Skip to content

Chapter 11

Chapter 11

Bakar Taada Book One Complete Hausa Novel 1,204 words 0 views Progress saved
Download Book

marubuciyar akan lambarta 08167768704 domin samun free pages na labarin kai tsaye, kafin ku kai ga yin payment.Kar ku manta it's a true life story,don haka ku hanzarta shiga cikin tafiyar da babu ✍🏻 danasanin bin alƙaminsa.... * *Shafin nan kyauta ne sukutum ga mamana* *Hajiya Hadiza Sodangi* *Na gode sosai Ubangiji ya shirya zuria* 7&8. Maganar Baban Marina ta dawo da ni tunanin da nake yi. Kamar a sama na ji ya ce "Na gode miki Asiya! Duk yadda nake jan kunnenki akan b'atawa Dada rai, da kuma dukan yaran gidan nan ba kya ji, saboda kin riga kin zama y'ar kuka. Uwarki kullum cikin yi miki kashedi akan shiga fa'dan yara da kuma tsokanar Dada, amma duk a iska ko? Na gode sosai da wannan bacin rai da kika sanya ni, Allah ya shirye ki". Ya tsugunna gaban Dada ya ce "Ki yi ha'kuri! Halin Asiya ni kaina ha'kuri nake yi da ita, amma zan dauki mataki akan ta'ba ki da take yi". Ta kyabe baki ta ce "To ka fara dan takidin aurensu. Jiya mun tattauna da kannenka sun ce su babu matsala ko yaushe auren ya zo a shirye suke, kai dai za'a fa'dawa ka fara tanadin tunda yaran ka har biyu ne". Ya yi gyara murya cikin k'arfin hali ya ce "Babu damuwa Dada ina saka rai Ubangiji zai kawo mini hanyar da zan samu na yi musu iya abin da zan iya." Ta murmusa tamkar ba ita ce mai kuka tana face majina ba. Ta ce "To babu laifi Allah ya basu na gari, masu kuma ha'kuri, domin mai yakana ne zai iya zama da Yabi dan wuyar zamanta ya kai inda ya kai, ba inda ta baro uwarta". Cikin sanyin jiki Baba ya mike yana cewa"Dada sai da safe mu kwana lafiya". Ta amsa masa da fa'din "Allah ya tashe mu lafiya". Na mike, Nazira ma ta biyo ni muka fice, ba tare da mun ce uffan ba. Domin na sake fusata da ta ce sun tattauna da kannensa amma shi ba'a saka shi cikin zaman ba. Muna jin ta tana fa'din "Wanda Allah ya bashi tsawon rai zai yi kallon tak'ama a wajen ki Yabi. Yarinya da ke amma kusan ke kike juya shashinku gaba'daya. Kina tashi Yayarki ta biki zungui zungui ko sallama ta kasa yi mini saboda tana rarrashin zuciyarki?". Ban juya ba, bare na tanka mata, balle kuma Nazira da take da sau'kin hali. Muna shiga shashinmu muka yi turus a dalilin halin da muka ga mahaifinmu a ciki, zaune yake akan tabarma a tsakargida. Sai fifita Gwaggo take yi masa, gumi na yanko masa babu kakkautawa. Muka isa gabansa, muka tsugunna, baki na rawa na ce "Sannu Babanmu! Abin mamaki sai ya daga mini hannu tabbacin ya amsa gaisuwar tawa. Nazira ma ta yi masa sannu ya amsa ta hanyar gyada mata kai. Mama ta fito daga bandaki ta kalle ni ta ce "Wannan ja'irar yarinyar sai kin zama sanadin mayar da kananun ya'yansa marayu, fitananniya tabtacciya. Ai duk gwanin na iya a rana ya ke" Ta ja tsaki mai tsanani ta wuce d'akinta. Bata jima da shiga ba ta k'walawa Nazira kira, ta mike a hanzarce ta nufi dakin nasu. Daidai lokacin Baba ya dan samu sau'kin zufar da take karyo masa. Ya yafito ni, jiki na rawa na isa gabansa. Ga mamakina sai ya mik'o mini hannunsa na dama. Hannu bibbiyu na ri'ke hannun nasa, cikin barin jiki gaba'daya. A sanyaye ya ce "Ina alfahari da ke Yabi! Kafatalin ya'yana ke nake da tabbaci akan ba zaki cigaba da