Chapter 3
Chapter 3
bada goyon bayan ta d'ari bisa d'ari, yanzu amincewar ku na ke buk'ata." Cike da kamala tsohuwar tace "Ba ka da matsala da amincewar mu *Fodio* (sunan mahaifin ta ne, dan haka ta ke ma sa inkiya da Fodio), tun da dai har ka shirya, kuma ka na ganin ba wata matsala, sannan matar ka ma ta amince ba tare da tashin hankali ba, ai ka ga Alhamdulillah, sai dai kawai mu bika da addu'a da kuma fatan alkairi." "Nagode sosai Mama, Allah ya k'ara lafiya da girma, yanzu kenan idan Abba ya shigo za ku iya magana da su, duk yanda ku ka yi zuwa dare idan na dawo na ji insha Allah." Kasantuwar shi d'an fari ya sa ko ido ba ta son had'awa da shi kamar ta na jin kunyar shi, ba tare da ta kalle shi ba tace "Shikenan ba damuwa, insha Allah zan fad'a ma sa." D'an gyara zama ya yi alamar zai tashi yace "Mama babu wata matsala ko wani abun da ku ke buk'ata?" "Ah, Fodio kai ne za ka bar gidan nan da wata matsala? Ai sai dai in ba ka raye, Alhamdulillah wallahi babu komai, Allah dai ya yi albarka, Allah ya sa ka gama da duniya lafiya." Sai da ya durk'usa k'asa ya amsa da "Ameen Ameen Mama, nagode sosai da addu'ar ki gare ni, ni zan wuce sai anjima idan na dawo." "To Allah ya yarda, Allah ya tsare, ka gaishe min da waccen mutumin." Dariya ya yi yace "Watak'ila fa gobe ku gan shi gidan nan, dan mahaifiyar shi ta tafi d'auko shi." Cikin wasa irin ta kaka da jika tace "Ka ce mi shi ma kar ya kuskura ya zo in har ya san ba zai taho da k'atuwar bak'ar leda ba." "Zai zo da ita Mama, ai kin san shi da k'ok'arin cefanai." "Ko dai k'ok'arin jefawa a ciki ba." Da wannan wasan ya bar gidan zuciyar shi sakayau da ita kamar kullum, dan har abada babu abin da ke dagula mi shi lissafi, b'angaren mace, Allah ya wadata shi da mata kamar Khadija, babu abin da ya nema a gurin ta ya rasa, haka ma iyaye, Allah ya bashi iyayen da su ke son abin da ya ke so, sannan su ke nusar da shi tare da kora shi da addu'a a kullum, hakan na sa shi farin ciki , kuma shima ya na k'ok'ari sosai wajen sauke hakk'ok'in duka b'angarorin, haka ne m'a sanadiyar da ta sa kullum ci gaba ya ke gani babu komawa baya ko rashin nasara, dan Allah ba ya kunyatar ko tab'ar da wanda ya kiyaye hakk'ok'in wannan mutanen a duniya. Khadija ma a gidan su farin ciki ta ke kamar ba ta farin ciki a gidan ta, hakan kuma ya samo asali ne sakamakon samun kan ta da ta yi a tsakiyar mahaifiyar ta da kuma d'an ta, sai sauran matan yayyun ta da kuma 'ya'yan su, bayan sun ci abincin rana yan uwan ta maza su uku su ka shigo gidan, anan ta tara su kuma ta fad'a mu su auren da mijin ta zaiyi, ta gaggauta fad'a mu su hakane saboda ta san sune za su iya bata shawara mai kyau wacce ta dace, kuma kamar yanda ta yi tsammani hakane ya faru, sosai su ka kwantar mata da hankali tare ja mata kunne da nasihohi ma su shiga rai, tare da kafa mata misali da matar babban yayan ta wanda da zai k'ara aure ta tashi hankalin kowa, a k'arshe dai sai da ta bar gidan, yanzu gashi nan sai amaryar ke rayuwar ta a b'angaren na su, abin da ba ta son ganin shi ke faruwa a bayan idon ta kuma ba yanda za ta yi, ga yayan ta ma su na hannun uban su sai yaga dama ya ke barin su su je wajen uwar, saboda hure mu su kunne da ta ke, hakan ya k'ara saka jikin Khadija yin sanyi, kuma ta yi niyyar yin aiki da shawarwarin da su ka bata, a haka ita ma ta yi yammacin ta tare da maman ta abar k'aunar ta, zuwa *5:30* na yamma kuma Bilal ya d'auki kayan shi su ka wuce tare da maman shi a motar ta. Su na isa gida Bilal ya wuce da yan kayan shi d'akin shi tare da canza na jikin shi, ita ma kaya ta sauya ta wuce madafa dan sarrafa abin da za su ci da dare, tare da Bilal su ka shiga ya na kama mata duk aikin da ta ke yi, sai da aka gama sallah magrib ta gama lokacin Bilal ya wuce masallacin da ke had'e da gidan su, ta na gama ajewa a mazaunin cin abinci ta yi wanka ta shirya cikin riga da zane wanda su ka d'auke jikin ta sosai, kasancewar babu wata tazara mai tsayi tsakanin sallah magrib da isha'i ya sa ta yi sallahn ta, ta na kammalawa ta fito falon ya yi daidai da shigowar Bilal daga masallaci tare da baban shi. Ta na ganin shi ta tashi tsaye ta turo baki tace "Sai yanzu za ka dawo min gida? Ina ka shige haka?" Kallon Bilal ya yi yace "Yau salon gaisuwar maman ka kenan? To ka fad'a mata ba zan amsa ba." Ita ma Bilal ta kalla tace "To ka fad'awa Abban ka ya juya ya koma in da ya fito, dan ba ya da muhalli a gidan nan yau." Dariya ya yi ya kalli Bilal yace "Ka tambayar min ita kaji, wai dama ana korar mutum da gidan sa?" Da shu'umin murmushi a fuskar ta tace "Ka fad'a ma sa sau nawa aka yi, idan kuma bai tab'a gani ba to yau zai faru a kan shi." Bilal da ya saki baki ya na kallon su dukan su ne ya matso kusan maman shi ya rik'e hannun ta yace "Momy dan Allah ni dai muje ki zuba min abinci na ci yunwa na ke ji." Dafa kanshi ta yi tace "Muje ka ji yaro na, kai da gidan ku." Sun juya za su wuce ta ji ya rik'o hannun ta, juyowa ta yi su ka kalli juna, murmushi ta masa tace "Ina so na rumgume ka, zuciya ta bugawa ta ke da k'arfi." Jan hannun ta ya yi su ka nufi d'akin shi, Bilal na ganin haka ya k'arasa shi kad'ai ya zuba abincin ya fara ci, dan ba zai iya jiran su ba, su na shiga d'aki su ka k'wak'wume juna kamar sun shekara ba su had'u ba, sumbatar ta ya ke tare da fad'in "Na yi kewar ki sosai, wuni d'aya ba mu had'u ba alhalin ina cikin garin nan, gaskiya ba zan k'ara nesanta kai na da ke ba." Da k'yar dai su ka rabu ta taimaka mi shi ta cire ma sa kayan ta mi shi wanka kafin su ka fito, zaune ya yi ta zuba mu su abinci a faranti d'aya, amma saboda sabo har Bilal sai da ya sa hannu a na su abincin ya sake ci, cikin farin ciki da k'aunar juna su ka kammala, Bilal ya wuce d'akin shi ya na kallo, su kuma su na nan falo. *Wannan ita ce rayuwar farin cikin da su ke ciki.*
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117