Skip to content

Chapter 19

Chapter 19

Kallon Kitse Book One Complete Hausa Novels 1,197 words 0 views Progress saved
Download Book

da yer uwar mu alkairi, dan gaskiya na yarda da tarbiyar shi da kuma dattakon iyayensu, sai dai Usman ba kamar sauran maza bane, zai iya nuna cewa kamar Khadija ba tsararsa bace irin tafi k'arfin shi, ni kuma a gani na Khadija ce za ta yi sa'ar samun miji kamar shi, sannan burin mu anan dukanmu bai wuce mu bawa Khadija mijin daya dace da ita ba, sannan mun wa mahaifin mu alk'awarin kula da ita har zuwa lokacin da za mu damk'a ragamar kula da ita a hannun mijin da ya dace, da wannan nake neman shawararku da idan kun amince, sai mu je har gidansu Usman sannan mu nema wa yer uwar mu auren nagartattacen mutum, ba fad'uwa mu ka yi, kuma ba abun kunya bane dan mu muka fara zuwa da maganar, hakan ba yana nufin mun arhantar da ita bane, sai dai ma k'ok'arin kare mutumcinta, ko ya ku ka gani?" Bashir ne yace "Tunda dai har ka yarda da shi ai ina ganin ba wani abu, kawai ayi d'in, burinmu shine ganin Khadija ta dawwama cikin farin ciki." Kallon mama Ashir ya yi yace "Mama ba ki ce komai ba?" Murmushi ta yi tace "Me zance ni, bayan iyayenta kuma yan uwanta sun gama magana, babu abin da zance sai dai addu'a da kuma fatan Allah sanya alkairi." "Ameen mama." Suka amsa a tare, Ashir ne yace "Yanzu tunda dukan mu mun amince, gobe zan je na samu kawu *Kabir* na fad'a ma sa, in ya so sai muje tare, amma ku sani dukanmu za mu tafi neman auren nan." Naseer ne yace "Kar ka damu ai, ni ne ma gaba saboda munfi kusa da ita." Habeeb ne yace "Kai dallah can malam, kowa a gidan nan ai yasan Khadija tafi shak'uwa dani." Wani wawan tsaki Ashir ya yi yace "Aikin banza, ai sai kuyi kuma, amma da yanzu za'a tambaye ta na tabbata ni ne farko." Bashir ne yace "Hum! Kun manta sunan da ta ke kira na da shi ne?" Dariya su ka yi sai Mansur ne yace "Dan ta kira ka da hannayenta sai me?" "Sai ya na nufin mahimmanci na a gareta." Ya fad'a har da juya baki, dariya Mama ta yi ta Mik'e tace "Sai da safenku." "Sai da safe mama." Su ka amsa. *Wannan* k'aramar magana ita ce ta girmama har aka fara shigar da maganar aure tsakaninsu, sai da komai ya daidaita ana shirin kawo akwatina kad'ai yan uwan su ka sanar da Khadija a tunaninsu sun mata (surprise) za ta yi murna, Khadija ta girgiza, amma jin dalilinsu na yin haka domin farin cikin ta ne kawai, a lokacin kukan da take bawai na farin ciki bane, amma saita share ta nuna musu na dad'i ne take, dukansu ta had'a ta rumgume tace "Na yi sa'ar samunku a matsayin yan uwa." A wajen Usman kuma har ya fara bore ya na nuna baya so, ya fad'a mu su kuskuren fahimta ne kawai, amma ko zaiyi aure yanzu ba yarinya kamar Khadija ya ke so ba, sai mahaifiyar shi ce ta zaunar da shi ta nusar da shi alfanu da alkairan da zasu iya tasowa sakamakon auren shi da Khadija, amma duk da haka sai da yace "Hajia, wallahi na tabbata ita ma yarinyar nan bata so na, zaifi kyau ku bar kowa ya zab'i wanda ya masa, amma kar ku ce za ku had'a mu saboda rashin fahimtar da Ashir ya yi." Sosai ta tank'wara shi har ya samu ya sauko ya amince, amma yace saboda sune kawai, ita kuma mahaifiyar ce tace "In dai kuma har saboda mu kayi, to ka sani ba kai ba nadama har abada, insha Allahu wannan auren zai zamar maka alkairi, ba za