Skip to content

Chapter 53

Chapter 53

Kallon Kitse Book One Complete Hausa Novels 1,201 words 0 views Progress saved
Download Book

da ya yi yace "Malama ya dai? Har yanzu ba ki kwanta ba kamar ki na jiran mu." Ganin Haseenah ta nufi b'angaren ta ko a kwalar rigar ta ya sa shima ya bi bayan ta, ita ma wucewa ta yi ta je falon shi ta zauna kan d'aya daga cikin kujerun teburi ta na jiran shi, ai kam bai jima sosai ba ya shigo falon da alama wanka zai yi, kamar bai ganta ba haka ya wuce uwar d'akin shi ya fara cire kaya, ita ma bayan shi ta bi hannu ta kai da nufin kama mi shi ya yi saurin ja baya sosai yace "Nagode." Ko wando bai cire ba ya wuce ban d'akin, ta na nan zaune har ya fito ya shirya duk ta na kallon shi ta rasa ma abinyi, juyowa ya yi zai fita yace "Idan kin gama kallon nawa na fita ni, zanyi kallo daga yanzu zuwa lokacin da zan kwanta ba na son takura." Da sauri har da gudu ta k'arasa gaban shi ta rik'o hannun shi, za ta yi magana sai kuma ta kasa saboda yanda ya raba hannun ta da na shi, shi kam ta na rik'e hannun shi ya ji kamar ta zuba mi shi ruwan zafi a jiki, ba ta yi magana ba ya fice ya bar ta, falon ta biyo shi cikin rawar murya tace "A...a..abincin..ka..." Da k'arfi ya mik'e daga zaman da ya yi kamar zai had'e ta cikin d'aga murya iya k'arfin shi yace "Ba na ci, nagode, dallah ki fitar min daga d'aki, zuciya ta tafasa take idan ina kallon ki, sam muryar ki babu dad'in ji kuma duk kin bi kin takura ni da zance kamar wata sabuwar rediyo (redio)." Wani dogon tsaki ya ja yace "Haba, ni na rasa gane wannan jarabar." Kai tsaye d'akin Haseenah ya nufa ya na ci gaba da mita, ragwaf Khadija ta fad'a kan kujera ta fashe da kuka, har za ta d'aga sauti sai kuma ta kame bakin ta ta tashi ta koma na ta d'akin, har ta dasa wani sabon kukan sai kuma ta tuna maganar lahaifiyar ta da take fad'a mu su "Duk abin da ya yi zafi laganin shi Allah, ku rik'e Allah a cikin lamarin ku, ba shakka zai taimake ku dan ya na tare da ku." Wannan maganar ce ta sa ta d'auro alwala ta shinfid'a sallaya ta d'auki Qur'ani ta fara karatu, saida ta raba dare kafin ta kabbara sallah a kowace sujuda ta na kaiwa ubangiji koken ta. Usman kuma na shiga ko da ya sauke idon shi akan amaryar shi sai wani irin farin ciki da shauk'i ya rufe shi, sam ya manta da komai a kan shi haka ya so hayake ma haseenah, ita kam sam tsoro ya kamata dan haka ta k'i amince mi shi, da k'yar da sud'in goshi ta lallab'a shi ya koma d'akin shi, amma a ganin shi da ya ga Khadija gwara ya zauna shi kad'ai, haka ya sha baccin shi har kiran sallah asuba. *Allah ka azurta mu da abokan zama na gari* 08/02/2020 Γ  23:04 - πŸ’‹πŸ˜˜πŸ’‹: πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘ *KALLON KITSE* _(Ake wa rogo)_ πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘ _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _D'AUKAR FANSA_ *3* _BA SO BANE_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI_ *6* _JIHADI_ *7* _K'ANGIN RAYUWA_ *8* _ITACE K'ADDARARMU_ *9* _KAWU NA NE_ *10* _MAATA_ *11* _KALLON KITSE..._ *SADAUKARWA GA* _MATAN FARKO_ πŸ§•πŸΌ *(UWAYEN GIDA)* πŸ‡ΈπŸ‡¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_πŸ€œπŸ€› ```Fatan alkairi masoya``` 1. Mom teema