Chapter 26
Chapter 26
kuka yace "Khadija, ita na ke tausayi, sai ta haihu kafin na dawo, ba na jin za ta wuce sati ba ta haihu ba, dan duk alamu sun nuna haka, kwana hud'u ko bacci ba ta iya yi saboda ciwon baya da mara, mtss." Ya k'arashe da d'an guntun tsaki. Murtala ne yace "To ya za ayi sai hak'uri? Kuma gashi ba ka fad'a mata gaskiyar magana ba cewa tafiyar nan za ta iya d'aukar ka wata d'aya ko fiye da haka." Ajiyar zuciya ya sauke yace "Sati d'aya ma na fad'a mata amma ta damu sosai, ina ga na fad'a mata wata d'aya zanyi? Shi ya sa ma na riga na barwa Hajia komai su kula idan ta haihu, kuma na gode Allah da na iya fad'awa yan uwan ta adadin lokacin da zan iya yi." "Hakan ma da ka yi ya yi daidai, kaga za su dinga kwantar mata da hankali." A haka su ka isa kuma su ka rabu suma cike da kewar juna, a daren wannan ranar Khadija nak'uda ta taso mata, da su ka tafi asibi har sai da gari ya waye rana ta yi fatsal-fatsal kafin ta haihu, duk abin da ake Usman na da labari, lokacin da Husseina ta bawa Khadija waya ya mata magana da ta kasa, wata k'ara tare da kuka had'i da salati da ta yi sai da ya ji kamar ya bud'a ido ya ganshi gabanta, a k'arshe dai *bayan wuya* sai dad'i, ta haihu lafiya haka ma yaro, lokacin wani mugun bacci ne ke d'ibar Khadija amma sai Usman yace Hajia ta bata waya su yi magana, daga kwance ta karb'i wayar ta d'ora a kunne, shiru ta yi sai shine yace "Barka baiwar Allah, daga k'arshe dai Gashi kin haifo min yaro, Khadija ina cikin farin ciki sosai, godiya ko dukiya ba za su iya biyan ki ba, amma ina so ki fad'a min duk abin da ki ke so? Ni kuma zan baki shi a matsayin tukuicin wannan kyautar." Cikin muryar jin bacci tace "Ina hushi da kai kafin minti ashirin da su ka gabata, saboda ka k'i zama tare da ni a lokacin da na ke buk'atar ta, da ka k'ara kwana d'aya tak da na haihu a gaban idon ka, amma bayan minti ashirin da ya wuce, lokacin da na d'ora ido na akan yaron ka, sai na ji komai ya yaye a zuciya ta, dan haka ka d'auka yaron nan shine tukuicinka gare ni." Wata nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke yace "Ki yi hak'uri Khadija, haka Allah ya so, kuma duk da kin ce ba jya buk'atar komai, amma akwai wani abu da zan ba ki, kinsan me ye?" Cikin lumshe ido tace "A'a." "Khadija, nine ya cancanci na yi wa yaron nan hud'uba, kuma gashi bana nan, dan haka babu wanda yafi cancanta sai ke, na d'ora mi ki wannan nauyin a kan ki, idan kin ma sa hud'uba sai ki rad'a masa sunan da ki ka ga ya dace kuma ki ke so." "Da gaske ka yarda na saka mi shi suna da kai na?" Ta tambaya da fara'a. "Sosai ma, wannan hukuncin na jima da yanke shi ai, ba kawai dan bana nan bane." Shiru ta yi kamar mai bacci kafin tace " *Abban Bilal*., hakan ya yi?" Da farin cikin jin sunan da ta sakawa yaron ya sa yace "Masha Allah, Bilal, sunan da ke birge ni, sunan da ya nake da burin sakawa yaro na shi, hakan fa ya na nuna k'arfin soyayyar da ke tsakanin mu ne." Jin bcci na son surarta ya sa tace "Ka gafarce ni Abban Bilal, bacci na ke ji sosai a ido na, za mu yi magana anjima." "Ayyah sannu momyn Bilal, zan barki haka to, amma anjima