Chapter 110
Chapter 110
Bilal shekara nawa mu ka d'auka muna neman haihuwa, amma zuwan Haseenah gidan nan sai gashi Allah ya azurtani da nawa cikin nima, watak'ila hakan ya faru ne saboda hak'urin da mu ka yi da kuma tsarkake zuciya ta da na yi wajen zama da ita, ba ka tunanin yanzu idan na sa ka dawo da ita Allah ya sake mana wata rahamar ta hanyar da ba mu yi tsammani ba?" Ganin ya yi shiru alamun maganganunta na ratsa shi ya sa tace "Za ka iya tuna a cikin karatun da ka ke koya mana kai ka bamu labarin abin da ya faru tsakanin *sayyidi na Abbakar* da *musd'ahu* mai hidima gare su kuma wanda su ke d'aukar nauyin shi, Musd'ahu na d'aya daga cikin wanda suke yayata k'azafin da akawa *Nana Aisha (RA)* cewa ta yi zina, a lokacin da ran sayyidi na Abbakar ya b'aci ya kori Musd'ahu daga gidan shi tare da cewa ba zai sake d'aukar nauyin shi ba, me Allah yace akan haka, Allah ya na son masu yafiya, idan ka yafe kuma sai ka manta da komai, sannan ka k'ara da kyautatawa, to hakanne ya kamata ya faru a yanzu, ka yafe mata gaba d'aya, sannan ka manta da abin da ya faru ka daina tunawa, kyautatawar da za ka mata kuma bai wuce ka dawo da ita d'akin ka ba ta haifi abin da ke cikin ta ba ta kuma raine shi gaban ka, kar kaga ka na keyawa da masoyan ka za su kula maka da d'an da za ta haifa, rik'on yaro sai uwar shi, duk wanda kaga bai rayu da mahaifiyar shi ba dan hakan na mi shi dad'i bane, dan Allah miji na, Usman na Nana, ka saurari matarka mana ka tuna had'uwar ku ta farko da ita da kuma yanda zaman ku ya kasance, saika yanke hukunci." Shafa kumatun shi ta yi ta d'aga shi zata koma d'aki dan ta bashi damar yin tunani, sumbatar kumatunshi ta yi ta rad'a mi shi a kunne cewa "Kar ka manta Khadija na matuk'ar son ka sosai, kai ne rayuwa ta babban mutum." Da murmushi kawai ya bita da kallo harta shige d'aki, ya jima nan zaune ya na tunanin abin da ta fad'a mi shi, har ga Allah babu ko k'aunar Haseenah a zuciyar shi bare soyayyarta, amma zai dawo da uta saboda farin cikin Khadija kawai, amma kuma ba yanzu sai ta shiga watan haihuwar ta kad'ai zai dawo da ita, kamar yanda ta sa Khadija zama a gidan su ita ma saita d'and'ana zaman gidan sosai ya ratsata kafin, tashi ya yi ya shiga d'aki saida su ka yi shirin kwanciya kafin ya fad'awa Khadija ya ji zai dawo da ita amma da sharad'i, da sauri tace "Sharad'in me?" "Zan dawo da ita amma ba yanzu ba, idan hakan ya mi ki to, in kuma bai mi ki ba to abar maganar, sannan zan dawo da ita ne ba dan ina buk'atar zamanta a gida na ba sai dan kin matsa." Kallonta ya yi yace "Kin yarda?" Da sauri tace "Na yarda Abban Bilal, duk da haka na san ba zaka tauye hakk'in ta ba." Daga ranar ya samu zaman lafiya Khadija ta daina mi shi magana, haka aka kwashe wasu watannin a lokacin cikin Haseenah ya shiga watan haihuwa, taje asibiti aka bata sati biyu idan bata haihu ba ta koma, a lokacin Khadija da Hajia da Usman da malam suka je gidan su Haseenah biko, abun ya bawa Haseenah kunya sosai ta yanda ta dinga kuka ta na neman gafarar Usman da Khadija, nan iyayen ta ma suka basu hak'uri kafin aka k'ara mata fad'a da nasiha, Khadija da kanta ta