Chapter 17
Chapter 17
cire takalmi za ta shiga kenan Usman shi kuma ya fito, saida jikinsu ya had'e da sauri ta ja baya, sai dai kuma ta na ja da baya ta kai wa tsohuwar karo, da azama ta sake matsawa ta na fad'in "Yi hak'uri, yi hak'uri dan Allah." Wani banzan kallo Usman ya mata ya rab'ata ya wuce ya saka takalmin shi, Khadija kam ajiyar zuciya ta saune ta k'arasa shiga ciki, zaune ta yi kusan katifar da tsohon ke zaune ta aje ledar hannun ta, da murmushi tace "Baba ya jiki?" Shima da murmushin yace "Jiki da sauk'i 'yata, ya na ki jikin? Ince dai ba ki ji ciwo ba ko?" "A'a Baba, ban ji ciwo ba." "To Allah ya k'ara kiyayewa, Allah ya kare mu daga sharrin k'arfe." "Amee Baba, kuma dan Allah ka yi hak'uri, laifi na ne abin da ya faru." "Ah haba haba, 'yata ba laifin ki bane, Allah ne ya aiko ai, sai dai Allah ya k'ara kiyayewa, kuma ku dinga kula ku na tafiya a hankali." "Insha Allah Baba, nagode, ni zan wuce." Tsohuwar ce tace "Sai tafiya y'ar nan, ko ruwa baki sha ba." Da fara'a tace "Ba komai mama, ai daga na ke, kuma tare da yaya na mu ke, ya na sauri zai fita aikin shi na tsayar da shi." "Kuma gaskiya hakane kam karki tsayar da shi." Tashi ta yi ta fito ta musu sallama, tun ranar kuma Khadija ba ta sake samun damar dawowa gidan ba saboda shirye shiryen tafiyar su k'asa mai tsarki, haka lokacin tafiya ya yi kuma su ka tafi sama tare da mama da matar Ashir da ta Bashir, dan dama an had'a su da mama ne saboda dukansu zuwan su ne na farko, masha Allah sun je lafiya kuma sun dawo lafiya, dukansu sun canza musamman Khadija da dama Allah ya hallice ta da kyanta, inda ta k'awata haurunan ta da hak'oran makka guda biyu, saida su ka yi sati su na karb'ar bak'i da huta gajiya, sai dai har lokacin nan Khadija na tunanin tsohon da ta buge, tunanin ta kawai ita ce silar kwantawar shi, dan haka ta shirya da dare tare da ware kayan tsaraba dan ta kai mu su, sanye take cikin bak'ar doguwar riga har k'asa mai walkiya da kwalliya, takalma sai d'an kwalin da ta mi shi sassauk'an aji a saman kan ta, farin gilashin ta mai kewaye da bak'ar kala ya dace da fuskar ta da kuma rigar, farin man leb'e ne kawai ta shafa, yau kuma Naseer ne ya shirya zai kai ta wanda ya zo hutu, har k'ofar gidan ya dire ta shi kuma ya fito ya tsaya bakin motar, ta na zura kai cikin soron sai duhu, wayarta ta fara k'ok'arin fitowa da ita daga cikin k'aramar jakarta sai kawai ta ji ta zube a k'asa, 😂 "Ahhhhhh." K'arar da ta saki kenan lokacin da Usman ya yi gaba da ita ta fad'i zaune a k'asa, wayarta da ledar hannun ta da kuma gilashi duka sun kama gabansu, da sauri Usman ya kunna wutar ta shi wayar dan ganin wacece, " *mai gilashi*." Abinda ya fad'a kenan, sai dai mamaki ne ya lullub'e shi ganin Khadija nata lalubar inda gilashinta ya ke, tambayar da ta zo mi shi ita ce "Ba ta gani ne? Ko kuma har yanzu duhun take gani?" Ya na kallon ta har ta kai hannunta kan gilashin ta, da saurita d'auka ta mak'ala a ido, tarau taga Usman zik'au a gabanta da hasken fitila, da sauri ta mik'e tsaye ta na tattare