Skip to content

Chapter 160

Chapter 160

Bakar Taada Book One Complete Hausa Novel 1,195 words 0 views Progress saved
Download Book

zama abu d'aya ba. Amma hassada da jahilci da suka samu gindin zama a gidan yanzu ya yi k'aura. Dada tana nan gar da ita. Umrah duk shekara. Tijjani ya tsaya mata. Ta kuma rungumi istigifari. Komai na ce mata na gyara zata karba babu inkari. Idan na so nishadi ma a wajen ta nake yini tana d'ora mini karatukan ta masu sanya ni dariya da tuna baya. Hatta kangire alherina na isarsu. Har yau din nan da Tijjani ya zama attajiri Ina matukar Jin dadin aikina da kuma sana'a ta domin idan a na je na yiwa first lady kunshi makuden kudade take zuba mini a jaka. Idan zan yiwa dangin uwata alheri bana jiran Tijjani. Duk da shima yana iyakacin kokarinsa. Haka nan yadda nake son ganin dakin Gwaggo da kayan ciye ciye haka nake gani, domin bayan siyayyar kayan abinci na duka gida da Tijjani yake yi. Ina warewa na yiwa uwata hidimar da dace da ita. Suma matan gidan na kan yi musu amma ba kamar ita ba. Tunda dukkan y'aya'n k'ofarmu sai da nasan yadda aka yi aka bawa kowa upper aiki. Duk dai k'ananun ma'aikata ne . Amma dai duk wata zasu ji albashinsu. Hatta Yaya Ummi ta samu aiki a woman center tana koyawa dinki tunda ta iya. Sannan Tijjani ya dauki nauyin karatun y'ayanta biyu maza da suka kammala sakandire a jami'ar Ahamadu Bello da take Zaria. Suna Karantar manyan kwasa kwasai domin sosai suke da hazaka. Har su Maijidda da su Saratu. Nazira kuwa koyarwa take yi tunda ta cigaba da karatunta tunda mijinta dan boko ne. Amaryar Yaya J a gidan radiom Toro ta samu aiki. Tuni ya farfado. Maijidda ce a BAUCHI a amaryar na Toro saboda aikinta. *** Waya muke da Nazira akan maganin rage tumbin ya ya isa gareta. Maimakon ta yi mini godiya sai sababi take yi mini tana ce wa "Yabi ban ga Malaysian Fabrics a ciki ba. Ban ga mayukan Oriflame da maclen da kika mini alkawari ba. Ban ga supplement din GHT na FASEELAT ba. Haka nan babu yajin Annur". Na yi dariya na ce "Adda Nazi ke ce kadai kike gatsa Yabi! Ina ce ke shaidace bayan hajjin da na yi ina ciki, na yi a yanzu kan girmana ma? Ta ja tsaki ta ce "Ba zance Hajiyan ba. Yar mitsitsiya da ke sai son girman tsiya.". Na yi dariya na ce "To kwantar da hankalinki gobe Aish lame zata zo garin zata tsaya ta gaida Dada zata taho miki da su. Kinsan wannan Yaya Ummi aka aikowa ta Jos." Ko ma na baki lambarta sai ki zabi duka abin da kike so yayata". Ta yi dariya ta ce "Yanzu na ji magana. To sai anjima hakima ta Yaya Bulkachuwa ". Na yi dariya na cigaba da karatun littafin *Ya za'a yi?* da nake yi a waya na marubuciya *Binta Abbale*. Labarin ya ja hankalina. Tuni na tura kudina ina paid group din ta dan na ji yadda za'a warware wannan dambarwar. *Tuni kuma nake group din Gaskiyar lamari na Nazeefa Nashe*da yake dad'i kamar kada shafi ya k'are *YA KAMATA ACE Y'AN JAHAR BAUCHI SUN SAYI LITTAFIN NAN RUTUTU KO DAN SU RAMA MINI K'AUNAR DA NAKE YIWA JAHARSU* 🥰 *IDAN KE Y'AR BAUCHI CE MUSSAMAN TORO KO BULKACHUWA AMMA BAKI SIYA BA, NA TAYA KI JIN KUNYAR WANNAN LAMARIN* *Fatan alheri GAREKU GABADAYA*. 