tayata had'a kaya dan da tace ma su bari har gobe Khadija tace a'a, tsaf suka had'a kayan suka fito tare da ciki kowace ta na turawa, kayan Usman ya karb'a ya kai mota kafin suka tafi, gida ma saida malam ya sake mu su jan kunne tare da tunatarwa akan zaman aure ibada ne kafin Usman ya mayar da su gida, suna fita Haseenah ta sake fashewa da kuka ta rik'e k'afar Khadija tace "Aunty Khadija ki yi hak'uri ki yafe min dan Allah, wallahi na yi nadamar abin da na aikata." Kamata Khadija ta yi tace "Haseenah na fad'a mi ki ba komai wallahi, na hak'ura har abada kuma, Allah dai ya k'ara had'a kan mu." Bilal ne ya fito daga d'aki da riga a hannu ya mik'owa Khadija yace "Mummy taimaka saka min rigar nan, wuyanta matse ni yake." Da sauri Haseenah ta tara mi shi hannu tace "Kawo na saka ma ka yarima." Bata ya yi ya na kallon mummyn shi a d'ard'ar ya matsa kusa da ita, saida ta saka mi shi ta kalle shi tace "Yarima ka yi hak'uri ka yafewa auntynka kaji, na yi nadamar abin da na yi." Kallon mummyn shi ya sake yi ta sakar mi shi murmushi hakan ya sa ya rumgume Haseenah yace "Aunty amarya, uwa fa ba ta neman yafiyar 'ya'yan ta." Kallon shi ta yi tace "To in dai uwa ce ni ai ba aunty ya kamata ka kira ni ba." Murmushi ya yi sosai ya kalle ta da kunya yace "Mummy." Har zuciya Haseenah taji muryar Bilal ya kira ta da sunan uwa, rumgume shi ta yi take taji wata soyayyar shi ta d'arsu a zuciyar ta, sun jima nan har Usman ya shigo kafin kowa ya nufi na shi d'akin, wani irin sanyi Haseenah taji sai take ji ashe zaman lafiya da wanda Allah ya had'a ka zama da shi dad'i ne da shi, sai taji kamar yau ne aka fara kawota gidan tare da k'udurawa a ranta zata wa Khadija biyayya ko da kuwa za ta zama baiwarta ne hakan ba zai dame ta ba, har ta yi shirin kwanciya Usman ya shigo da doguwar riga yace ta same shi falon Khadija, da to ta amsa mi shi ya fice ko kallon ta baiyi ba, haka ta fito jiki a sanyaye dan tasan yanzu ba mutumcin ta Usman zai gani ba, kuma kamar yanda ya fad'a a gidansu cewa ya fa zo ne saboda Khadija ce ta matsa, to tabbas tasan dawowar nan da ta yi zaman Khadija ne za ta yi, sun samu Khadija zaune da alama su take jira, zaune ya yi kusan Khadija Haseenah kuma cike da kunya ta zauna k'asa, Khadija ce tace ta zauna sama amma tace a'a tafi jin dad'in nan, Usman ne ya gyara murya ya fara magana kamar haka. "... 15/03/2020 Γ 23:06 - πππ: ππππππππππ *KALLON KITSE* _(Ake wa rogo)_ ππππππππππ _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _D'AUKAR FANSA_ *3* _BA SO BANE_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI_ *6* _JIHADI_ *7* _K'ANGIN RAYUWA_ *8* _ITACE K'ADDARARMU_ *9* _KAWU NA NE_ *10* _MAATA_ *11* _KALLON KITSE..._ *SADAUKARWA GA* _MATAN FARKO_ π§πΌ *(UWAYEN GIDA)* πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€ πππππππ ```Fatan alkairi masoya``` *ALHAMDULILLAH ALA NI'IMATUL ISLAM* _Bismillahir rahamanir rahim_ *40* "Haseenah, Allah ya nufa dai akwai sauran zama tsakani na dake, ina fatan abubuwan da suka faru a baya sun koya mi ki wa'azi, Haseenah zan fad'a mi ki wata magana wacce a
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117