Skip to content

Chapter 136

Chapter 136

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
Download Book

a rantaba da jin furucinsa, sai sakin hannunshi da tayi lokacin da sukazo dab da ƙofar Mama, cikin alamun gajiya da kuma yunwa dake damunta tace. "Yauwa Ya Ahmad bari inje inyi wanka sai inzo muyi hira, ka cewa Aunty Lubna ta gasa min abin daɗi yunwa nakeji, please ko roasted fish nema nasamu idan nazo." "To." Kawai yace tare da juyawa yayi side ɗin Mamy. Ita kuwa Zaleeha da sallama ta shiga, da sauri ta kutsa kanta cikin parlour'n, saboda hango Mamanta na zaune fuskar nan a kumbure alamun tsananin fushi, da sauri ta durƙusa agabanta cikin tsoro tace. "Lafiya kuwa Mama? Meya sameki? baki da lfy ne?." Duk tayi mata tambayar cikin kulawa, irin wacce ke tsakanin Ƴa da Uwa. Cikin tsananin takaici Mama ta watsa mata harara tare da cewa. "Ae naji ke har dariya ma kike ko? yayinda ni kika barni ina nan baƙin ciki da ɓacin ranki zasu haɗu su kasheni!." Cikin zaro ido haɗi da tsoro tace. "Na shiga uku Mama me nayi miki?." A hasale Mama tace. " kikamin ko kikayiwa kanki." Sai kuma ta miƙe tsaye tare da watsawa Zaleeha wani irin mugun kallo. Sannan tayi cikin bedroom ɗinta, wanda idan ba doleba, sam bata son shigarsa, saboda idan taga wannan kayan ji takeyi kamar ta faɗi ta mutu, tsabar baƙincikin dake cika zuciyarta. Da sauri Zaleeha ta bita, a gaban Maman ta tsaya, cikin raunin murya tace. "Mama kiyi haƙuri in na miki laifine ki gaya min Wallahi bazan sakeba!." Azafafe ta nuna mata tarin akwatunan wanda ita sam bata gansuba sai yanzu cikin kakkausan murya tace. "Kinyi asara Zaleeha, Wallahi kinyiwa kanki sakiyar da ba ruwa, ki rasa wanda zaki zaɓa duk cikin masoyanki sai wannan banzan nakasasshen da baya ji baya magana, uwa uba kuma baya tafiya, ki zaɓeshi matsayin miji har zaki bashi dama ya turo iyayenshi su kawo tarkacensu harda su sadaki, wato kin maidani shasha naje inata haushi ashema ban saniba kece kika amince mishi sai ɗazu Habu yake sanar min." Mama fa bata tsagaita da masifaba bare tasan halin da Zaleeha ke ciki. sai Zahira ne ta zaro ido da ƙarfi ganin yadda Zaleeha tasa hannu da tsananin ƙarfi ta kama kanta, yayinda tuni kunnuwanta sun toshe tun lokacin da Mama tace mata an kawo sadakinta kuma wai ga kayan aurenta a gabanta, sannan wai da yardarta uwa uba kuma wai da wancan ginannen taɓon ne da Allah ya ƙawatashi da kyan sura, daga nan bata kuma jin zancen Mama ba, sai rumtse idanunta da tayi tare da cilla wani irin gigitaccen ƙara mai tsananin ƙarfi, haɗe da cewa. "Ƙarya ne banice na turo shiba, bana sonshi! bazanyi aureba Wallahi, bazan zauna da kowaba sai wanda ya taimakeni!!." Sai ta kuma buɗe idanunta, wanda sukayi jazir ta kalli tarin akwatunan, wani irin gigitaccen ƙara ta saki wanda yasa, Ahmad, Habu,Aunty Lubna da suka nufo parlour'n maman tun ihunta da sukaji na forko ya sasu shigowa a guje, suna shiga ita kuwa zaliha ta yanki jiki ta faɗi sumemmiya. Da sauri Ahmad ya tarota ta faɗa jikinshi, cikin rawan jiki murya a hargitse yake ɗan jijjigata tare da marin kumatunta yana faɗin. "Zaleeha! Zaleeha!! Ki tashi Zaleehaaa!!!." Sai ya kuma kalli Zahira daketa kuka tana cewa. "Shike nan ta mutu, tace muku bata son auren ba wanda take so ku barta ta jira wanda takeso anƙi gashi yanzu baƙin ciki zai kasheta. Mama kuwa da sauri ta juya ta nufi falon Baba malam tana shiga tasa kuka tare da cewa. "Shike nan baƙin ciki zai kashe