kayan da su ka zube, shi kam sai ya ji ta ma ba shi haushi, guntun tsaki ya yi ya wuce ta cikin b'acin rai ya fice daga gidan yana fad'in "Idan dai ki ka ci gaba da anfani da gilashi haka kawai, wallahi kin kusa zama makauniya, in banda hauka har cikin dare ma sai kinyi fama da gilashi, kuma yanzu haka ma na masu larurar ido ne take sakawa." Ya na fitowa ya ga Naseer tsaye, gaisawa su ka yi cikin sanin juna, dan da Usman da Ashir sunyi aji d'aya a makarantar boko, hakan ya sa su ka zama abokai sai dai ba abota irin sosai d'in nan ba, ita ma data shiga ciki k'anan Usman da suke uba d'aya ne ya mata iso har d'akin babansu, bai gusa daga wajen ba ya na kallon fuskarta da murmushin ta ya na jin kamar yace ya na son ta, har ta taso ta fito ya rakota k'ofar gida, kallon juna su ka yi ita da Usman da suke ta hira da Naseer, sallama su ka yi Naseer ya shiga mota ita kuma ta juya ta kalli *Mannir* tace "To sai anjima ko." "Sai anjima, sai yaushe kuma?" D'an wasa ta yi da idon ta tace "Kowane lokaci ma za ka iya gani na." "Shikenan to, sai anjima." Bud'a k'ofar motar ta yi za ta shiga sai kuma ta ga Usman sai wani kallo ya ke mata kamar irin ya na jin haushin ta, dan haka ta rufe k'ofar ta zagayo wajen shi ta kalle shi cikin taushin murya da nutsuwa tace "Na ga kamar haushi na ka ke ji saboda abin da ya faru, dan Allah ku yi hak'uri ku yafe min, duk da nasan laifi na ne, amma kuma Allah ne ya aiko, ka gafarce ni idan na b'ata ma ka rai." Juyawa ta yi ta shiga motar, shi kuma juyawa ya yi ya na jan wani tsakin, bin Mannir ya yi da harara yace "Sai ka rufe bakin to sakarai, har da wani sai yaushe za ta dawo, to uwar me za ta maka idan ta dawo?" Bai jira me zaice ba ya wuce sabgar gaban shi, tun daga ranar kuma Khadija ba ta sake komawa gidan ba, dan lokuta da dama ta kan ji ta na so taje saboda tsohuwar da tsohon masu kirki da kuma saka mata albarka, amma idan ta tuna Usman sai ta share kawai, a cewar ta wannan ba shi da kirki ko kad'an, gashi da d'acin rai da zuciya, alhalin Usman kuma ba ma mazauni bane, baya cikakken sati a gida bai tafi sabgar gabanshi ba, musamman ma da iyayen ke yawan mi shi magana akan ya yi aure, shi ya sa ba ya son zaman gidan dan duk motsin shi sai suce da ya na da aure da anyi kaza, aure ba shine gabanshi ba, ya na so ya taka wani mataki kafin ya yi aure, shi ya sa ma shekarun shi *talatin da d'aya* ba sa damunshi, k'annan shi mata yan biyu da suke bi mi shi tuni suka hayayyafa a gidajensu, sannan d'aya k'anan shi da suke uwa d'aya ma yayi aurenshi shekara biyu data wuce, k'annan shi mata kuma hudu ne a gidan mazajensu, duk iskancin da suke mi shi ko a jikinshi kam, neman sisi da kwabo yasa a gaba. *Bayan wata bakwai* Khadija har ta fara karatunta na jami'a (lycée) hankali kwance, ta yi sababbi k'awaye sosai a ciki ne ta had'u da *Barira nagoma* wacce unguwarsu ke kusa da gidansu Usman, duk da Khadija ce ta bige tsohon amma ta manta da abin da ya faru, ranar kawai sun taso daga
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117