Skip to content

Chapter 115

Chapter 115

Bakar Taada Book One Complete Hausa Novel 1,198 words 0 views Progress saved
Download Book

danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya* *08039183880* ✍️ *Oriflame products* *Daga make up artist din Guduyo* *Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko Kuma kina sha'awar yin register da su*. *Ki tuntubemi babbar dealer din su Aisha lame* *Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea* *Akwai pop corn* *07036662633* *JAN HANKALI* *BAN YARDA A HADA MINI DOCUMENT BA! BAN AMINCE BA.* *DUK WACCE TA YI HAKAN YANZU, KO BAYAN NA KAMMALA LABARIN NAN, WALLAHI NA KAI TA K'ARA WAJEN UBANGIJI.* *FATAN ALHERI GA* *Aunty Umma Kulsum Muhd Kumo* *Aunty Maryam Saminu Sulaimanu* *Gaisuwa da fatan alheri, na gode sosai da alherinku a gare ni*. *Yabo da godiya ga* *Mamana* *Hajiya Zahra Shehu* *Fatan alheri mai yawa a gare ki da ahalin ki* Tsawon lokaci yana tunanin abin yi. Ya rasa inda zai dosa meman ta. Ya tabbatar ba zata nufi Toro ba. Ya tambayi kansa to ina zata tafi har tana fa'din idan dare ya yi zata kwana?. Kukan Hamim na sake rib'anya tashin hankalin da yake ciki. Ga haushinta, ga zullumin fishinta gaba'daya sun ha'du sun yi masa rubdugu. Ya mike ya shiga gidan, ya tarar ta kammala abincin da take yi. Ransa ya sake b'aci da abin da Yabi ta yi, wato manufarta ta bar musu gidan su yi komai ma. Cikin rashin sukuni ya ce "Ha'da kayan ki zan kai ki tasha ki koma gida. Tafiya ta same ni zuwa gadar mewa. Ba zai yiwu kuma na bar ki ke ka'dai a gidan ba." Cikin nutsuwa ta ce "To". Amma yaran fa?" Cikin rashin sukuni ya ce "Zan kai su wajenta daga can, tunda hanya ce". A hankali ta ce "To ko zamu tafi gaba'daya ina ajiye mu a wajenta sai mu dawo gobe da ita". Da rawar ya ce "A a, mu je dai na kai ki tashar, ba zai yiwu na yi ta yawon kasuwa da ke ba." Tunda ya ajiye ta a tasha yake gararanba a titunan Bauchi. Gaba'daya ya rasa ta inda zai fara nemanta. Nasiba kuwa da ta Isa Toro a gidan Marina ta tarar da gyatumarta tare da Dada. Cikin mamaki Dada ta ce "Ke da kika ce sai an gan ki kuma sai ki dawo, duka duka yaushe kika tafi ne?" Cikin nutsuwa ta ce "Yabin ce ta tafi Kangire dubiya. Shi kuma ya ce na taho tunda kwana zata yi". Dada ta ce "Ikon Allah. Ga kuma uwatata bata fadi wani abu ya samu ba, bare mu yi mata ja je". Sai lokacin Baba Maryo ta ce "Hmm Wallahi ba abin da ya faru, kawai zamanta ne bata so a gidan. Shi kuma da yake salallamamme ne shine ya ce ki taho. Yarinya k'ank'anuwa sai azabar iya barikanci. To duk shure shuren kaza baya hana a dirza mata wuka. Yabi akwai tuggu Wallahi shi yasa na washe ta, bata da kunya ko kad'an bare mutunci". *** Da azahar na dira a Bulkachuwa. Babah sai ganina ta yi kwatsam. A sanyaye ta shiga yi mini barka da zuwa. Sai da na yi sallah ta bani abinci da ruwa, na ta'ba ka'dan na rufe. Ta zuba mini ido ainun. Ta ce "Wai mene ne damuwar ki ne Yabi? Maimakon tunda yanzu ba shayarwa kike yi ba, ki murje ki cike, amma kullum sai fige wa kike yi tamkar wacce ake tsakurarki?." Na yi k'asa da kaina, ba tare da na ce komai ba. A tausashe ta ce "Yanzu me yasa kika taho