Chapter 46
Chapter 46
fita daga gidan ba?" Cikin turo baki tace "Na shirya fa na ke ta jira aunty Khadija ta min magana, tunda ai ba zuwa zanyi ba na tisa ta a gaba har sai ta gama shirin ta, ina falo kawai sai fitar ta na ji." Ba dan ya yarda da abin da ta fad'a ba yace ta jira shi ya zo ya d'auke ta, dan in dai Khadija za ta fita to bata kaiwa warhaka bata fita ba saboda taje ta dawo da wuri ta kama aikin gaban ta, hanya ya d'auko dan ya zo ya d'aukar ta ya kira Khadija a waya, bayan ta d'auka ne yace "K'anwar ki ta kira ni tace wai kin tafi kin barta, shine na ce ya akayi haka ta faru?" Khadija da ke tuk'i ne tace "Ba ta fad'a ma ka na kai mak'ura bane wajen jiran ta? Ko kuma kawai ta fad'a ma ka abin da ta ga dama ne?" Murmushi ya yi daga in da ya ke yace "Ran gimbiya ya huce, kawai dai ina tambaya ne." Cike da rashin kulawa tace "Ka ga ina tuk'i fa, sai munyi magana." Kasje wayar ta yi ta ci gaba da abin da take, shima kuma d'auko Haseenah ya yi sai dai bai fad'a mata yanda su ka yi da Khadija ba har suka isa ya sauke ta, da d'ar-d'ar ta shiga gidan bikin ta na sallama wata bayan wata, cikin sa'a ta hango su Hassana da Husseina da duk sauran yan uwan tare da Hajia sarakuwar su zaune, da azama ta isa can ta zauna su ka gaisa, Rabi'a ce ta fara tambayar ta da "... *Ku yi hak'uri masoya abisa jinkiri na, hakan na faruwa ne sakamakon al'amura da su ke sha min kai na.*π 04/02/2020 Γ 21:00 - πππ: ππππππππππ *KALLON KITSE* _(Ake wa rogo)_ ππππππππππ _SAMIRA HAROUNA_ *Littatafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _D'AUKAR FANSA_ *3* _BA SO BANE_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI_ *6* _JIHADI_ *7* _K'ANGIN RAYUWA_ *8* _ITACE K'ADDARARMU_ *9* _KAWU NA NE_ *10* _MAATA_ *11* _KALLON KITSE..._ *SADAUKARWA GA* _MATAN FARKO_π§πΌ *(UWAYEN GIDA)* πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€ ```Fatan alkairi masoya``` *πΈπ¦ZAMAN AMANA WRITER'S* (GIDAN ZAMAN LAFIYA DA AMANA INSHA ALLAH)π€π€ *SANARWA! SANARWA!! SANARWA!!!* *INA JIGA JIGAN MASOYAN πΈπ¦ZAMAN AMANA WRITER'S WAD'ANDA BASU DA TAMKA A WAJENMU????? DUK WANDA YAKE TARE DAMU A CIKIN GROUPS D'INMU TO MUN TABBATAR K'AUNARMU CE TASA KUKA KASANCE TARE DAMU, MUNA YABAWA KUMA HAR ABADA BAMU DA KAMARKU WALLAHI,π DUK DA HAKA DAI GA LOKACI YAZO, KUMA DAMA TA SAMU NA TABBATAR MANA DA KUMA NUNA MANA HAK'IK'ANIN K'AUNAR DA KUKE MANA,π* Kunsan cewa k'ungiyarmu *πΈπ¦ZAMAN AMANA WRITER'S* suna cikin gagarumin gasa na samun award Wanda *women24 TV WhatsApp group* suka shirya kuma zasu gudanar? A wannan gasar ne za'a samu k'ungiyar da tafi kowacce k'ungiya yawan fans da Kuma bin k'a'idar rubutu Dan ki samu damar zabar k'ungiyarmu *πΈπ¦ZAMAN AMANA WRITER'S ASSOCIATION* zaki iya tuntub'ar wannan lambar 09030159301 Dan su saki a *WOMEN24 TV WHATSAPP GROUP* anan ne za'ayi zab'en k'ungiyar da tafi kowacce k'ungiya yawan masoya *Women24 Tv* Ba zabe kad'ai zakiyi ba Zaki k'aru da abubuwa da yawa kamar haka *Yanda ake girke girke* *yanda zaki gyara jikinki* *yanda zakiyi makeup* *yanda zaki daura Dan kwali* Kuma suna shirye shiryen nan na *arewa24 tv* kamar su *TARKON KAUNA* *DADIN KOWA* *KWANA CHASA'IN* *JAMAI