Chapter 74
Chapter 74
Tandama: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *NAKASA BA KASAWA BACE* *PAGE 18* NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 _Free page hmmm sunfa kusa ƙarewa yaseen gwara ka/ki biya yafi miki, kada kuyi shagala da free page wasan yanzu aka fara, somin taɓine. Daga yawan page ɗinma kunsan labarin mai tsawone shiyasa nake inƙanta yawan pages sabida rage muku zaƙuwa, biya ɗari uku kacal dan samun damar karantashi har ƙarshe._ *Turo katin mtn ta wannan no 09097853276. Ko ta asusuna 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ku turo shaidar biyan naku ta wannan no 09097853276* Sai ta kuma yi saurin sa hannu ta rufe bakinta dan ganin yadda ya had'e fuska kana ya tsareta da kyawan manyan idanun shi, had'iye mgnar tayi kana ta fara b'allo magungunanshi tare da fara yi mishi nuni da wai zata bashi mgnani. hannunshi ya mik'a mata ganin haka ta bashi maganin. Bisimillah yayi a ranshi kana ya afasu cikin baki sannan, ya kuma mik'o mata hannu da sauri ta bashi goran ruwan mai sanyin dake hannunta, amsa yayi ba tare daya kuma kallontaba, ya had'iyi maganin, tare da shanye rabin ruwan dan bin shawarwarin da doctors suke bashi na ya yawaita shan ruwa, a ranshi yake cewa. "Fitsararriya kawai mai kwaɗayin tsiya." ita dai sai kallon saitin mararshi takeyi da alamun tsoro, ya fahimci tsoro ne yasa taketa mishi kallon kurillah. Tsuke fuska ya kumayi tare maganar zuciya, "Ganta kamar mayya, wannan kallo kamar zata cinye min Saif ɗina, ja'ira to wannan dai nan gani nan bari." A zahiri kuwa, hannunshi ya d'ago kana ya had'a yatsunshi biyu dogo na tsakiyar nan da babban yatsarshi ya murzasu suka bada sautin. Tab-tab!! da sauri ta juyo ta kalli fuskarshi. dan tayi nisa da kallon haƙilo da takewa sashin lafiyarshi na inƙarman na miji mai cikar zarra, hannunshi ta zubawa idanu wanda yaketa yimata nuni data fita, ba musu ta kama hanyar fita baya ta ajiye magungunan har taje bakin ƙofa ta kuma juyowa ta kalleshi a hankali tace, "Uhummmmmmm to wai wannan da yana lfy kuma ya yake?." sanin ba amsa yasa ta fice tanata zancen zuci. Shi kuwa Hamma Saifuddeen tsaki ya ja tare da da had'e hak'oranshi, duk duniya babu matar da ta tab'a ganin tsiraicinshi tunda akayi mishi kaciya ya worke lokacin yana d'an shekaru shida, koda Ummin shi da Aunty Rahma basu kuma ganin tsiraicinshi ba, sai wannan yarinya rana tsaka. Wani d'aci yakeji zuciyarshi na mishi tunowa ita gani tayi bai mance Zaleeha ba lokacin da ta lab'e bayanshi ta kama kugunshi lokacin da taga wadannan y'an daban sunyi kansu da makamai, ido ya kuma rumtsewa jin yadda tsikar jikinshi ya mik'e tuno a lokacin tasa hannunshi ta zagaye konkosonshi tana k'ok'arin janshi garin zame hannunta ta shafa sirrinshi ta had'a da ƙugunshi ta riƙe abinda da babu wata d'iya mace data tab'a ko ganinshi bare ta shafa, tun daga wannan shafar da tayi mishine kuma wata azabebbiyar kasala ta rufeshi mood nashi ya canza yaji wata iriyar fitinar da bai tab'a jiba a iya tsawon rayuwarshi hakanne ya bawa yan kalaren daman yin nasara a kanshi. cikin ranshi yake cewa. Da a iya zatonshi shi baida cikekkiyar zarra tunda ko azumi yayi Saif ɗinshi koma yakeyi ya ɓuya, haka kuwa in yayi aikin wahala kaɗan abin kan noƙe, sai randa ya fara ganin laɓɓan Zaleeha a tv ne ya fahimci waye shi, sai kuma gashi daga taɓashi sau ɗaya da tayi har yau bai kuma konciya ba, a ranshi yace. "Ya Allah ka sauk'ak'amin k'addarorina daga wannan ta tab'a sirrina sai wannan taga matsayina. Yarinya har ta