Hakima 2. Yar baba ( Fatima Zara ) 3. Momyn Dady 4. Chappa *Auntyn Khadi* 5. BILKISU Z. YA'U 6. Raheenah m Abbacar 7. Aishan Umma 8. Maman Labyb 9. Aunty Hawwer 10. Hawwer Jidda 11. Alawiyya 12. Amina 13. Yagana Mousa 14.Rukayya 15. Maman souhailat 16. Ummu sultan 17. Ouma saadou 18. Rahilat 19. Azima *momyn Imane* 20. Mme Jamil 21. Ummi 1 22. Ummi 2 23. Nazeefa 24. Jamila 25. Maijiddah 26. Sadia magaji 27. Phartee shehu 28. Ummu halima 29. Halima Muhammad 30. Maman Tasleem 31. Jawahir Gombe 32. Fareedah Boube 33. Lubabatu Shehu shayi 34. Zeinab mai kano 35. Maman Ahmad 36. Firdaussi Shehu 37. Binta Umar 38. Preettyy Aeeshartyy 39. Rukayya Usman 40. Maryam Abdul Mumin 41. Salma Ibrahim 42. Hussy luv 43. Hafsat A.A 44. Jamila Musa 45. Choukriyya 46. Khadija Isa 47. Matar manya 48. Mamar Soja 49. Momyn Rasil 50. Meeynert 51. Mandiya😁 52. Habiba Bala _Duk wanda ya ga sunan shi to ya na zuciyar *Samira* ne, sai dai wanda na manta kawai a matsayi na na yar adam ajiza._ _Bismillahir rahamanir rahim_ *21* Abincin jiya ta fara d'aukewa kafin ta d'ora na karin kummalo, ba ta wani d'auki lokaci ba ta k'arasa shirya komai, saida ta shirya ta tashi Bilal shima ta taimaka ma sa ya shirya da sauri, karin kuma ta had'a mi shi ya ci ya k'oshi kafin ya nufi d'akin mahaifin shi, abun mamaki shine a al'adar Usman ba ya komawa bacci bayan sallah asuba, amma sai gashi yanzu rauni da sauyin da aka samu ya sa kasala ta rufe shi ya gagara abin da ya dace, haka ya koma ya kwanta baccin shi, doguwar riga kawai ya zura suka tafi ya kai shi, ko da ya dawo ya samu Khadija zaune a falon shi, da sauri ta mik'e ta kalle shi tace "Ina kwana." "Lafiya." Ya fad'a ya na shirin wucewa, da ido ta bishi har ya wuce d'akin amarsu, tashin ta ya yi a bacci suka shiga wanka tare su ka fito, sun jima kafin su gama shiryawa su fito tare, Khadija na zaune in da ya barta tun farko, zaune su ka yi akan kujera ita kam sai ta kafe shi da ido da tsananin mamaki, jinkirin ne ya sa yasa Usman kallon ta ganin ba ta da niyyar zuba abincin ya sa yace "Abincin na ki ko na siyarwa ne? Sai ki mana baya ni ai." Murmushi ta masa ta mik'e ta fara zubawa, shi ta fara zuba ma ta aje a gaban shi sannan ta zubawa Haseenah da ke ta kakkaryewa ta aje mata, ta na shirin zuba ma kan ta Haseenah ta ture faranti gefe ta mik'e tsaye ta kalle shi tace "Baby, zan koma d'aki na na kwanta, ba na jin sha'awar cin abincin nan kwata-kwata." Kamar mazari haka ya fara tambayar ta "To me za ki ci idan ba ki ci abinci ba? Fad'a min me ki ke so ki ci to? Ai ba kya zauna da yunwa ba ki cutar da kan ki." Cike da yatsina fuska tace "Umm, da ace zan samu indomie da na ji dad'i." Kallon Khadija ya yi ya kula kallon ta yace "Abu mai sauk'i, bara yanzu a dafa mi ki, kije ki kwanta to." Kallon Khadija ya yi da ke tsaye yace "Am dan Allah na ce ba, ki taimaka mata ki d'ora mata, ina ganin kamar ba ta da lafiya ne fa, dan gaba d'aya yanayin ta ya canza." Kallon shi Khadija ta yi ta na wani shegen murmushi mai kama da na mugunta tace "Ka yi hak'uri Abban Bilal, ban raina ka ba, kuma ka isa ka sani komai na yi maka, amma banda hidimar matar ka,

Table of Contents

Chapters

117 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117