Chapter 105
Chapter 105
isa haka". Ta d'ago ta ce "Yarinya me kike fa'da ne? Kina son ki ce wai dak'ashin za'a bari su sha?". Cikin girmama wa ta ce "Eh Dada. Domin alfanunsa mai yawa ne a jikin jariri. Shine rigakafi na farko da Allah subhanahu wa ta'ala ya fara yiwa dan-adam da shi." Dada ta bar komai ta kafe ta da manyan idanuwanta ta ce "To sannun ki, amma su wadannan baza su sha datti ba. Kullum a cikin yiwa Allah da ma'aiki k'arya ku ke. Allah dai ya shiryeku idan zaku shiryu". *GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATTUN SAIWOWI NA MUSSAMAN KUMA GANGANRIYA DAGA CHADI* *IDAN KINA DA KANWA KI DIYAR DA ZAKI AURAR TO KI ZO KI JARRABA WADANNAN KAYAN DA BABU ASARA KO ALGUS A CIKINSU*. *SANNAN KE MA DA KIKA KWANA BIYU A DAKI AKWAI BUKATAR KI SABUNTA KANKI* *AKWIA SAIWOWIN SANYI* AKWAI SAIWOWIN DAHUWAR KAZA* *AKWAI SAIWOWIN DAHUWAR TATTABATU* *AKWIA SAIWOWIN TSUMI* *AKWAI PACKAGE DIN MAGANIN SANYI SADIDAN* *AKWIA PACKAGE DIN AMARYA* *AKWAI PACKAGE DIN MAIJEGO* *AKWAI KAYAYYAKIN MASU INGANCI A FARASHI MAI RAHUSA*. *AKWAI GORAN TULA SYRUP* *AKWAI GORAN TULA FRUIT* *INA AIKAWA KO WANNE GARI A FAD'IN TARAYYAR NIGERIA* *, SO SU MINI MAGANA TA WANNAN LAMBAR 08032773332* *DAN ALLAH SERIOUS BUYER'S*. Ta sake rank'wafawa da nufin yin abin da ta yi niyya. Ma'aikaciyar ta ce "A a Dada daure ki yi hakuri. A yanzu Asiya ba a hannunku take ba. Tana hannun gwamnati ne da kuma hukumar lafiya. Dan haka duk abin da za'a yi mata dole zai kasance k'arkashin kulawar hukumar asibiti ne. Bijire wa hakan kuma yana iya sawa mu gurfanar da mutum gaban kuliya. Dan haka ki yi ha'kuri ki bar hukuma ta yi aikinta. Wannan karon kam a zabure ta ce "ke yarinya kar ki mini iyashege kin ji. Dan Allah falfala da gudu ki kirawo mini hukumar mu yi arangama domin mutuwa ce ka'dai zata hana ni matse wa Yabi mataccen nono marar amfani, ba ku da kuke yiwa masu jajayen kunne bauta ba." Ta murmusa ka'dan ganin Dada ta kufula da yawa. Ta ce "Dada abin bana b'acin rai ba ne. Ki Fahimci bayanina. A da an rayu cikin duhun kan cewar nonon farko mai kalar rawaya matacce ne kuma mai illah. A yanzu da ilimi ya cika duniya masana kimiyya sun gano d'inbin amfanin da Allah ya ajiye a nonon uwa. Mussaman na awannin farko da haihuwa. Yana rigakafin ciwon hanta, k'oda, huhu. Yana hana tasirin ciwon k'yanda da tarin fuka, da shawara. Yana k'arawa jariri kaifin k'wak'walwa, yana kuma daidaita k'asusuwansu". Dada ta dauki salati tare da cewa "Ni Binta ina ga ni da sauraron kinaya. To da kunsan da hakan amma kuka sake k'ak'alo allaurar da ake daukar watanni ana yiwa yara babu tausayi bare imani da sunan rigakafi ce. Yanzu wanne ne gaskiyar magana kenan?" Malamar ta yi murmushi ta ce ko wanne gaskiya ne Dada". Ta ce "To ku ri'ke gaskiyarku, amma ni ban yarda da ita ba, bare kuma na yi muku biyayya" Da walwala ta ce "Shike nan Dada ki ri'ke fahimtarki. Amma tunda har aka kawo Asiya asibiti to wajibi ne abi ka'idojin hukumar lafiya. Idan ba hakan ba zamu sallame ku ne. Komai ya biyo baya kuma babu ruwanmu. Kafin haka kuma, zan rubuta tirjiyar da kuka yi, idan abu marar da'di ya biyo baya ke ce da d'aukar alhakin komai. Domin na tabbatar za ki ga ni". Nan da nan Dada ta d'auki