za mu yi magana, kin yarda?" Cikin hamma tace "Na yi alk'awari." Da haka su ka yi sallama, kamar yanda ya bar komai hannun Hajia haka ta dage sosai ta yi takamata, dan mawasu lokutan maman Khadija da yan biyar ba sa tsayawa komai da an nemi abu za su siyo su kawo, haka dai aka yi shagalin biki babu uban yaro, a lokacin Khadija ta fara damuwa da rashin dawowar Usman, da k'yar yan uwanta da mama suke kwantar mata da hankali, tun suna waya ya na cewa zai zo aiki ne ya rik'e shi har ya kai ya rasa me zai ce mata, sai kawai zuciyar shi ta bashi ya daina kiranta, ita kuma idan ta kira jar ya d'aga sai an kwana biyu, wannan dubarar ce ta jefa Khadija a wani hali na daban, da ta kwashe kwanaki ta na kira bai d'aga ba, damuwar ta ta nunku sosai, mama kuma sai take cewa tayi hak'uri mana da yanda Allah ya hukunta mata, hakan ya sa Khadija tunanin ko Usman ya mutu ne dai, kawai sai ta yanki jiki ta fad'i, sai da ta kwana asibiti, a ranr Usman bai shirya tahowa ba amma dole ya taho, dan cewa ya yi neman kud'i ba zai ja mi shi rasa matar shi ba wacce ya ke da yak'inin ba zai samu kamar ta ba a wannn k'arnin, sai lokacin kad'ai Khadija ta samu sauk'i ta kuma huce. *Allah ka k'ara mana lafiya mai anfani.* 20/01/2020 Γ 12:38 - πππ: ππππππππππ *KALLON KITSE* _(Ake wa rogo)_ ππππππππππ _SAMIRA HAROUNA_ *Littatafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _D'AUKAR FANSA_ *3* _BA SO BANE_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI_ *6* _JIHADI_ *7* _K'ANGIN RAYUWA_ *8* _ITACE K'ADDARARMU_ *9* _KAWU NA NE_ *10* _MAATA_ *11* _KALLON KITSE..._ *SADAUKARWA GA* _MATAN FARKO_π§πΌ *(UWAYEN GIDA)* πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€ πππ *My Heenat, My BK, My Meelat*πππ _Alkhairin Allah ya lullub'e min ku, ina k'aunar ku._π ```Fatan alkairi masoya``` *MOMYN DADY, KI JI DAD'IN KI WANNAN PAGE TA KI CE KYAUTA.* π _Bismillahir rahamanir rahim_ *13* Kullum taresu ke idan dare ya yi har ba ya son rabuwa da iyalin shi, kuma bai sake wani tafiya ba har sai da ta yi arba'in, sabon gidan da ya gina mu su matsakaici daidai da rayuwar su suka tare, haka suke rainon Bilal cikin kulawa da so da k'auna, ta b'angare d'aya kuma ta na ci gaba da zuwa makarantar ta, kasancewar babu nisa da gidan su da makarantar ya sa take aje Bilal nan kafinta wuce, idan ta sauko ta biyo ta d'auko shi, a haka dai har ta kammala karatunta lafiya, haka ma Usman ya na k'ara samun hab'aka a kasuwancin shi, a lokacin da ya ke tunanin nemawa Khadija aikin karatun da ta yi, sai kawai ta shawarce shi kan ta na son fara kasuwanci, ta na so Ashir ya fara kawo mata kwanuka da karap (jug) da sauran kayan anfanin mata ta na siyarwa, ya ji dad'in haka kuma yace nauyi ne a kan shi ya mata hakan, Ashir ya nema su ka yi magana sannan ya fara bashi *million d'aya* dan a fara da ita, cikin ikon ubangiji kuma sai Allah ya sawa kasuwar albarka, duk da komai bashi ne, amma dai ana samu sosai, lokaci na tafiya kamar walk'iya in da abubuwa ke faruwa, ta na taimakon danginshi da danginta da ita kan ta ma da kasuwancinta, in da
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117