Chapter 99
Chapter 99
ko, ni zan fita." Gyale ta d'auka ta fesa turare ta juya zata fice, da sauri ya duro daga kan gadon yace "Ina za ki je?" Ta na kallon idon shi tace "Bak'o..." Sai kuma ta yi shiru saboda tuna ranar da ya kwamtse mata baki, rik'e k'ugu ta yi tace "Ka ban hanya mana zan wuce." Rumgumo ta ya yi jikin shi ya dawo da ita ya zaunar akan gado, ture shi ta yi tace "Malam ka daina tab'a ni mana." Sosai ya kalle ta yace "Khadija, har yanzu fa ni mijin ki ne, a labarin da ki ka bani ba ni ne na kore ki ba, amma Khadija ki na hukuntani abisa laifin da na ke tunanin ko da na aikata shi ne dadangan za ki yafe min, me ya sa haka Khadija? Kin daina so na ne yanzu? Ko kuma ba kya son ki tsufa a gida na ne yanzu kamar yanda ki ke fad'a min." Mik'ewa ta yi tsaye tace "Ni dai kawai ka fitar min daga d'aki, so ka ke mutane su d'auka wani abun ne ke faruwa anan? Dan Allah ka tashi ka fita." Yau fa ya yi niyyar ba zai bar gidan nan ba babu wani sakamako mai kyau, dan haka ya haye gadon ya gyara kwanciya ya kalle ta yace "Ba zan fita d'in ba, idan kuma ki na ganin za ki saka k'artin 'yan uwan ki ne su fitar da ni to bismillah." Mamaki ne ya sa ta zaro ido tace "Abban Bilal, yan uwan nawa ne ma k'arti? To ai ko ba k'artin banza bane tunda su na ciyar da duka girman gidan nan dama wasu dake kewayen shi." Hararan ta ya yi yace "Ni kuma na gaza ko? To ki jaraba kiran su ki gani mana idan za su iya." Rumgume hannaye ta yi tace "Amma dai kasan tsaf zan iya saka su kefa min kai cikin kwalbatin unguwar nan ko?" Wata irin dariya ya bushe da ita yace "To ki kira su mana, na fad'a mi ki ina tsoro ne." Fitowa kam ta yi daga d'akin amma abun mamaki ba kowa a falon har telebijin ma an kashe, mayar da d'akin ta yi ta rufe ta dawo ta zauna kan kujerar da ke gaban madubi, kallon ta ya yi yace "Hajia ko za ki iya samo min kayan bacci a gidan nan?" A harzuk'e ta kalle shi tace "A ina zan samo ma ka kayan bacci? Na wa zan d'auko ma ka?" Har ta yi shiru shi kuma ya fara dariya sai kuma ta kalle shi tace "Wai ma tsaya, idan na d'auko ma ka kayan baccin me za ka yi da su?" Ba alamar wasa yace "Nan zan kwana yau, tunda na fahimci ba za ki koma gidan ki ba, kinga saina raba mu ku kwana, biyu a nan biyu a can." Tasowa ta yi ta kamo hannun shi ta na fad'in "A'a wallahi, akan me? Haka kawai kasa a kafa min hak'ora, kwana a nan saboda me?" Fizge hannun shi ya yi yace "In dai ba kya son na kwana nan to ya zamar mi ki dole ki had'a kayan ki yanzun nan mu tafi na mu gidan." Cikin b'acin rai tace "Wallahi babu in da zanje, haka ake kawai ka b'ullo min ta wannan hanyar." A nutse ya kalle ta yace "Na fad'a miki ki bani hak'uri tare da lallab'a ni dan na mi ki maganin matsalar ki, amma girman kai ya hana ki ko? To ba damuwa mu ci gaba da zama a hakan tunda haka ki ke so, yarinya sai taurin kai." "Ni na fad'a ma ka wani abu na damu na?" Ta fad'a ta na nuna kan ta da yatsa, saida ya tashi zaune yace "Ke kuwa ke da damuwa, gata nan b'aro-b'aro ina gani a idon ki." Duk da idon na ta na cikin gilashi amma saida ta mitsika idon ta kafin tace "Ban gane ba fa." Kashe mata ido ya yi yace "Yaushe rabon ki da ni? Yaushe rabon da na yi wasa da ke? Hajia Dije yaushe rabon da ki ji zallar ingantacciyar madara a jikin ki?" Shiru ta yi kawai sai kallon bangon d'akin da take, murmushi ya yi yace "Shi ya sa yanzu zuciyar ki ta cika saurin hawa, ki ka cika masifa da jaraba, sannan ba kya da kuzari kamar yanda ki ke a baya, sannan hakan zai shafi lafiyar abin da ke cikin ki, saboda ni d'in nan da kika raina to lafiyayyen abincin shi na jiki na, za ki iya haifar yaron ki babu kazar-kazar a jikin shi da walwala kamar sauran yara, saboda ya rasa wani muhimmin abu da ya kamata ya samu amma kin hana shi saboda ki na bak'in ciki." Juyawa ta yi ta kalli agogo ta ga har k'arfe goma ta soma wucewa, dan dama shi ma tara ta wuce ya shigo, kallon shi ta yi tace "Dan Allah babban mutum ka tashi ka tafi dare ya yi, ni kai na bacci na ke so na yi." "Wasa ki ke ko Khadija? Yanzu ki na nufin ba ki yarda da abin da na fad'a mi ki ba kenan? To shikenan, ni dai na yi niyyar kwana anan, idan ke ki na jin kunyar kar mu wayi gari mu fito a d'aki d'aya to ki je d'akin Bilal ki kwanta." Dafe goshi ta yi tace "Na shiga uku na, Abban Bilal ya ka ke so na yi ne?" Wani kallon mamaki ya bita da shi, saukowa ya yi daga kan gadon ya tsaya daf da ita yace "Khadija, ke da kan ki, ke ce yau saboda takura da gundurar da na mi ki har ki ke iya fad'a a cikin ido na cewa kin shiga uku, Khadija me nai mi ki da zafi har haka? A gaskiya ban yi tsammanin jin wannan maganar daga bakin ki ba." Juyawa ya yi cikin sanyin jiki ya d'auki hular shi yasa ya kalle ta yace "Shikenan uwar yarima, ni zan tafi, bana iya ce mi ki ga ranar da zan dawo ba, dan gaskiya kin kashe min k'warin gwiwa na, tunda ba kya son komawa zan rabu da ke, idan kin haihu kuma sai ki min magana idan ki na buk'atar takardar ki." Kama hanya ya yi zai bar d'akin Khadija da idon ta su ka cika taf da hawaye ji ta yi kamar ta k'urma ihu, saida ya kama hannun k'ofar zai murd'a ta yi k'arfin halin janyo rigar shi da k'arfi, baya ya yo kamar zai fad'i tare da kallon ta, kafin ya ankare ta hankad'a shi kan gadon ya fad'a da k'arfi, da iya k'arfin ta ta fad'a kan shi ba tare da tunanin cikin jikin ta ba, rufe shi ta yi da duka tako ina kamar Allah ne ya aiko ta, kallon ta kawai yake bai hana ta ba sai murmushi da yake dokawa, ita kam kuka take ta na fad'in "Aikin banza kawai, ashe dama ba so na ka ke ba shi ya sa har za ka iya saki na, so ka ke kaje kai da amaryar ka ku ci amarcin ku." Ganin sosai ta ke kukan da gaskiyar ta ya sa ya kwantar da ita a k'irjin shi
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117