😀 Ina kwance kan gado ya shigo yana sab'e da Halifa. Na kalle shi ya zama CIKAKKEN mutum mai cike da Kamala. Tuni na fara hango shi a matsayin gwamnan gobe. Wato jihar BAUCHI ta jima tana yin zatan gwamnoni dogaye farare masu farar aniya. A fili na ce "Allah ga Baban 2 a cigaba da yi masa afuwa da rahama. A Buda masa kirijinsa a bashi ikon sauken nauyin jama'a babu gajiyawa. A cika zuciyarsa da son Hajiya Yabi da tausayinta da mararinta babu gundaura." Ya kwashe da dariya sosai ya ce "Ubangijinma sai kin ce masa ke Hajiya ce?" Na ce "To ai tunda zuwa gabar ne sharadin zama Hajiya ai tuni ita ce tun banzo duniya ba" Ya rungume ni ya ce "Hakane Hajiya little. Ina matukar farinciki da ya burina ya cika na kai ki gabas Hajiya. Dukkan burikan sun cika fatana Allah ya cigaba da bani lafiyar da zan ciyar da ku halali na jiyar da ke dad'in duniya dan ki gane ba komai a gabana da ya wuce ki idan kika cire Babah". Na langabar da kaina a jikknsa na ce "Ina godiya. Ubangiji ka so Tijjani, ka karba daga gare shi. Ina godiya bisa kaddara mini ya zama mijina, ina fatan ka tabbatar mini da shi har a aljanna." Ya dinga Ameen dear Hajiya. Allah ya cigaba da iya miki, ya mayar da makiyanki fadawanki, ya shirya mana zuriarmu. Muddin rai ke ce tauraruwar zuciyata." Daidai lokacin naji dirin mota tabbacin Yara sun dawo, daga school na yi maza na zame nasan Hamim idan bai ganni a falo ba sai ya biyo ni daki. Ilah kuwa ya murda kofa ya shigo. Ya ce "Baban 2 Sannu da gida". "Sannu dai Baban Marina. Tijjani ya fad'a da murmushi. Ya iso gare ni ya rik'e hannuna ya ce "Ammi mun dawo". Na ce "To sannu a je a cire uniform a yi wanka tunda kun yi sallah a school". Ya ce "To ya juya zuwa dakinsu." Yana fita Hanif ya shigo. Ya bude baki ya ce "Baban 2 yau baka je ofis ba?" Ya ce "Hutawa nake yi Baban Bulkachuwa". Ya rik'e baki ya ce "Gaskiya Baban 2 ba'a haka. Babu kyau fashi tamkar tauye mudu ne. Mai tauye mudu kuwa d'an wuta ne". Ya janyo yaron jikinsa ya ce "Na gode da tunasarwa Babana. Zan kiyaye". Ya sake shi ya matso gare ni ya dafa ni ya ce "Ammi sannu da gida ina Husna my dear?" Da murmushi na ce "Tana wajen Dada! Ka je ka yi wanka sai ka je ka ganta." Ya ce "Tom". Ya ja hannun Halifa da yake zaune a k'asa yana wasa da kayan wasan da Tijjani ya ajiye masa. Ya juya ya tafi amma Halifa ya saka kukan sai ya dauke shi. Haka ya dawo ya dauke shi ya tafi da shi. Ni mamakin yadda Halifa yake banbance shi da Hamim nake yi. Kafin na yi magana Bulkachuwa ya ce "Wato Hamim ba k'aramin miskili ba ne. Ke ce kad'ai idan bai ganki ba zai damu. Amma daga ni har yan'uwansa baya damuwa da rashinmu. Gara ma ya damu da Hanif". Na ce "Ai Hamim danja ne, ance ni ya gado, ni kuwa ai mai son jama'a ce. Mussaman yan'uwana ". Ya ce "Hakane shima zai warware. Allah ya shirya mana su gabad'aya. Na ce "Ameen dear". Da daddare daga ni har yara muna wajen Dada ana ga sharholiya cikin farin ciki ya shigo ya gaishe ta a tsaitsaye. Ta ce "Alhaji Shehu daga tsaye yau?" Ya ce na gaji ne Dada. Ina son na kwanta. Ta ce "To babu laifi. Mu kwana lafiya." Ya tafi Yara suka bi bayansa a guje. Ta kalle ni ta ce "Haba Hajiya tashi mana ki bi bayansa. Kya bar shi da yara?" Na ce "Rabu da shi Dada

Table of Contents

Chapters

161 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161