Skip to content

Chapter 67

Chapter 67

Kallon Kitse Book One Complete Hausa Novels 1,200 words 0 views Progress saved
Download Book

idan za ku yi anfani da su sai ki mata magana, saina dawo." Ya na fad'in haka ya juya rumgume da Haseenah a jikin shi, suna fita saida ya gama shinshine ta da lalabe lalabe kafin ya fito da enveloppe ta kud'i har jaka d'ari biyu ya bata, zo kaga murna ga yar matsiyata an bawa Khadija jaka talatin an bata d'ari biyu, 😂 da k'yar ya fita Murtala ya d'auke shi ya tafi cike da kewar amaryarshi. Sai da rana Aziza ta zo gidan da kayan ta, lokacin Khadija na zaune ta na waya da wata yer uwar ta (cousine) ta na mata k'orafin ta daina zuwa wajen ta, *Aishatu* ce tace "Aunty Khadija na zo Allah ko, ba dai ni nace mi ki na zo ba." "Hum, yaushe to?" Daga d'aya b'angaren ne Aishatu tace "Idan na sa lokaci na sanar da ke." "To ina jiran ki." Ta fad'a su ka yi sallama tace ta gaishe da su aunty (k'anwar maman ta). Ta ga shigar Aziza b'angaren Haseenah amma ko a jikin ta, ta na jin su suna aiki a madafa amma bata kula da tsiyar su ba, har lokacin d'auko Bilal ya yi daga islamiyya, Ashir ta kira a waya bayan sun gaisa ne tace "Yah Ashir wata alfarma a gurin ka dan Allah?" Saida ya yi murmushi yace "Auta ai babu alfarma tsakanin mu, fad'i me ki ke so yanzun nan a mi ki shi?" Cikin sanyin murya tace "Al'amarin Abban Bilal ya na buk'atar addu'a, na sani mijina ba ya hayyacin shi, yanzu haka ya yi tafiya, amma ni saida safen nan na sani, kuma ya tattara makullan mitar shi da tawa ya bawa yarinyar nan, yace sai dai idan ina buk'ata na karb'aa wurin ta, a gaskiya yah Ashir hakan zubar min da mutumci ne, na tabbata sai mun samu matsala da ita akan haka, yanzu haka Bilal na ismaliyya ba'a d'auko shi ba, shine na ke so ka samar min wanda zai dinga kai shi ya na d'auko shi har lokacin da zai dawo, tunda ka ga ma nan da kwana kad'an za'a koma makaranta (school)." Duk da ya ji ba dad'i amma cewa ya yi "Kinga kar ki damu da wannan, barta da makullan ta had'iye su in za ta iya, yanzu zanje na d'auko Bilal d'in na kawo shi gida, ba buk'atar sai an d'aukar mi shi dreba, ba wai dan ba za'a iya biyan kud'in ba, sai dan darajar Bilal ta wuce haka a wajen mu, kamar yanda na ke kai yara na da kai na haka zan dinga biyowa ina d'aukar shi shima, ko da babu mazauninshi a motar shi to za'a siyi sabuwar mota ne saboda shi kawai, motar tsiyar me da har za'a mi ki iko da ita." Ya na fad'a ya kashe wayar bin wayar ta yi da kallo tasan ranshi a b'ace ya ke, amma ta ji dad'i kuma da Allah ya bata yan uwa masu huce takaici, baifi minti sha biyar ba saiga Bilal ya shigo gidan da k'atuwar leda da kayan mak'ukashe a ciki, Haseenah da kallo ta bi shi har ya shiga tana mamakin waya kawo shi, ya na shiga ya aje ledar gaban Khadija ya shiga dan sauya kaya, ba jimawa ya dawo da wayar shi a hannu ya shiga latse latse ya na korawa da kayan mak'ulashen shi, sai daf da la'asar Aziza ta shigo wajen Khadija kawo mu su abinci, ko kallon Allah ya isa ba ta ishi Khadija ba har ta aje ta fita, ta na fita Khadija ta