Chapter 34
Chapter 34
ci da sha, nan suka zauna suka d'anci, suna fitowa gidansu Saminu suka wuce gidansu Warisu. Dalinshi tana ganinsu tai ta farin ciki tare da sa musu al'barka nan ta kawo musu fura da nono, sunsha nonon sosai daga nan suka fito suka shiga gidansu Mudassir nan suka samu ya Adnan ya dawo jiya da dare, yana ganinsu yace. "Iye Umma zo ki ga 'yan samarinku, wlh yarannan sun girma sosai fa kalli duk sun kusa kamoni tsawo fa." Bud'a kafad'u sukayi tare da had'a baki sukace. "Kai Ya Adnan mun kamo ka dai kawai zaka ce." Umma dai sai murmushi takeyi, shi kuwa Adnan kamo hannun Saifuddeen yayi tare da cewa. "Duk baku da kunya Saifuddeen ya fiku mutunci, dan ku gani kuke kunma fini." sai ya kuma kalli Ahmad dake tsare fuska cikin raha yace. "Kai Ahmad me na had'e fuska haka?." tab'e baki yayi tare da cewa. "Au ashe dai baka mance niba ai wlh ya Adnan baka da kirki, kullum Dada sai tayi cekiyarka in taga Mudassir tace wato kai kam tunda Ya Nuruddeen ya rasu ka yanke zumuncin dake tsakani." da sauri ya juyo ya kalli Ummanshi dake cewa. Ai wlh shi Adnan sam baida k'afa dama Nuru shike sashi ziyara, kullum in yazo sai nayi ta binshi yaje amman sai ya zama ko fitan baya so." da sauri ya katsesu tare da cewa. "Kinga ko Umma wlh yanzuma niyata shabewa zan tafi dan wlh nima kaina nayi kewan goggo Dada tun rasuwar Abba ban kuma ganintaba." shi dai Saifuddeen baibi ta kansuba, shiko Ya Adnan bayan sun shiga d'akin Umma ne shi kuma ya fita. Kai tsaye gidansu Saifuddeen ya nufa, yana shiga ya samu Ummi a tsakar gida cikin shiga ta salla, tana ganinshi ta fad'ad'a fara'arta cikin jin dad'i tace. "Lale marhabin da Ya Adnan yaushe a gari mutanen Zaria." cikin sakin fuska ya zauna bisa taburmar data shimfid'a mishi cikin sakin fuska yace. "Jiya da dare ne Ummi shiyasa ban shigoba." gyara zama tayi tare da cewa. "Ayyah sannu da hanya." "Yauwa sannu Ummi ya gida yasu Saifuddeen ina auta Hayatuddeen." juyawa ta d'anyi ta kalli k'ofar d'akin Rahma cikin d'an d'aga murya tace. "Auta ga Ya Adnan d'inku." jin haka yasa Hayatuddeen fitowa da sauri, ita kuwa Ummi juyawa tayi ta kalli Adnan tare da cewa. "Yanzu ya dawo idi shida Faruq to wai zai tafi shabewa wurin Goggo Dada da yake Adam da Raliya suna can shiyasa suketa d'okin zasu tafi can." shi kuwa Hayatuddeen yana zuwa ya ruggumi Adnan yayinda Faruq ke bayanshi da sauri ya iso ganin Adnan na mik'o mishi hannu ruggumesu yayi baki d'aya yana jin tausayin yaran da k'aunarsu yana tuno irin so da k'aunar da Nuruddeen ke musu. ita kuwa Ummi cikin sanyin sautin da ganin Adnan ya tuna mata d'anta ta kalli Rahma da yanzu ta fito ganin Adnan ne yasa ta koma cikin d'aki da sauri, jin muryar Ummi na cewa. "Rahma fito mana kizo ki kawo mishi abinci." cikin sanyin murya tace. "To Ummi bari insa hijabi." daga nan sukaci gaba da hira, cikin kula Ummi tace. "Ya karatu yanzu kam ka kusa gamawa ko?." gyara zama yayi tare da cewa. "Alhamdulillahi Ummi ai nama gama." cikin jin dad'i tace. "Alhamdulillahi nayi farin ciki Allah ya taimaka ya baka aiki cikin sauk'i." ido ya lumshe ganin Rahma data rutsuna gabanshi, sai ya kuma kauda kai daga gareta tare da sauk'e numfashi kana ya kalli Ummi tare da cewa. "Amin Amin Ummi aiki kam ya samu ma da yake karatun likitanci ne samun aikin ba wuya, next week zan koma gombe dan na samu gurbin aiki a