmu wanda shi kuma dama nine na sayeshi da sunanku. dan haka ku dena wahal da kanku ai sauk'in yazo." yana fad'in haka ya juya ya nufi bayan gidan, a dai-dai bakin k'ofar ya fad'i. Wanda kafinma a d'agashi ya cika. Wannan rana anga tashin hankalin wannan ahlin, dole Abba kwanan keso yayi, washe gari da hantsi akayi mishi sutura, wanda tuni k'ofar gidansu ta cika da al'ummar annabi. Bayan an mishi sutura an kimtsashi kamar yadda musulunci ya koyar damu anzo za'a d'auki makar ne za'a fiddashi. da sauri Bappa Ali ya kalli Saifuddeen daya rik'e makarar yanayin wani irin kukan da yasa dukkan bani adam dake wurin zubda zazzafan hawaye, tuni shima Bappa Ali sai ya zame kana ya ruggumi Saifuddeen da Hayatuddeen dake ruggume dashi, kuka sukeyi wanda duk kan mai imani zai tausaya musu. shi kam Saifuddeen duniya ta mishi zafi ji yakeyi tamkar bai tab'a farin cikiba, fata yake inama shima mutuwar tazo ta d'aukeshi. tausayin kanshi da mahaifiyarsu da k'anneshi da yayarshi yakeji tamkar zai d'auke numfashi sa. Man Liman ne suka janye bappa Ali kana Baba Hamisu yasa hannu ya janye hannun Saufuddeen daga rik'on da yayiwa makarar. Baba Ashiru kuwa da wani abokinshi wanda kuma malamin islamiyarsu Saifuddeen ne sune suka kamashi ganin yanayin da yake ciki, cikin sanyi Baba Ashiru ya cewa Hayatudden. "Deen je ka kawo min ruwa. cikin kuka ya mik'e kana ya kawo ruwan amsa yayi kana ya kalli Saifuddeen da idanunshi sukayi jazir tamkar zasuyi aman wuta, ganin bazai k'arb'a bane yasa Malaminshi amsar ruwan ya kai mishi har baki, kana cikin sanyin murya

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148