Chapter 135
Chapter 135
biyu tak a duniya Malam ya siyo mini ita tare da katangar wankan jegon ki. Amma yau kika fasa mini da gangan?". Ita kuwa tunda ta fasa gumi yake yanko mata. Wani irin abu tamkar kiyashi take jin yana sauka daga kanta. Bakinta ya yi nauyi ainun. Daidai lokacin da Innarsu Ubaida ta shigo yiwa Dada sallama zata gidan suna. Tana ganin ruwa ya jik'a tsakar gidan ga fasasshiyar randa ta hau jaje tana ce wa "Yanzu randar nan mai kafirin sanyi yau ta hadu da ajalinta?" Da kuka Dada ta ce "Eh kuma kisan wulakanci da rainin wayo a hadu da shi. Ta ajiye ledar kayanta, ta shiga kwashe rugurguzun randar. A nan ta ga k'atuwar laya. A tsorace ta ce "Dada a 'kona wannan ko ta tsari ce?" Murya babu amo ta ce "Jefa ta a wuta bansan ko ta mece ce ba. Gidan nan kam ai tuni Malam ya kafe shi. Ba dai mugu ya ga kofar shigowa ba. Ai kuwa ana kona layar Baba ta ji nauyin da zuciyarta ta yi ta ware. Sanyin da yake ratsa ta na tsoro da zullimin yin jayayaya ta ji duk ya gudu. Ta dinga Hamdala. A zuciyarta kuwa sai gasgata surkulle a ka yi mata ita kanta. A haka Tijjani suka shigo tare da Nasiba asibiti suka je yin gwaji. Bin su kawai take yi da ido. Bak'inta sai ambaton "Hasbunallahu wa ni'imal wakil yake yi. Zufa kuma bata fasa feso mata ba. Gabadaya ta shiga alhinin BAK'AR TA'ADAR da y'ar uwarta shakikiya ta aikata a dalilin son kai da na zuciya. Ta zuba ido tana nazarin Tijjani. Gabadaya ya kasa sukuni. Idonsa ya kad'a tamkar gauta. Shima sai zufar yake yi. Ya gaishe ta a sanyaye. Ta amsa masa murya babu amo domin gabad'aya ta duniyata ta yi mata tsanani. Jira take ta ji ya yi sallama ko ta fita. Amma yana zaune, duk da bai sake Bude baki ya yi magana ba. Duk takalarsa da magana da Dada take yi. *Annur food Delicious* *Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.* *Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa* *HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna* *Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya* *08039183880* Ya dai gaishe ta a gajarce. Tsawon lokaci yana zaune. Rigarsa ta jike ta gaba saboda yadda zurlfa take keto masa tamkar mai hadiyar kunama. Fiye da shudewar mintina talatin yana zaune ba ya um ba ya um um. Gabadaya Babah ta shafa'a da miyar da take yi wa Dada. Sai tashin kauri suka ji a hancinansu. Da azama ta yunkura ta sauke. Sannan ta janye wutar ta kashe. A tausashe ta ce "Dada me za'a d'ora kuma?" Cikin bagararwa Dadan ta ce "Kashe kawai." Domin bata sakar mata fuska a dalilin tana taya autarta Maryo fishin cin mutuncin da suke k'irarin ta yi mata da ta je wajenta takanas. Ta fito da garwashin. Ta kashe sannan ta yayyafa ruwa a murhun ta kashe shi gabad'aya. Ta dawo ta zauna. Sannu a hankali Tijjani ya fara dawowa cikin nutsuwarsa. Gumin da yake yi, ya fara tsane wa. Mintina kad'an ya mik'e ya ce "Zan tafi. Babah yaushe zaki koma?" Da mamaki ta ce "Tukunna." Da hanzari ta fice yana fad'in ",Na tafi Dada". Bai ko bi takan Nasiba ba, bare ya yi mata sallama. Babah ta kasa gane al'amarin domin tamkar mai jinnu haka yake canjawa. Ta hakura ta kudiri aniyar tsananta addu'a domin ta yi imanin Ubangiji