medical senta gombe harma sun bani gidan zama a can a jerin gida jen ma'aikatan su." Sosai Ummi tayi farin cikin wannan labarin, daga bisani ta tashi taja hannun Hayatuddeen da Faruq da tace. "To muje in had'a muku kayanku, kai Auta baka ganin girmanka sai kayi ta zama jikin mutane." murmushi yayi tare da zaro kud'in 'yan ishirin-ishirin ya bawa Hayatudden guda goma hakama Faruq aifa nan sukayi ta tsalle suna murna, cikin had'a fuska Rahma tace. "Baku iya godiya bako?." da sauri suka juyo tare da cewa. "Ya Adnan mun gode Allah ya saka ya k'ara bud'i." Amin Amin yace, tuni su kuma sunbi bayan Ummi, shi kuwa Adnan idonshi ya d'an lumshe tare da sa yatsunshi biyu ya d'an ja jelan kitson Rahma dake har bisa kafad'unta, da sauri ta d'an juyo tare da cewa. "Wash Allah na ya Adnan zafi." girarshi d'aya ya d'aga mata tare da cewa. "Raguwa kawai." ido ta lumshe da sauri jin yana cewa. "Kinji na gama karatu har na sama mana aiki, bakice komaiba." idon ta ta d'an bud'e tare da cewa. "Nayi mana addu'a ai ya Adnan." gyara zamanshi yayi ya kalli gefe ganin Ummi ta fito zata shiga d'akinta cikin yin k'asa da murya yace. "Kinga sauran burinmu na gaba, yanzu dai na kusa in baiyana kaina gaban bappa Ali ya aura min ke in rik'e 'yar k'anwata in sata farin ciki." da sauri ta kuma rufe ido, shi kuma sai ya d'an d'aga murya tare da cewa. "Yunwa fa nakeyi bani abinci inci." hararanshi ta d'anyi sannan ta zuba mishi abincin ganin zai fara cine yasa ta yunk'ura zata tashi, sai kuma ta koma ta zauna jin ya kamo hijabinta, dole ta zauna suna d'an hira yana cin abinci. har saida ya k'oshi sannan yace. "Nafa yi amarya." ido ta d'an zaro alamun tambaya, murmushi yayi tare da cewa. "Bafa amaryar da za'ake konciya da ita a gadoba machine ne kasia na saya mana." cikin jin kunya tace. "Masha Allah, nayi farin ciki." juyawa yayi ya shiga d'akin Ummi kud'i ya zaro yan d'ari-d'ari rafan dubu uku ya mik'awa Ummi, amsa tayi tare da sa mishi al'barka ta kuma yi godiya, daga nan ya fito tare da cewa su Hayatuddeen su fito ya kaisu gidan goggo Dada aifa da murnarsu suka fito, suna fitowa Raihana kuma dake k'ofan bappa Ali tana taya Aunty Nina kirba fura itama ta fito nan tace zata bisu, nan take ta shirya suka fita suka nufi shabewa. Su Saifuddeen kuwa ranan sun zazzagaya gidan yan uwa da abokan arzik'i, sai bayan sallan magrib suka dawo gidan Ummi inda dama sukace tayi musu miyar kuka da tuwon semo wai sun gaji da cin kayan maik'o, aifa sukaci sukayi hanik'an, har sha d'aya na dare Ahmad yace shifa zai koma aiko sukace yasin bazasu rakashi ba, dole Salisu ne ya maidashi. Ishaq kuwa ranan wuni yayi yana zura idon ganin Saifuddeen, yayi ta gwada kiranshi kuma woyar tashi bata shiga, haka ya hak'ura ya kwanta da niyar gobe da sassafe zai tafi dukku. Washe gari kuwa Saifuddeen yayi kolliya na gani na fad'a dan zaije gidan Abokan Abbanshi Baba Hamisu kakansu Faruq kenan da kuma Malam Ashiru, yana gama kimtsawa ya d'auki turare ya feshe jikinshi dashi kayan sunyi matuk'ar mishi kyau shida Hayatuddeen da Ahmad ne wanda Ahmad d'inne ya d'inka musu shi, yad'in voyel ne mai ruwan madara yadin mai gidan dara-dara, sai surfani bak'i da akayi aikin d'inkin, sai kuma takalmi bak'i mai ratsin fari da hula zanna bukar bak'i da ratsin farin, sosai kayan sukayi
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148