ka tab'a kuka da zab'in mu ba." Magana ta kankama sosai, amma ango da amarya babu wani mai shiri ko farin ciki, an saka wata *hud'u* mai zuwa, yan uwan amarya da mahaifiyar ta sun dage wajen shirin bikin autar su, gaisuwa kad'ai ke had'a Usman da Khadija a waya, su na gaisawa zata aje wayar ko shi ya aje, kuma kamar an k'yasta ashana sai gashi an cinye wannan lokacin da aka saka, ba dan Usman ya so ba ya baro harkokinshi ya zo sabgar bikin shi, fad'an irin tartsatsin da aka yi a bikin ma b'ata lokaci ne, dan yan uwa biyar sun yi bajinta sosai wajen k'ayatar da yer uwarsu, sai dai kamar yanda Usman ya ke ganin baiyi wani bajinta ba sosai, hakan ya sa yace ba ya buk'atar komai daga gare su shi ma sai amaryar kawai, hakan kuma ya birge mutane da dama, haka akayi wannan walima aka kai amarya d'akin mijinta, kuma duka yan uwa biyar d'in su suka saka k'anwar su tsaka suka iza k'eyar ta har ta shiga d'akin ta. Gidan malam Ali da shima ya gada a wajen na shi tsohon, matsakaicin fili ne sai d'aki ciki da falo, sai ban d'aki a farfajiyar gidan da kuma k'aramar runfar da aka yi ta tΓ΄le aka aje kayan abinci ya zama wajen girki, d'akin nan tamtsam aka mi shi da kaya na gani na fad'a, bayan yan kai amarya su tafiyar su aka bar ango da amarya, shima fita ya yi kafin dare ya k'ara yi ya dawo gidan. Zaune ya same ta akan gado fuskarta rufe, k'arasowa ya yi tare da "Amincin Allah ya tabbata a gare ki." Wayu ta had'e ta rintse ido gabanta na fad'uwa tace ".. *Allah ka mana kyakyawan k'arshe.* 14/01/2020 Γ  14:03 - πŸ’‹πŸ˜˜πŸ’‹: πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘ *KALLON KITSE* _(Ake wa rogo)_ πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘ _SAMIRA HAROUNA_ *Littatafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _D'AUKAR FANSA_ *3* _BA SO BANE_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI_ *6* _JIHADI_ *7* _K'ANGIN RAYUWA_ *8* _ITACE K'ADDARARMU_ *9* _KAWU NA NE_ *10* _MAATA_ *11* _KALLON KITSE..._ *SADAUKARWA GA* _MATAN FARKO_πŸ§•πŸΌ *(UWAYEN GIDA)* πŸ‡ΈπŸ‡¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_πŸ€œπŸ€› ```Fatan alkairi masoya``` _Bismillahir rahamanir rahim_ *11* "Kai ma haka." A hankali ya zauna bakin gadon ya aje ledojin hannun shi, kallonta ya yi ya d'anyi shiru, dama dai fuskarta a rufe take, dan haka ita ma ta yi shiru, kowa da abin da yake sak'awa a ran shi, kusan minti sha biyar su ka d'auka a haka kafin ya sake kallonta ya d'anyi gyaran murya yace "Ko za ki iya bud'e fuskar ki." Shiru ta yi kamar ba ta ji ba kuma bata bud'e ba, numfashi ya sauke cike da nuna kasala ya zuro hannayenshi ya yaye mayafin, fad'uwar gabanta ne ya nunku, shi kuma ya kafe fuskarta da babu ko d'igon kwalli da ido, sai dai lumshe ido ya yi saboda matsowar da ya yi kusanta k'amshin turaruka ne suka bigi hancin shi, ajiyar zuciya ya sauke yace "Ya kamata muje mu yi alwala ko?" Ba tare da tace komai ba ta fito da k'afafun ta daga tank'warewar da ta mu su ta sauka daga kan gadon, bin bayanta ya yi su ka samu buta su ka yi alwala su ka dawo, hijab ta saka ta shinfid'a sallaya ya shiga gaba ya kabbara sallah, raka'a biyu su ka yi su ka sallame, juyowa ya yi ya na fuskantarta ya zuro hannunshi zai dafa kanta dan yin

Table of Contents

Chapters

117 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117