Chapter 15
Chapter 15
so, kar kuma ka kuskura na gan ka ko a bakin titi ne, dan ran ka zai b'ace." Mik'ewa Bilal ya yi ya matsa kusan shi yace "Ka yi hak'uri Abba, ba zan sake ba." Kan shi kawai ya shafa bai ce komai ba, jakar shi ya d'auka mai d'auke da littafanshi yace "Na gama." Kallon shi ya yi yace "Ka tabbata ka k'oshi?" Kai kawai ya d'agaalamar Eh, hannun shi ya kama yace "To muje." Juyowa ya yi ya d'agawa mahaifiyar shi hannu yace "Sai na dawo sarauniya." Murmushi ta masa tace "Allah ya tsare, a kula sosai ka ji ko?" Usman ma kallon ta ya yi yace "Ni ma na tafi ba zan dawo ba." Ba alamar wasa a tare da ita tace "Sai na bika duk in da ka ke ai." Dariya ya yi yace "Kar ki damu sarauniya zan dawo ai, ke ce fa." "Ah to, sai na ma riske ka duk in da kaje." Ta fad'a ta na tashi dan had'a kayan da su ka karya. *Kafin mu ci gaba, za mu waiwaiya baya mu ji yanda wannan soyayyar ta fara ta Khadija da Usman.* _Sai mun had'u a shafi na gaba._β 10/01/2020 Γ 12:20 - πππ: ππππππππππ *KALLON KITSE* _(Ake wa rogo)_ ππππππππππ _SAMIRA HAROUNA_ *Littatafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _D'AUKAR FANSA_ *3* _BA SO BANE_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI_ *6* _JIHADI_ *7* _K'ANGIN RAYUWA_ *8* _ITACE K'ADDARARMU_ *9* _KAWU NA NE_ *10* _MAATA_ *11* _KALLON KITSE..._ *SADAUKARWA GA* _MATAN FARKO_π§πΌ *(UWAYEN GIDA)* πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€ ```Fatan alkairi masoya``` _Bismillahir rahamanir rahim_ *9* *Alhaji Ahmad*, dattijo mai dattako, mutum ne da Allah ya wadace shi da komai, dukiya, ilimi da 'ya'ya, matar shi d'aya *Hajia Sadiya*, suna zaune lafiya cikin farin ciki, mutum ne shi da bai da ra'ayin tara mata, hakan ya sa suke zaune daga Sadiya sai yayan ta, Allah ya azurta su da yaya maza guda biyar, *Ashir* shine babba, sai *Bashir* sai kuma *Habib* da *Mansur* da *Naseer*, Naseer na da shekara biyar aka samu cikin da ya wahalar da Sadiya, tun a lokacin su ke ji a jikin su cewa Allah zai musu sauyi ne, cikin ikon Allah kam bayan laulayin da ta sha sai gashi ta haifo kyakyawar yarinya mai kama da ita, *Nana Khadija*, yarinya ce da ta zama tamkar wata zinariya a cikin mutane, kowa soyayya ya ke nuna mata, lele kawai da gata take gani, su kan su yan uwanta suna matuk'ar k'aunar ta, dan har fad'a suke akan wanda ya fi sonta ko wanda zai d'auke ta, haka Khadija ta taso cikin gata da kulawar iyaye da yan uwa, sai dai tun da ta fara tafiya suka lura kamar tana da matsalar ido, basu b'ata lokaci ba wajen ziyartar likitoci, nan aka sanar da su tana da matsalar gani, bata iya gani da kyau sai dishi-dishi, sosai mahaifinta ya damu kuma yake yawon nema mata magani, amma sam ba'a dace ba har k'asar waje an fita da ita, haka dai suka hak'ura aka d'ora ta akan saka gilashi mai k'ara gani, wannan laurar sai tasa iyayenta da yan uwanta sake tausaya mata da k'ara k'aunar ta, sam larurarta bata tab'a damunta ba bare tasa damuwa, tana jin dad'in kasancewarta a yanda take, duba da wasu sam idon ne ma basa da su, tana da shekara *goma sha biyu* a duniya ranar wata alhamis da dare, suna zaune a farfajiyar gida su na ta hira Khadija na kan