salati tare da fashe wa da kuka ta koma gefe tana ce wa "Yau ko da wa kike tak'ama sai na yi sharia da ke tunda kika ce zan ga ni." Ita kuwa bata damu ba, da alamu ma dariya Dadan ta bata. Domin sai guntse bakinta take yi. Ta kuma d'ora mini yaron tana nuna mini yadda zan tallafe shi a duk sadda zan shayar da su gudun kada su dinga kware wa ko su kasa samun iska. A lokacin da yaron ya fara tsotso wani irin rad'ad'i ya ratsa ni. Na zabura ta ce "Sannu". Na kasa amasawa, kunyar idon su Babah ya hana na yi kwarmato. A daddafe ya sha. Ta dauke shi, ta dauko d'ayan. Ya fara sha ke nan Tijjani ya iso da kayayyaki a hannunsa. Ya ci birki ya tsaya yana kallon yadda take rurrufe ido tana cije wa ga yaro yana sha. Farin cikin Asiya ta zama uwar y'ay'ansa har biyu tashi guda yana matu'kar saka shi tsumaye. Amma ganin Dada na kuka ya takaita masa murnar da yake ciki. Ya ajiye kayan a gefe ya isa kusa da da ita. Yasa hannu ya ru'ko hannunta da take share hawaye. A tausashe ya ce "Dada kukan me kike yi haka ne? Ina ce d'azu kika dinga rangwad'a murnar alherin da ya samu a cikin alhalinki na samun tagwaye?" Cikin kuka mai yawa ta ce "Ayyah mai sunan manya ai wannan ja'irar yarinya tana neman mayar mini da murnar tawa ciki. Ba yadda ban yi ba kada ta bawa yaran nan dattin nono amma sai da ta kafe ta basu suka shanye. Idan an yi sa'a sun rayu, to tabbas zasu tashi da kukan da baya jin rarrashi ga yawan kumburin ciki, sannan mafi muni suna iya samun tawaya a hankalinsu". Ta ke ce da kuka mai tsananin gaske. Fargaba ta shige shi ainun. A ki'dime ya ce "jariran aka yiwa sanadin raunin k'wak'walwa Dada?" Ta kad'a masa kai tabbacin eh. Tare da ce wa "Kuma Wallahi tunda ta ce mini zan ga ni, sai na yi shari'a da ita ko da me take tak'ama kuwa. Ba zata lahanta mini tattaba kunne, sannan ta bini da mugun k'ulli na kuma ha'kura ba. Ko waye ubanta a garin Toro da kewaye sai mun je gaban gatan marar gata wato kuliya". Ya sake ta ya isa gaban su yana leka yadda a ke bawa yaron nono. A gigice ya ce "Baiwar Allah ya zaki dage sai sun sha abin da zai zame musu illah?" Ya fara k'ok'arin karb'e yaron. Babah ta Bulkachuwa ta yi wani irin tari mai kama da kashedi. Nan da nan ya ankara ya fahimci gargadi ta yi masa. Ya d'aure ya saki yaron. Ya koma gefe amma zuciyarsa ta dinga wani irin tsalle. Dada kuma ta sake tsananta kukan tana fa'din "Duk wannan iyakacin da aka nuna mini akan y'ay'an nan baki ji ciwo ba ashe? Ba ki hana ta ci mutuncin uwarki ba, baki hana ta nakasa rayuwar y'an mala'ikun Lillahi ba. Shi ya zo zai kwatar mana yancinmu ni da su shine zaki hana shi? Eh lallai! To ki je na barwa hukumar asibitin ke, ranar da zamu yi shari'a da su ki zame musu shaida ki kwaye wa uwarki da jikokinki baya". Ta juya ta fice tana kuka bilhakki. Yayin da Babah da Inna da kuma Mama suka bita da nufin lallashi da ban baki a gare ta. D'akin ya yi saura daga mu sai Yaya Ummi. Ya d'auki yaron ya rungume shi tsam tsam. Yana ta tofa masa addu'ar da ta zo bakinsa. Ya kalle ni ya ce "Sannu Asiya! Ubangiji ya yi miki albarka, ya baki lafiya, ya baki hakuri da kuma juriyar raino da tarbiya". Na kalle shi ina jin wata irin
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161