Skip to content

Chapter 57

Chapter 57

Kallon Kitse Book One Complete Hausa Novels 1,198 words 0 views Progress saved
Download Book

ta kud'i a fara mata magani, Khadija na kallo suka dawo suka nufi b'angaren ta, ya jima ya na bata magana da rarrashi kafin ya fita, a gida ma suna tafiya mahaifin ta ya fito ya hau moton shi, bai zame ko ina ba sai *pharmacie salfiya* cibiyar magunguna na addini, da ya fad'a mu su matsalar sun zo ya zo da mara lafiyar da suga yanayin jikin ta, amma tunda ya riga ya zo sai suka bashi wanda ya dace da abin da ya fad'a, amma sunce in har ba ta daina ba to su kawo ta wajen su dan su duba ta, ya na barin nan gidan Haseenah ya wuce kai tsaye, dan suna so su d'auki matakin tunda wuri, Khadija na ganin shigowar shi amma ba ta kawo komai a ran ta ba dan bata nufin kowa da sharri, har falon Haseenah ya ke zaune ya na fad'a mata yanda za ta yi anfani da su, saida ya gama kafin ya bar gidan, Haseenah na ganin fitar shi ta kai magungunan d'aki ta aje, d'ibar wasu ta yi daga cikin wanda za ta yi anfani da su yanzun ta zubar. Usman kuma na barin nan gidan su ya nufa, Hajia ya fad'a ma halin da ake ciki, ta jinjina al'amarin tare da dogon nazari akai, sai dai zuciyar ta ta kasa yarda cewa Khadija za ta iya cutar da ita, dan da za ta hana ta zaman gidan ai da bata ma barta ta shigo ba, amma dai "Allahu a'alam." Cewar Hajiar, ya na fita Aziza ta taso maganar dan ta na waje ta ke jin wasu maganganun, cike da damuwa Hajia ta fad'a mata yanda aka yi, ke Aziza ki na fitowa sai ki ka kira Hassana ki ka fad'a mata, kafin ka ce kwabo maganar ta karad'e yan uwan mata ana ta caccakar Khadija da maganganun b'atanci. Yamma na yi Haseenah ta shiga madafa ta d'ora girki, sai bayan magriba ta k'arasa ta yi wanka ta shirya, ko da ya shigo ya yi wanka ya sake kaya ya zauna wajen cin abinci, kallon shi ta yi tace "Bara na kira su aunty Khadija su zo mu ci abinci." Da ido kawai ya bita har ta fita, jim kad'an su ka shigo tare da Bilal, Khadija ba wai ta shigo bane saboda ta na son cin abinci sai dan gudun matsala, akan cinyar sh ya zaunar da Bilal in da Haseenah ta fara zuba abincin, a faranti d'aya suka fara ci shi da Bilal, amma Bilal na kai lomar farko ya kalli Haseenah ba ko k'yabtawa, da k'yar ya samu ya aika lomar ta gangara cikin shi, Khadija da Usman ma na kai wa suka yi saurin furzo shi waje suna goge baki, haka ita ma Haseenah ta na sawa ta firzo ta na ta faman goge baki, Usman ne ya kalle ta yace "Haseenah me ye haka? Kin d'and'ana girkin nan kuwa kinji?" A marairaice ta kalle shi tace "... *Yasin na gaji.* 11/02/2020 Γ  18:31 - πŸ’‹πŸ˜˜πŸ’‹: πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘ *KALLON KITSE* _(Ake wa rogo)_ πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘ _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _D'AUKAR FANSA_ *3* _BA SO BANE_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI_ *6* _JIHADI_ *7* _K'ANGIN RAYUWA_ *8* _ITACE K'ADDARARMU_ *9* _KAWU NA NE_ *10* _MAATA_ *11* _KALLON KITSE..._ *SADAUKARWA GA* _MATAN FARKO_ πŸ§•πŸΌ *(UWAYEN GIDA)* πŸ‡ΈπŸ‡¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_πŸ€œπŸ€› _*H. UMAR*, mahaifin da ya fi na kowa, ina alfahari da kai Baba na, wannan sadaukarwa ce gare ka kai kad'ai, ka cancanci fiye da ita ma, ka huta ka ju dad'in ka, Allah ya k'ara girma da lafiya dattijon arzik'i, *kut.kut.kut.