ba zai juyar da addu'ar ta ba. Sannu a hankali kwanaki suna ta shude wa har ya zama saura kwanaki goma auren da ake ta cece kuce a kansa. Lefe ne kawai ba a kai ba, an yanke shawarar idan ta je gidansa ya bata domin zuciyoyi sun kai kololuwa wajen fusata. * Da safe bayan ya tafi da yara makaranta, shi kuma ya wuce Dass. Ina zaune a falo ni kad'ai, kuka kawai nake yi, irin kukan nan da yake zuwa ko da baka so ba. Gabad'aya duniyar ta mini zafi. Idan na tuna saura kwanaki 'kalilan na fara raba Bulkachuwa da Nasiba sai na ji ina fatan mutuwa ta dauke ni kawai. Na kifa kai a hannun kujera ina kuka tamkar mai wake, domin bilhakki na Bude baki nake yi. Ba zato waya ta hau kuwwa. Na mika hannu a dalilin Gwaggo kawai na saka taken da yake tashi. Sai da na yi jarumtar shanye kukan sannan na dauka. Murya ta kawai ta ji. Ta tausasa harshe ta ce "Kuka kike yi ne Yabi?" Haka kawai ta fad'a na rushe da kuka mai tsananin gaske. Cikin kuka sosai na ce "Gwoggo ba zan iya ba, zuciyata na mini ciwo, tana zafi mai radadi." Ta numfasa ta ce ",Zaki iya mana. Ai ba a kanki aka fara yin kishiya ba, ba kuma za'a kare a kanki ba". Da rawar murya na ce "Amma dai kishiya irin tawa Gwaggo zan zama cikin mutane kad'an da aka yiwa irin ta. Mena yiwa Tijjani da zai mini irin wannan cin mutuncin a rayuwata?" Da taushi sosai ta ce "Nutsu ki ji ni! Shawara zan ba ki, ba umarni ba, kinsan umarni wajibi ne ki mini biyayya. Ita kuwa shawara sai kin so za ki bi. Amma idan kika bi zai fi miki alheri fiye da barin." Ta nisa tare da ce wa "Duk runtsi kada ki ce mijinki ya sake ki matukar bai keta haddi da alfarmar shari'a ko ta aure ba. Sannan ki yi dukkan iyawar ki, kada ki nuna damuwa ko gazawarki a gaban mahaifin ki Yabi. Ya damu da halin da kike ciki. Ki daure, ba abin da ba zai wuce ba, sai ikon Allah". Na yi shiru illah kukan da nake yi mata tamkar zan shid'e. Cikin jarumta ainun ta ce "Allah ya sassauta miki, ba komai kin ji. To ban da ma kin saka damuwa a ranki ai bai kamata al'amarin duniya ya susuta ki irin haka ba Yabi. Kinsan kalubalen da yake gaban ki kuwa? Kwanciyar kabari kad'ai da muna saka ta a gabanmu da bamu bari kalubalen duniya ya kidima mu ya shagaltar da mu yiwa kanmu tanadin kwanciyar da Ubangiji kad'ai yasan adadin tsayin ta ba. Me yasa kishi ya ke sawa mu manta Annabi ya ce mu yawaita sadaka, sallah da istigifari. Domin ya hango mataye da yawa yan'wuta ne. Kuma tsananta kishi alamu ne, na mace ta barranta kanta daga ayar da Ubangiji ya saukar. Wacce kuwa ta barranta daga imani da ayar Allah. La budda tana cikin hatsarin kafirta matukar bata gaggauta tuba tare da yin hak'uri cikin hukuncin da Ubangiji ya halasta ba." Tsikar jikina ta zuba k'warai da gaske. Na sassauta kukan da nake yi. Ta sake sassauta wa ta ce "Ki yawaita karatun kura'ani domin karanta shi kad'ai yana wanke tsatsar zuciya. Ki yawaita sallah. Ki rungumi y'aya'nki da sana'ar ki. Miji kuwa kada ki zalunce shi, kada ki tauye shi, kada ki hana shi samun nutsuwa da ke ko a gidansa. Illah iyaka ki sassauta zazzafar soyayyar da zata saka ki halaka, ki
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161