Chapter 76
Chapter 76
jinjiri, matsala ce ta faru da tasa dole sai na bar gidan nan na wani lokaci, ku yi hak'uri, na bar ka lafiya." Ta na gama fad'a ta shiga adaidaitar suka wuce, da kallo ya bisu ya na fad'in "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un, ita kuma amaryar da abin da ta zo da shi kenan? Wannan wace irin jaraba ce, mata da mijin ta kullum cikin farin ciki, idan ka ji hayaniya to suna wasa ne kamar yanda su ka saba, amma yau gashi su na shirin rabuwa dalilin wata, kai Allah ya kyauta." Usman na ciki shi da Haseenah bai san tsiyar da ake ba, ba jimawa kam adaidaita ya sada Khadija da gidan su, Mama na ganin su da kaya ta fara salati da sallalami, kai tsaye d'aki ta nufa ta aje kayan ta ta wuce d'akin ta, tashi Mama ta yi tabi bayan ta sai matan yan uwan ta ne su ka bisu da ido, matar Habeeb ce kad'ai ta iya cewa "Aifa lokacin ya yi." Shiru sauran su ka yi dan suma kawunan nasu a rarrabe suke, kowa da b'angaren da yake saboda suma akwai uwayen gida akwai kuma amare. Babu abin da Khadija ta b'oyewa maman ta duka ta fad'a mata, duk da taji ba dad'i sosai amma sai bata nuna mata ba, kallon maman ta tayi tace "Dan Allah Mama taimaka min da maganin ciwon kai." Tashi kawai Mama ta yi ta d'auko ta kawo mata tasha ta kwanta, matar Mansur ta shigo d'akin dan su kwashi labari sai dai ta samu Khadija har ta fara baccin wahala da fuska har yanzu a sumtume, sam Mama ba ta fad'awa 'yan uwan ta ba ko a waya sai dare da suka dawo su ka tarar da wannan abin takaici, lokacin Khadija zazzab'i ya sake rufe ta, Naseer har da k'walla ya yi da ya kalle ta, yanda ya sunkuyar da kai ne ya sa Habeeb dafa shi, goge fuskar da ya yi ne ya tabbatar musu kuka yake, Bashir ne yace "Kai haba dai maza, kuka fa? Ai ba kai ya kamata ka yi kuka shi ya kamata ya zubar da hawaye." Wasu hawayen ne suka sake taho mi shi yace "Yanzu domin Allah me ya sa Usman ya yi haka? Mufa mun bashi ita ne da tunanin zai kula da ita, me ya sa zai mana haka yanzu? Saboda kawai ana ganin ita marainiya ce mahaifin ta ya rasu." Sun jima d'akin ta suna tattaunawa in da take kwance ta dunk'ule, saida dare ya yi suka tashi suka koma nasu dak'unan, saida tasha magani kafin ta sake kwantawa, sai dai ba ta yi bacci ba har aka kira sallah asuba, sallah ta yi ta sake komawa ta kwanta ta na istigfari tasbihi da hailala da hannun ta na dama. Ko da Usman ya fahimci basa gidan haka kawai yaji bai wani damu ba, hakan ya sa ma da safe ko da ya je gida ya samu su Hajia da maganar ya kuma fad'a mu su kar suce za su je su dawo da ita, harda had'a su da Allah akan su barta harta shiga hankalin ta, Bilal kuma d'an shi ne ba ta isa ta raba shi da shi ba, amma malam yace sam ba da shi za ayi haka ba, a k'arshe ma tambayar su dalilin faruwar haka akayi, fad'an Hajia shine "Makulli Usman ya bawa Haseenah ta aje na mota da zai tafi, ita kuma ta tashi fita tace ta bata, shi kuma yace kar aba kowa idan za'a fita a fad'a mi shi zai aiko da wani ya kaisu duk in da za su je, shine ta turmushe yarinya da k'aramin ciki ta karb'i makullin, dalilin hka fa ya kusa sawa ta yi b'ari." Duk da jin haka yace zaije ya dawo da ita gidan ta, kuma kamar yanda ya fad'a ya cika maganar shi, amma maganganu mabanbanta ya ci karo da su, musamman da suka fad'a mi shi har da duka, har d'akin Khadija aka mi shi jagora ya ganta kwance da k'arin ruwa a hannu, dan tunda ta yi sallah asuba zazzab'i ya sake rufe ta, hakan ya sa Naseer ya d'auko likita har gida aka dubata, sosai suka nuna mi shi b'acin rai da cewa ba za ta koma ba har sai Usman ya dawo hankalin shi, baiga laifin su ba kam dan ya sa dole wata rana zai neme ta, haka malam ya juya rai b'ace da kuma kunyar abin da ya aikata, tun a hanya yace Usman ya same shi gida za su yi magana, da "To Baba." Ya amsa. *Ku na ganin zaije? Yanzu fa Haseenah ita kad'ai ce.* Saida ya sake wanka ya shirya yace "Amarya ta zanje gida na dawo, amma ba zan jima ba kinji, ki kula da kan ki." Kallon shi ta yi ta na k'ara rufe jikin ta da zanin gado tace "Gida kuma? Na d'auka d'azu ka ce min gida ka tafi, ya da wuri haka za ka koma." Ya na gyara zaman hular sa yace "Eh wallahi Baba ne wai ya ke son gani na, amma na san ba zan jima ba ai zan dawo." Shiru ta yi a zuciyar ta tace "To idan fa yanzu ma dawo da Khadija za su tafi? Dole na yi wani abu." Shagwab'e fuska ta yi tace "Yanzu tafiya za ka yi ka barni a haka? Ba ka da matsala kenan tunda ka samu biyan buk'atar ka ko?" K'ok'arin saukowa ta fara daga kan gadon ta na fad'in "Shikenan ai ka tafi." Matsowa ya yi kusan ta zai kamo hannun ta ta kubce ta shige ban d'aki, bakin k'ofar ya tsaya yace "Haba ke kuwa, kar ki yi hushi mana, kinfa san ba na son b'acin ran ki ko kad'an." "Ahhhhhhh, wayyo Allah ciki na, marata." Fad'in Haseenah daga cikin ban d'aki, bai tsaya tunanin komai ba ya kutsa ciki ya same ta zaune dafe da ciki alamar fad'uwa ta yi, bai tsaya komai ba ya d'auko ta sai kan gado ya dire ta, kallon ta yake ciki da damuwa ya na rik'e da hannayen ta yace "Garin yaya ki ka fad'i haka? Haseenah karfa ki mana asarar kyautar nan da Allah ya bamu, kinfi kowa sanin lokacin da na d'auka ina fatan Allah ya sake bamu haihuwa, ina son na ga gidan nan ya cika da yara kuma ya zamana ke ce uwar su." Yanda ya k'arashe maganar kamar zaiyi kuka ne yasa tace "Ka yi hak'uri dan Allah, ni ma santsi ne kawai ya kwashe ni, ban kula ba sai ji na yi na fad'i saboda rai na a b'ace yake." Kallon ta ya yi yace "To me ya b'ata mi ki rai haka da har ki ke neman ja mana babbar asara." Cikin turo baki tace "To ba kai ne ka ce zaka fita ka bar ni ba, ni kuma wallahi ba na so ka tafi, satin ka biyu fa baka gari, kasan dai dole munyi kewar ka mu na buk'atar ka a kusa da mu, shine kawai daga ka samu yanda ka ke so sai ka ce za ka fita." Da rawar jiki yace "Ai dai fitar ce ba kya so ko? To na fasa, kin gani ma?
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117