Chapter 97
Chapter 97
wadannan hanyoyi shine mutum ya fahimci cewa Kibr, wata siffa ce wadda ta ke~anta ga Allah wato kamar yadda yazo cewa Walahul-Kibriya’u.Saboda haka wannan wata siffa ce wadda bata cancanta ga kowa ba face ga Allah Ta’ala. Daga cikin wadannan hanyoyi na magance girman kai shine mutum ya yi tunani a kan cewa dukkan abin da yake tinkawo da shi wadda har ya kai shi yana girman kai ga wani ko wasu da abin,to Allah ne fa ya ba shi,in yaso zai iya kwacewa,saboda haka idan Allah Ta’ala ya yi maka wata ni’ima,abin da ya hau kan mutum shine ya gode ma Allah ya kuma kasance mai tawadi’u. Daga cikin wadannan hanyoyi shine mutum yayi dubi da kuma tunani kan ayoyi da hadisai da suke suka da kuma bayanin mummunan sakamako na mai girman kai,da kuma wadanda suke nuna yabo da sakamako mai kyau na mai tawadi’u. Daga cikin wadannan hanyoyi na magance girman kai shine mutum ya yawaita tunanin Akibarsa wato karshensa a fagen addini,ba mamaki wanda kake ma girman kan shi yayi kyakkyawan karshe kai kuma wa’iyazu-billahi kayi mummunan karshe. Daga cikin wadannan hanyoyi shine lizimtar addu’a musamman ma ta Makarimul-Aklak,mai son ganin ta yana iya duba littafan addu’oi kamar mafatihul jinan,in mutum zai iya ya kasance ko wane dare bayan sallar tahajjud dinsa ya karanta ta, ko kuma akalla ko wane daren jumma’a ko ranar.Haka nan kuma mutum ya dinga rokon Allah ya ba shi lafiya daga dukkan cututtuka na ruhi,shi yasa idan mutum na addu’a na Allah ya ba shi lafiya to ka da ya tsuke tunani ga neman lafiya ta gangar jiki kawai, A’a har da ta ruhi,domin mutum zai iya kasancewa ga shi da lafiyar jiki amma kuma ruhinsa bai da lafiya.Haka nan idan mutum na rokon Allah ya wadata shi,to ya roka har da wadatar zuci,saboda mutum zai iya kasance ga shi da dukiya amma kuma bai da wadatar zuci.... Fa’idodin nisantar girman kai:Yana da fa’idodi masu yawa daga ciki akwai jawo ma mutum son Allah da kuma son Manzon Allah kai har ma da son mutane.Yana haifar ma mutum wanzuwar ni’imar da Allah yayi masa,sa~anin girman kai da ke janyo ma mutum gushewar ni’ima. Yana daukaka mutum awajen mutane da kuma wajen Allah Ta’ala.Akwai hadisi da aka ruwaito daga Imam Sadiq[AS] cewa,wani mawadaci ya zo wajen Manzon Allah da tufafinsa fes-fes,sai ya zauna gaban Manzon Allah,can kuma sai ga wani talaka ya zo da tufafinsa ya yi datti,sai ya zauna kusa da wannan mawadacin,sai mawadacin ya tattare tufafinsa.Sai Manzon Allah ya ce masa kana tsoro ne ka da ya shafamaka talaucinsa? sai mawadacin yace A’a,yace to kana gudun ka da ya sa maka datti a tufan ka ne? Ya ce A’a.Sai Manzon Allah yace masa to mi yasa ka yi haka? Sai yace aikin shaidan ne.To nan take sai mawadacin yace na bashi Rabin dukiya ta.Sai Manzon Allah ya tambayi matalaucin akan zai amsa? Sai yace A’a.Sai mawadacin ya tambaye shi miyasa ba zai amsa ba? Yace ina tsoron abun da ka yi mani nima in yi wa wani.A takaice dai nisantar girman kai ya na haifar ma mutum da kyakkyawan sakamako a duniyarsa da kuma lahirarsa.... {issoshi na karshen masu girman kai:Mu duba saboda girman kai yadda karshen shaidan ya kasance.Mu duba tarihi zamu ga yadda girman kai ya haifar da mummunan karshe na wadanda suka ki bin Annabawan Allah da kuma Aimma[[AS]. Haka nan mu duba sakamakon girman kai yadda ya haifar da mummunan karshe ga wadanda suka Ja da wadanda Allah Ta’ala ya yi amfani da su wajen jaddada addini misali a zamanin Shehu Usman dan Fodiyo da kuma Imam Khumain. Atakaice dai girman kai yana haifar ma mutum da mummunan karshe a duniyarsa da lahirarsa,kuma mutum ya lura da mai girman kai ko a rayuwarmu ta yau da