d'auki wayar ta kira *Hafsatu* Mak'wabciyar ta tace ta aiko yara ya amshi abinci, ba jimawa yarta ta zo Khadija ta juye mata shi a kwano d'aya ta tafi da shi, dan ita dai ba za ta ci abincin Haseenah ba in dai har za ta fitar mata da na ta da d'an ta a had'e, sai dai kome zai faru ya faru. *Tun daga wannan rana* Ashir ne ke zuwa ya d'auki Bilal da kan shi tare da yaran shi da na yan uwan shi, dama shi ya d'orawa kan shi alhakin kai yaran, sai dai ba kullum yake zuwa d'aukar su ba sai dai ya sa a d'auko su, amma yanzu da ya zamana akwai Bilal a cikin tawagar da kan shi ya ke d'auko su, hakan ya sa har yanzu bakin Khadija da na Haseenah bai had'u ba da sunan magana, ta yi shiru ta rik'e makullai ta na jiran ace kawo ta yi rashin kunya, Khadija kuma ta nuna mata ita ba bak'uwar mota ba ce, ana cikin haka hutun k'arshe ya k'are na makaranta, yara da manya aka fara hada hadar komawa, Ashir ne ya wa Bilal komai kama daga sababin kaya da abin da zai buk'ata a sabon ajin shi, har zuwa kud'in makarantar shi ya biya ba tare da sanin ma Khadija ba, saida aka kawo kayan kad'ai ta ji kuma ta gani, Usman kuma dama ba kiran ta ya ke ba, idan ma ta kira shi zai ce ta kashe zai sake kiran ta yana cikin mutane ko wani abu, sai in ya kira Bilal ne kad'ai yace ina maman ka yace gata nan, to lokacin zai ce bata waya kuma har su jima suna magana ya na tambayar ta abubuwa. Zaman Aziza da Haseenah ma ba laifi, a fuska faran-faran take mata, amma da ta bada baya za ta bita da harara dan duk ta gundureta, sai dai kuma har yanzu ba ta bar yiwa Khadija bita da k'ulli ba, duk ranar girkin Khadija idan ta aiko mu su da shi bata nunawa, dan dama Aziza sai ta tafi islamiyyar su ta dawo wacce Haseenah ce ke bata kud'in adaidaita dan ta yi nisa daga nan, kullum sai kusan k'arfe d'aya take dawowa, Khadija kuma na gama abinci da wuri tun kafin Bilal ma ya dawo, hakan ya sa da an kawo mata zata zauna ta ci ta k'oshi tasha ruwa, sauran kuma komai yawanshi da kyawunshi sai dai ta shek'a mi shi ruwa ta zuba wajen wanke wanke, da Aziza ta dawo za ta nuna ba'a basu abinci ba, haka za ta aikata ta siyo mu su awara ko soyayyan dankalin hausa, wata rana kuma su dafa indomie ko suyi taiba, kullum a takarce suke hakan ya sa Aziza da taje gida ta fad'awa Hajia, a wannan karan kam Hajia ta yarda tunda Aziza ce ta rantse ta fad'a mata, da farko ta so ta kira Usman ta fad'a ma sa dan ya mata magana, amma sai tayi tunanin ja mata matsala, dan haka saita shirya taje gidan da kan ta da nufin yi mata magana cikin ruwan sanyi, amma abun mamaki a gabanta ta zubawa su Haseenah na su abinci kwanon miya da na tuwo ta bawa Bilal ya kai, ita ma saida aka zubo mata ta ci ba wani sosai ba kafin ta mata sallama za ta tafi, saida ta shiga da nufin yi wa Haseenah sallama ta samu Aziza sun ware sai shigar tuwo suke kamar 'ya'yan yunwa, nan fa Aziza ta shiga cewa wallahi dan ta ga Hajia e ta zo ta zubo mu su, kuma d'ari bisa d'ari Hajia ta yarda, haka ta tafi

Table of Contents

Chapters

117 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117