fara cemin jarabebbe, ko jarabar uwar mi na mata? alhalin ita keta kallona kamar ta cinyeni ɗanye." sai ya kuma bud'e ido tare dayin mgnar zuciya. "Zaleeha ce sila da bata tab'ani ba da bazan rink'a d'imaucewa ba duk sanda na tunota." ido ya kuma rumtsewa yanaji bayanshi kamar ba'a jikinshi yakeba. Ita kuwa Amina tana fita tayi kicibis dasu Ummi da Dr Batulu tayiyo musu jagora da suka fito office d'in Dr Aliyu, cikin girmamawa ta gaidasu kana ta wuce, su Kuma sukayi ciki. Zaleeha da Ya Ahmad d'inta da Mamy da Mama dasu Habu wanda yayan Zaleeha ne kana sai maryam yayar Zaleeha wacce tazo da mijinta Aminu wanda d'an bappansu ne yayan Baba malam, duk sun nitsu sunyi shiru, shi kuwa Baba malam cikin cikar haiba da dottaku da nitsuwa da kamala irinta manyan mutane wadanda suka wadatu da ilimin addini, ya fara yi musu addu'a kana yayi musu nasiha mai ratsa jiki sannan ya d'aura da cewa. "Alhamdulillahi duk kunsan sanadin zamannan namu tunda kukaga mun zauna zaman jiran Zaleeha." gyad'a kai sukayi baki d'aya sai Aminu wanda da ka ganshi kasan irin mutanen nanne masu zafi da tsauri fuskarnan tashi tana had'e sai harara yake cillawa Zaleeha k'anwarshi d'iyar Bappanshi k'anin mahaifinshi wanda suke uwa d'aya uba d'aya, kana k'anwar salihar matarshi Maryam. Ya Ahmad kuwa tonk'oshe kafafu yayi cikin tsanin girmamawa yace. "Na'am". Alamun suna jiran umarni ko shawara daga mahaufin nasu. Shi kuwa Baba Malam, Malam Bashir Sulaiman Dukku kenan, gyara zama yayi tare da cewa. "Dama ta k'arshe zan baiwa Zaleeha wanda zan ninka mata da damar dana bata, wata shida baya, nace ta fito da gwoninta, na bata dama tayi zab'inta duk da shariya ta bani dama in zab'a mata mijin danaga ya dace a matsayinta na budurwa ni kuwa mahaifinta, to amman na bata dama zan kuma k'ara bata dama na k'arshe kada ita da mahaifiyarta suyi zaton bani basu hak'k'insu,." sai kuma ya tsagaita kana ya kalli Mamansu Zaleeha wacce fuskarta ke had'e kauda kai yayi tare da cewa. "Halima ki shawarci d'iyarki data fidda goninta cikin masu sonta, nanda tsawon shekara guda, na bata wannan damarne sabida ina sane da k'orafin da kikayi tayi a auren Maryam cewa nayiwa yarki auren dole kika rink'a zugata data bijirewa zabin da ni nayi mata, sai nayi dacen Maryam salihace muminace mai biyeyya a gareni, tabi zabina ta watsar da mummunar shawarar da kike bata ta ruggume aurenta tayi biyeyya ga mijinta d'an uwanta." sai ya kuma kalli Maryam wacce yasan duk yayanshi daga Ahmad sai ita basa son duk wani abu da zai bata mishi rai bare ya zubda mutuncinsa. Cikin taushin lafazi yace. "Allah ya miki Al'barka Maryama ubangiji ya sa yaranki su miki biyayya fiye da yadda kikayi min, Allah ya saka miki da jannatul firdausi." "Amin Amin ya rabbil izzati ngd Baba Malam Allah ya kara nisan kwana". Cewar Maryam kana duk parlour suka amsa da Amin, Ita kuwa Mama sai k'ara had'e fuska tayi, itako Zaleeha sai k'ara sunkuyar da kanta ta kumayi, gyaran murya Baba malam ya kumayi sannan yaci gaba da cewa. "Zaleeha ki fito da zab'inki cikin watanni goma sha biyun nan, ki fara lissafi tun daga yau d'in nan yanzun nan kuma, kinga dai a baya na baki wata shida, shiru baki fidda mijiba, to ki sani muddin kika cika wa'adin da na baki baki fidda mijiba, toh zab'i ya dawo gareni, duk wanda naga dama shi zan aura miki, domin nasan, baki rasa ma nemaba, amman kinyi burus da zancen, kinasa ana nunani in na wuce ana cewa shine babanta, ai yar malami ne, wasu na tuhumar to
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148