kullum za ka ga daga karshe sai ya walakanta har ma ya zama abin tausayi.Kuma irin wadannan munanan siffofi na girman kai,Riya,Hassada,munana zato ga juna,son matsayi da sauransu sune suke dabaibaye mutum daga ayyuka na da’a,misali ka ga mutum da yana ibadodi kaza da kaza amma yanzu ya yi rauni a kai ko ma bai yi. Haka nan kuma irin wadannan zunubai su suke hana mutum samun istikama a tafarki na Allah Ta’ala,ka ga da yana tafarkin Allah amma yanzu ya barshi.Saboda haka yana da muhimmanci mutum ya yi mujahada domin ya samu tsarkaka daga wadannan munanan siffofi,wato ka da ya bari mutuwa tazo masa alhali yana tare da wadannan munanan dabi’u,domin in ya tafi da su lahira to zasu zama masa matsala babba.Muna rokon Allah Ta’ala ya tsarkake mu da tsakakewarsa,ya kuma samu cikin tsakakan bayinsa...." *DanAllah wattadians ina bukatan Followers dakuma votes🙏* #team Zuly #team Mom *Vote,comment&share* *ZULFA* @MHIZZPHYDO A Sweet and pitious Romantic love story *Bismillahir Rahmanir Rahim* *Page 96* "Ameen" suka sake fada atare inda Mom tadinga sauke ajiyar zuciya akai-akai, gyaran Murya Maram tayi cikin sanyin murya tace "Kawata kiyafe min! Amma kisani bawai don na bata miki rai na aureshi bah na aureshi neh soboda son danake mishi" Dago kai Mom tayi har zata harareta saikuma takawar da kanta tana mai gyada kai alaman ba damuwa, murmushi Zuly tayi soboda sarai taga abinda Mom tayi amma tabar hakan amatsayin dabi'rata ma'ana yanda tasaba yi kunga kuwa ba alokaci daya abin zai barta bah! "Toh Allah yakara karfin jiki!"ustaz yafada tareda ajiye ledar hannunshi sannan sukayi musabaha da mazajen waje yafice hannunshi nacikin na Raees. Da ido suka bi bayansu kafin kowa yayi jugum ana tunanin abin duniya. Matsowa yayi kusa da Zuly tareda dan zungurinta da hannunshi make kafadarta tayi tana turo baki alaman bazata juyo bah, murmushi yasake kafin ya dan tsuguna daidai kunnenta yace "Haba ustaziyata Kuma Malamata!" Murmushi tayi soboda yanda yayi maganan tana dan kawar dakanta cikin turo karamin bakinta, mikewa yayi yana shafa laulausar suman kanshi duk abinda sukeyi idanuwan Mom nakansu, ajiyar zuciya tasauke tana maimaita Kalman istgfari acikin zuciyarta, Maram ceh tace "Toh muntafi kawata Allah yakara karfin jiki" "Ameen"tafada cikin sanyin murya tana danne hawayenta,fita sukayi inda yarage sauran Zuly, Mourad, Mom dakuma yen gidansu! "Toh muma mun tafi Allah yakara karfin jiki"yafada yana mikar da Zuly wacce sai zumburo baki takeyi, Suna fita daga ward din ta fauce hannunta tareda cikawa bujenta iska! Cikeda damuwa yabi bayanta ganin yanda tadauki zafi alokaci guda, bude mata gaban mota tayi tashiga ko kallonshi batayi bah ta koma owners corner din motan wato gidan baya tazauna tareda slamming kofa, Dayan bangaren yakoma yabude bayan motan tareda zama agefenta, matsawa tayi ganin yanda ya matsota Kaman zai shige mata jiki Gani kawai tayi yadaura kanshi akan cinyarta, cikin rawar murya yace "Zulynah yanzu akan abinda nafada dazu kike fushi dani?" Hankalin ta bakaramin tashi yayi bah jin muryanshi kaman na mai shirin yin kuka, hannun tasa asamar kanshi tana shafa sumarshi "bakai bane!"tafada cikin shagwaba "Toh shikenan bazamuyi honeymoon dinmu a Nigeria bah sai ki zaba mana inda zamuyi ko bahaka bah?"yafada yana dago kanshi tareda shafan gefen fuskarta Kura mishi idanuwa tayi kafin tasaki murmushi tace "wai ma don miye kanace sai munyi Honeymoon namu a Nigeria neh?" "Toh Zulynah banda abinki ai Inaga duka kasashen waje da-daya neh bamuje bah so why not muyi honeymoon namu anan
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138