*πŸ˜‰ kaza._ ```Fatan alkairi masoya``` _Bismillahir rahamanir rahim_ *22* "Wallahi bansan ya akayi gishirin nan ya yi yawa haka ba, ni fa lafiya k'alau na kammala girki na, kuma babu yanda za ayi na yi girki ban d'and'ana na ji yanda ya ke ba, sannan idan ka duba ai haka ba ta tab'a faruwa ba." Satar kallon Khadija ya yi wacce ta kafe Haseenah da ido ta na murmushi dan ita ta fahimci me take nufi da abin da ta fad'a, girgiza kai ya yi yace "Shikenan kar ki damu, komai ya wuce." Mik'ewa ta yi duk ta yi kalar tausayi tace "Ku yi hak'uri dan Allah, bara na samo mu ku ko soyayyen k'wai ne ku ci." Da sauri ya katse ta da "A'a ki barshi kawai, tunda hakane ake so mu zauna, ki kawo mana madara gari da sugar kawai sai mu had'a da farar shinkafar." Haka kam akayi taje ta kawo ta zuba a kofofi ta had'a ma kowa, ta mik'owa Khadija ta mik'e tsaye tace "Gaskiya ba na cin wannan had'in da dare, zanje na samu wani abu na ci da zai d'auke ni a wannan daren." Kai tsaye madafa ta nufa, ba ta ji wahalar d'aukar silallan naman dake cikin masuburbud'ar sanyi ba ta had'a sassauk'an miya mai kyau da dad'i, fitowa ta yi lokacin sai Bilal da Baban shi akan salon suna kallo ta zo gaban tebur d'in ta d'ibo sabuwar shinkafar ta zuba a faranti ta zuba miyar, Bilal ne ya juyo ya kalle ta yace "Mummy ni dai na k'oshi." "Dama bance ka zo ka ci ba." Ta fad'a ta na kai lomar farko, hankali kwance ta kammala ta tashi tace wa su je su kwanta, kallon Usman ta yi tace "Saida safe." "Saida safe." Ya amsa ya na shafa bayan Bilal, da ido ya bisu har suka b'acewa ganin shi, ya na ganin fitar su ya taso in da ta ci abinci, ya na bud'a k'aramin kwanon miyar ya lumshe ido, cokali ya sa ya d'auko tsokar nama ya jefa bakin shi, saida ya sake lumshe ido ya na taunawa ya na fad'in "Umm, umm." Da sauri ya d'ebo shinkafar kad'an a wani faranti ya zuba miyar ya dinga turawa saboda gudun kar Haseenah ta riske shi, har ya gama bata fito ba dan haka ya same ta d'akin ta na ta shirin bacci, nan ya fara lulawa da ita wata duniyar, sunyi nisa sosai ya na neman gangara kawai ta raba kanta da shi ta sauko daga kan gadon, ya na kallon ta kamar wasa ta canza kayan jikin ta ta saka hijab, ba tare da ya taso ba yace "Lafiya dai? sallah za ki yi ne?" Ko kallon shi ba ta yi ba ta nufi k'ofar fita, zaune ya tashi yace "Wai lafiya? Ina za ki je haka?" "Gidan mu." Ta fad'a ta na fita daga d'akin, da sauri ya sauko shi ma ya zura doguwar riga ya fito, ko da ya fito har ta kai farfajiyar gidan, rik'o ta ya yi yace "Haba Haseenah, ina za ki je da daran nan haka?" Kallon shi ta yi kamar za ta yi kuka tace "Ka yi hak'uri dan Allah ka barni na tafi gidan mu, wallahi ba zan iya kai safe gidan nan ba, ni kad'ai na san me na ke ji." A tak'aice dai haka Usman ya yi juyin duniya Haseenah tace ba za ta kwana gidan nan ba, shi kuma a ganin shi abun kunya ne ya kai ta gidan su, a cikin daren nan ya kai ta gidan su wajen Hajia, sam

Table of Contents

Chapters

117 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117