yin mini *Bak'ar Ta'ada* ta y'an ubanci ba, na tabbatar da hakan. Ina saka rai ta dalilinki yarana zasu dawo tsintsiya. Na so ace da wuri na haife ki Yabi. Da al'amuran da suka dame ni basu yi mini tsananin da nake ciki ba. Amma Alhamdulillah! Ubangijinmu baya kuskure na gode masa, ina kuma tuba a gare shi." Hawaye tuni ya goce mini dukkan zuciyata a jagule take da tsananin tausayin Mahaifina da a yau nake ganin wani irin tashin hankali da raunin da ban ta'ba ganinsa a ciki ba. Gwaggo tana fifita, tana kuma share k'walla.y Ya numfasa ya ce "Idan na mutu Yabi, duk runtsi ku gaisa da yan'uwana, ko ba zasu taimakeku ba, to lallai ku dinga saka su a cikin al'muranku, idan kina yi, sannu a hankali zaki samu wanda zasu yi koyi da ke, tunda tun yanzu al'amura sun haska ke ce mai tsayayyen ra'ayi wanda yafi kusa da kyau da kuma dace wa." Murya na rawa na ce "Mu sasu a alamuranmu ko da ba zasu taimakemu ba, ko da idan mun fa'da musun ba zasu dauki al'amarin namu da girma ba?" Ya sake damk'e hannuna ya ce "Haka nake so Yabi". Da karfin zuciya na ce "Da Ikon Ubangiji zan yi yak'i da dukkan zuciyata na yi hakan. Amma ina ro'kon arziki ka mini afuwa, ka yafe mini muzancin da na janyo maka dazu". Ya girgiza kai ya ce "Baki yi laifi ba, na sani. Sannan su d'in ma bana son ki d'auki abin da suka yi mini a matsayin muzanci ko tozarci, na sani baki da sauki, kina da ru'ko, dan haka na umarce ki, ki manta komai". Na murmusa hawaye na kwaranyo wa na ce "Shi kenan Babanmu! Allah ya kara maka lafiya da nisan kwana, yadda a ke mini habaicin tunda aka haife ni ka tsiyace, ina ro'kon Ubangiji kullum, ya saka idan na girma na samu sanadin da arzikinka zai dawo ta dalilina fiye da wadda ka rasa a shekarar da na iso duniya". Ya ce "Rabu da maganar jahilai, ko iya hakan na ga ni ai na gode, sanadin sana'arki na daina fargabar a tambaye ni ku'din sabulu a gidana. Alherin da kika janyo mini mai yawa ne, mafi farin-ciki a ciki shine wanda kike yarda ya'yan da na haifa duka daya ne a wajenki ta fuskantar mua'amala ta zahiri." Da'di ya tsirga mini ban ta'ba zaton Baba ya fahimci yadda nake da ra'ayin rikau akan kannena ba, bansan ya fahimci ina tare musu fa'da ba, hakanan ban san hakan yana yi masa da'di ba, tunda kullum a cikin kirarin bani da hakuri yake. Sannan kuma baya ta'ba nuna mini ina abin a yaba, sai dai ya ce ai duka yan'uwane tunda ragowar ma y'ay'ansa ne da yan'uwansa suka haifa masa. Cikin son na sake k'arfafa nasa guiwa na ce "Duk d'an da ka haifa ina jin sonsa har cikin zuciyata Baba". Idonsa ya ciko da k'wallah cikin k'arfin hali ya ce "Allah ka shirya mini yarana, ka saukaka musu, ka basu lafiya, ka cika zuciyarsu da tsoronka, ka jefa soyayya da tausayin juna a tsakaninsu. Allah ya yi miki albarka Yabi". Daga ni har Gwaggo muka hau fa'din "Ameen ameen". Na kalli Gwaggo na ga hawaye ya goce mata, jikina ya sake yin sanyi, domin ita din wata irin mace ce mai k'arfin zuciya k'warai da gaske, abin da zai saka ta yi kuka to kuwa ya girgiza ta ba ka'dan ba, duk tsananin da take fuskanta a rayuwar gidanmu ban ta'ba ganin ta yi kuka ba. Na yi kasa da kaina cikin rauni mai yawa na ce "Ameen Baba! Allah ya kara maka

Table of Contents

Chapters

161 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161