ba shiri ba komài?" Na fara hawaye, ba tare da na bu'de baki na ce komai ba. Ta ri'ke hannuna ta ce "Da ke da Ihisan daya nake jinku. Dan haka zan fa'da miki gaskiya. Gaba'daya aure hakuri ne. Ba yadda ake so ake ga ni ba. Idan Ubangiji yasa farin yafi ba'kin yawa a cikin zamantakewar sai a yi ta gode wa Allah. A kuma yi hakuri da inda aka kuskure. Idan kuwa ba hakan ba sai ki ga gidan aure ya zama tamkar kurku dan tsanani. Adadin mutuwar aure ya yi ta tunbatsa. Yin sassauci da kawaici babban jigo ne da yake rike da gidajen aure. Cikin kuka na ce "Wallahi ina yi." Ta ce "Na sani. Yanzu fa'da mini abin da ya yi miki har kika kasa hadiye wa" Cikin kuka na tsara mata yadda muka yi da shi, ban yiwa al'amarin kwaskwarima ba. Da kuma kafewar da ya yi sai ta zauna da mu saboda tana da alkairai masu yawa a idonsa. Cikin kuka na ce "Ni kuma Wallahi bazan yarda na zauna da ita ba". Ta yi shiru, na tsawon lokaci kafin ta ce "Tashi ki je d'aki ki yi kwanciyar ki. Kar kisa wannan maganar a ranki. Kina da gaskiya dan hakan zan tsaya miki, da kuwa baki da gaskiya da a yau zan mayar da ke dakinki". Dad'i ya kama ni. Babah ta fahimci irin rad'ad'in da nake ji. Ina kwance ta shigo ta ce "Kuma sai kika bar mata yaran?" Fuska ba walwala na ce "Eh". Ta ce "Da kin taho mini da su, ina cikin kewarsu ainun. Amma bar masa din da kika yi akwai hikima mai yawa tunda ba sha suke yi ba. Kukan Hamim kadai ya ishe su ai. Ki yi zamanki ba wanda zai san kina nan tunda Umman gidan nan tana garinsu tafi wata a can. Ko Nasiru ma baya gari. Aliyu ne ya ce zai zo yau, to kuma ya fasa sai satin sama, saboda zasu je Ibadan". Ta dauki abin da zata dauka ta fice. Tana fa'din "Da ni yake zancen". Sai da dare ya fara ja sannan ya koma gida. Bayan Nasiba ta masa text din ta sauka lafiya. Tunda ta kira shi ya fi sau biyar yana gani amma bai dauka ba. Da asuba ya kira wayar Yaya Ummi. A d'an tsorace ta ce "Yaya Bulkachuwa barka da asuba" Murya na amo ya ce "Ummilolo taimake ni ki bani lambar mijinki na nemi izinin aikenki yanzu zuwa gidan Marina". Ta ce yana jinka ma yanzu haka, na saka ta a sifika ka tambaye shi." Ya bu'de murya cikin ladabi ya gaishe shi. Ya kuma roki alfarmar zai aiki Ummi zuwa gidan akan wani al'amari da tayar masa da hankali. Nan da nan ya ce "Babu komai na amince ta je. Ya mika wayar ga Ummi. Ta ce "Ya ya ne Yaya Bulkachuwa?". Cikin zullumi ya ce "Asiya ce ta yi mini yaji Ummi! Tun jiya ta fice ta bar mini gidan da yara." A zabure ta ce "Subhanallah a kan me Yaya Bulkachuwa?" A sanyaye ya ce "Hmm! Kawai mu bar maganar tattauna wa ki tashi yanzu ki je gidan, ki duba ko ina. Idan kin ganta kada ki nuna komai kawai ki dawo gidanki. Ki fa'da mini sai na taho". Yana rufe baki Ummi ta ce "Gaskiyar magana ban jin Yabi zata iya zuwa gidanmu da sunan yaji. Ta tsani yamididi, tana kuma matu'kar tsoron bacin ran Baban Marina". Ya fesar da iskar damuwa ya ce "To saboda Allah ba kisan inda take ba Ummilolo?" "Wallahi ban sani ba, ko waya bamu yi da ita ba. Amma bari na je sumame gidan Nazira". Da sauri

Table of Contents

Chapters

161 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161