RAJA* *SAPNE SUHANE* *GIDAN BADAMASI* *RUDIN ZUCIYA* *BAGHYA LAKSHMI* *AKUSHI DA RUFI* *AUDIO NOVEL* *HAUSA NOVELS* Kada ki manta da ranar zabe inkin shiga group d'in ki zaba *πΈπ¦ZAMAN AMANA WRITER'S* tanan ne zaki iya nuna mana irin sonda kuke ma k'ungiyarmu da littattafammu Allah yabar zumunciπ€ππ₯°π _Bismillahir rahamanir rahim_ *19* "Haseenah ke kad'ai ki ka taho ne?" Da kunya ta kalle ta tace "A'a, shi ya kawo ni ai, da tare da aunty Khadija zamu taho, to kuma bansan tafiyar ta ba." Ai kuwa abin da ta fad'a ya samu shiga sosai, hakan ya sa Hassana cewa "Amma yasan za ku taho tare?" "Eh ya sani, shi yace ma mu taho tare tunda safe." Rabi'a ce tace "Amma kuma dan rashin mutumci shine ta taho ta baro ki? Lallai ma matar nan, kullum iskancin ta k'aruwa ya ke." Husseina ce tace "To ba ita ke da mota ba, kinga kuwa dole ta yi yanda ta so." "Hum." Cewar Hassana, cike da wauta Aziza tace "Wallahi kema kar ki yarda ya siya mi ki ko moto ne, dan ba za ki zauna ta na mulkar ki ba." Hajia ce ta kalli Haseenah tace "Ki shiga wajen mai jegon mana ku gaisa." "To Mama." Ta fad'a ta na mik'ewa, cike da dattako Hajia ta sake cewa "In ce dai ya baki abin da za ki kaiwa mai jegon?" 'Yar dariya ta yi tace "Eh Mama, tunda safe ma ba bamu dukan mu." Hajia na ganin wucewar ta ta kalle su dukan su tace "Yanzu mi ye anfanin haka? Wannan yarinyar yaushe ta shigo cikin ahalin ku da har ku ka yarda da ita haka? Mi ye Khadija ba ta mu ku ba a rayuwa da har ku ka butulce ma ta haka? Dukan ku fa mata ne, kuma Rabi'a ce kad'ai ba ta da abokiyar zama a ciki, ke kan ki Aziza da ki ke wata banzar magana na ga saurayin da ki ke so ai mata gare shi, shin idan aka mu ku haka za ku ji dad'i? Nace za ku ji dad'i idan aka mu ku haka? Ba za ku ji ba kenan? Shine kuma ku ke wa wata rashin kunya wacce ta mu ku alkairin da ki shi d'an uwan na ku bai mu ku kamar shi ba, shi d'an uwan na ku kunsan yanda ya ke d'aukar ta da kuma matsayin ta a wajen shi? Ku kan ku da akwai mutumci ai Khadija tafi k'arfin komai a wurin ku, wallahi ta wuce cin mutumci da cin zarafi, ko ba komai mafi soyuwar abu a zuciyar d'an uwan ku shine d'an wannan matar da ku ka raina, sannan ina yak'ini akai ko tamtama babu cewar Khadija ma tafi soyuwa a zuciyar d'an uwan ku, idan kuma kun shirya rasa shi ne to dan Allah ku ci gaba da mata rashin kunya, ni dai na fad'a mu ku gaskiya a matsayi na na uwa, kuma ke Aziza." Hajia ta fad'a ta na nuna Aziza da hannu kafin ta ci gaba da "Kar na sake jin bakin ki daga yau in har su na maganar su, tunda ke kinfi kowa butulcia cikin su, Aziza matar nan har kashi da fitsarin ki ta ci kamar yanda ni ma na ci, matar nan ta kwantar da ke a gaban k'irjin ta kamar 'yar da ta haifa, matar nan ta mi ki wanka da hannayen ta ta shirya ki, duk lokacin da mijin ta baya nan ke ce abokiyar rayuwar ta, har rayuwa ta canza mu su ta haifi nata yaron ba ta banbanta ki da shi ba, Aziza sai da aka kai k'adamin da ta ware mi ki d'aki a gidan ta, kinfi kowa sanin Khadija a cikin dangin mu, amma kash ke ce farko wajen juya mata baya, Allah ya kyauta." Ta na fad'a mik'ewa ta yi daga kan
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117