min ƴata, in ta mutu ai kowa ya huta sai a kaiwa shashashan musakin gawanta." Shiru Baba malam yayi sai murmushin da yakeyi, Mamy kuwa da sauri ta miƙe zata nufi side ɗin Maman, dan da fari da suka jiyo ihun Zaleeha sunyi zaton ko uwarce ke dukanta, shiyasa data yunƙura zata je Baba malam ya dakatar da ita. A can ɗakin Mama kuwa a kiɗime Lubna ke cewa Ahmad. "Hubby a sume take fa, ko dai da gaske al'jani ne ya taima keta shine yau zasu baiyana kansu? Hubby mu kaita wurin Baba Malam!." Tafaɗi maganan cikin tsananin ruɗewa. Yunƙurawa Ahmad yayi da ita a jikinshi, fita yayi da matsanancin sauri ya nufi parlour'n Baba Malam, a bakin ƙofa sukayi karo da Mamy. Cikin tsoro da firgitan ganin Zaleeha kamar gawa Mamy tace. "Malam da gaske Zaleeha ba lfy." Shi kuwa Ahmad a gaban mahaifin nasu ya direta tare da cewa. "Baba malam al'janine fa a jikin Zaleeha da gaske danfa kawai taji batun auren ne yasa ta suma." Habu ne yaja wani dogon tsaki tare da cewa. "Ya Ahmad meyasa kake yarda wai Zaleeha iska gareta?." Cikin tsawa yace da Habu. "To in ban yarda tanada iskaba meya sumar da ita? please Baba malam ayi mata ruƙiyya ko al'janin zaiyi magana." Cikin takaici Habu ya juya gaban fridge ɗin dake gefenshi, buɗewa yayi tare da ɗaukan goran bottle water mai ɗan karen sanyi, kana ya juyo marfin gorar ya murɗa kana ya ziraro da bakin gorar dai-dai saitin fuskar Zaleeha ya fara tsula mata ruwan sanyin. Wani irin wawan ajiyan zuciya taja, me ɗauke da azaban ƙarfi kana ta fizgo numfashinta da wani zazzafan kuka, cikin kuka mai cin rai ƙuna da kuma tsananin tsoro take cewa. "Bana sonshi Ya Ahmad ka gayawa Baba malam wallahi bana sonshi na tsaneshi!." Sai ta kuma kamo hannun Ya Ahmad ɗinta da tuni ya fara zubda hawaye, cikin kuka taci gaba da cewa. "Ya Ahmad ka gayawa Baba malam mana, ka faɗa mishi cewa gurgu nefa haka kuma kurma ne, kace mishi bana sonshi na tsaneshi, wallahi in aka aura min shi zan mutu wlh ya Ahmad mutuwa zanyi!!!." Taƙare maganar cikin wani irin kukan fitar hayyaci. Habu ne ya watsa mata wani zazzafan harara tare da cewa. "To ki mutu mana! In kin mutun sai me? Ko kina zaton mutuwarki zaisa muma mu mutu ne?." Faɗawa jikin Aunty Lubna dake raɓe agefe tana zubda hawaye tayi, cikin kuka da raunin murya tace. "Wayyo Allah na Aunty Lubna ki taimaka min ki faɗa musu inada wanda nake so, kice musu wlh bana son musakin can." Cikin rauni Ahmad ya kalleta murya a tausashe yace. "To meyasa kika ce mishi kin amince dashi ya turo iyayenshi tunda kin san bakya sonshi?." cikin kiɗima da gigita tace. "Wallahi ban faɗaba wlh ƙarya yake min, to shida kurmane ta inama zaiji abinda zance mishi?." cikin hatsala Habu yace. "Ba text messages kika tura mishi ba, da wayarki." Miƙewa tayi a hargitse ta kalli Mahaifinsu da ya zuba musu ido, yana murmushin ganin ƙuruciyar yaran nashi, ba abinda ke sashi murmushi kamar yadda Ahmad yake taya Zaleeha kuka kamar yaro, yana jin daɗin zafin Habu dan yasan Habu Baban ya Aminu ya gado yayan Baba malam kenan, cikin kuka Zaleeha tace. "Wallahi ƙarya yake min ni bani da number shi ma." Mama ce tayi kaffa tare da jan dogon tsuka. Habu kuwa falon Mama ya koma, jim kaɗan sai gashi da wayar Zaleeha riƙe a hannunshi, cikin takaici ya cire wayar a key dan yasan komai na wayar, hakan kuma tsarinshine dan bincikar woyoyin ƙannenshi yasa su duk yasan komai na wayarsu. kai tsaye inbox

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148