k'afafun mahaifin ta, da sauri ta juya ta kalli baban ta tace "Baba, ka ga wani ya shiga d'akin ka." Da mamaki ya juya ya kalli k'ofar d'akin na shi ya gan shi rufe, murmushi ya yi ya kalle ta yace "Auta ni banga kowa ba, gashi ki na gani ma d'akin a rufe ya ke." Naseer ne yace "Wallahi nima Baba sai na ga kamar giftawar mutum." Sake juyawa ya yi ya kalli k'ofar yace "To wa zai shigo cikin gidan bayan ga k'ofar nan a gaban mu kuma ace ba mu ga shigowar shi ba." Almajirinsu da ke zaune nesa da su ne ya na cin abinci ne yace "Baban Khadija wallahi nima na gan shi, wani dogo da fararen kaya, amma banga fuskar shi ba, kuma na so inyi magana saina kasa na ji tsoro." _Wallahi wannan wani abun al'ajabi ne da ya faru da wata baiwar Allah da na sani, za mu iya cewa mala'ikan mutuwa ne_ Sadiya ce tace "Kai Ashir tashi ka duba mana." Kallonta ya yi yace "Mama, ni kad'ai? Kawai ki bar shi idan ya ga ji zai fito ai mu gan shi." Dariya aka saka sai Baba ne yace "Ki bar shi kawai, watak'ila fa gizo idon su ke musu, na ga ai ga k'ofar shigowa nan, babu wanda mu ka ga ya shigo." Haka aka share wannan magana aka ci gaba da hira, Khadija ce bacci ya dauke ta a k'afafun shi, a hankali ya d'auke ta ya kai ta makwancin ta ya shafeta da addu'a, fitowa ya yi su Ashir ma har sun tashi, dawo da su ya yi suka zauna, ya jima ya na musu nasiha da su rik'e Khadija da kyau su zama gatanta ita kad'ai ce k'anwar su mace, har sha biyu na dare ta wuce kad'ai suka tashi, d'akin shi ya shiga ya yi shirin kwanciyar shi sannan ya d'auro alwala, raka'a biyu ya samu damar yi wani nauyayyen bacci ya sure shi akan sallayar, daga wannan bacci ne Allah ya karb'i abin shi. Mutuwar nan ta girgiza mutane sosai, musamman Sadiya da ke kwance asibiti ba ta san me ake yi ba, Khadija ma yan uwan ta kad'ai take iya yarda da su, amma haka ko da lokaci ya tafi kowa ya manta, sai dai ciwon na nan a zuk'ata, dukansu mazan babu wanda bai da aikinyi mai kyau, hakan ya sa suke matuk'ar kula da k'anwar su, sosai suke shagwab'a ta, ga yarinya na girma amma gatan da take samu yasa kullum kamar yarinya. Tun Khadija na da shekara sha biyar Ashir ya gwangwaje ta da moto, duk da sauran yan uwan kowa ya so ace shi ya siya mata, amma haka suka hak'ura tun da ya fisu zafin nama, wannan lokacin ne aka musu rabon gado, kowa ya tashi da na shi kason mai tsoka, na Khadija kuma tace a bawa Ashir da Mansur su ci gaba da juyawa dan sune suka fi sha'awar kasuwanci, mamansu ma dama ta na nata kasuwanci, dan haka ta ci gaba daga inda ta tsaya. *Duk* wata ba'a daina abin da Alhaji Ahmad ya fara ba, ana yanka rago ayi sadaka, sannan akanyi waina ayi miya sai su aika inda mahaifinsu ke zama da yamma wajen abokanan shi, haka rayuwar ke tafiya har lokacin da Khadija ta ci jarabawarta kuma sakamako mai kyau, babbar walima yayyun ta suka shirya mata a bazata, kayan da suka shirya mata suka sata ta saka suka tafi da ita babban wajen cin abinci, k'awayenta da maza da dama ta samu wanda su ka yi karatu tare, ta ji dad'i sosai a ranar, anan ta yanka (πbansan me zan kira cake da hausa ba, amma bara nace mu
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117