Skip to content

Chapter 80

Chapter 80

Kallon Kitse Book One Complete Hausa Novels 1,199 words 0 views Progress saved
Download Book

tunanin ta kenan ba zai zo ba ya na nufin na yi ta zama a gida. Gida Usman ya koma dan sanar da su ya tattauna da Nura kuma za su je neman masa aure, har d'aki ya samu iyayen na shi ya sanar da su yanda ake ciki, ya d'an jima suna tattaunawa akan lamarin kafin ya fara yunk'urin tafiya, "Karb'i nan." Cewar malam, kallon malam ya yi ya kalli kofin hannun shi, ruwa ne dai fari k'al da su, kallon malam ya yi yace "Baba wannan fa? Na miye?" "Karb'i kasha, na tsari ne." Ya fad'a ba alamar wasa, hannu ya sa ya karb'a ya yi bismillah ya kifa kai ya shanye, aje kofin ya yi ya musu sallama ya fita, bayan shi Hajia ta biyo saida ya zi gaf da d'akin ta tace "Bismillah nan." Saboda ba za ta kira sunan shi ba, bayan ta kawai ya bi suka shiga, ya na shiga ta mik'o mi shi roba da nono a ciki da abun magani tace "Shanye ka bani roban, kuma ka hi bismillah, sannan kasha zuciyar ka d'aya ba tare da tunanin cutar da wani ba ko wata." A raunane ya kalle ta yace "Hajia shi kuma wannan na miye?" Wani kallo ta watso masa amma ba tace komai ba, sanin ma'anar kallon ya sa ya kifa kai nan ma saida ya shanye kad'ai ya mik'a mata robar ya mata saida safe ya fito, haka ya d'auki hanya ya na tunanin abin da iyayen shi ke nufi da shi, da haka ya isa gida ya samu Haseenah yau dai ta yi girki kam, amma badan ranshi na so ba ya ci abin da ta dafa d'in har suka kwanta. Bayan tafiyar shine Hajia ta ji kamar ta yi kuskuren rashin sanar da shi wani abu, amma ta yi niyyar fad'a mi shi gobe da safe idan ya zo, sai dai kuma ta makara kam, dan Usman ya jima baiyi bacci ba ya na dafe da cikin shi, da Haseenah ta tambaye shi kuma bud'ar bakin shi cewa ya yi "... _Mu tara a shafi na gaba insha Allah._ *Ku yi hak'uri da ni mutane na abisa jinkira na, hakan na faruwa ne saboda sauyawar yanayi na.* ~*LUVE U ALL*~πŸ₯°πŸ˜˜ 23/02/2020 Γ  13:03 - πŸ’‹πŸ˜˜πŸ’‹: πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘ *KALLON KITSE* _(Ake wa rogo)_ πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘ _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _D'AUKAR FANSA_ *3* _BA SO BANE_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI_ *6* _JIHADI_ *7* _K'ANGIN RAYUWA_ *8* _ITACE K'ADDARARMU_ *9* _KAWU NA NE_ *10* _MAATA_ *11* _KALLON KITSE..._ *SADAUKARWA GA* _MATAN FARKO_ πŸ§•πŸΌ *(UWAYEN GIDA)* πŸ‡ΈπŸ‡¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_πŸ€œπŸ€› ```Fatan alkairi masoya``` _*Lubabatu Shehu shayi*, ina ganin sak'onninki sosai, lallai ke masoyiya ce ta hak'ik'a, tun a gidan Raheenat muke tare, kuma gashi har yanzu kina tare dani a gida na na kallon kitse, Allah ya bar k'auna._ *KALLON KITSE FAN'S 1&2* πŸ’‘ _Wannan sadaukarwar taku ce, kuyi yanda kuke so da ita._πŸ’‘ _Bismillahir rahamanir rahim_ *30* "Wallahi kawai wani kindirmu ne Hajia ta bani nasha, gaba d'aya ya na neman lalata min ciki ma." K'aramin tsaki ya yi, ita kam da mamaki tace "Kindirmu kuma? Haka kawai?" Kamar wanda aka takura dole yace "Ina jin ko magani aka saka a ciki kome, ban dai sani ba ni dai kawai ya lalata min ciki sai tayar min da zuciya yake." Cike da kissa ta shafo shi tace "To in hakane kar ka sake sha mana, tunda ya na tayar maka da zuciya, zai iya saka ka amai ma fa." "Ina tunanin haka nima." Ya fad'a ido rufe, kallon shi ta yi tace "To wai ma maganin meye aka baka? Ba ka da lafiya ne dama ban sani ba." Bud'e ido ya yi ya kalle ta yace "Ke kar ki tsora ta, lafiya ta k'alau mana ke shaida ce, tace dai ko maganin tsarin jiki ne da kuma...mtss na manta dai, kawai share." Tashi tayi zaune ta na kallon shi idon shi rufe, tabbas in dai har hakane to iyayen shi sun fara hango wani abu kenan, d'aukar mataki shine abin da ya kamace ta kawai, dan haka tace "To beby in hakane me zai hana ka karb'o maganin, kaga sai ka rik'a sha anan zaifi da sai kaje can, koya ka gani." Cike da damuwa yace "Kar ki damu kan ki, ni fa ba wani shan shi zan dinga yi ba, ina addu'a na tsarin jiki hakan ma ya isa, kawai ki rabu da su, kinsan tsofaffin nan da tame-tame." Murmushi ta yi tace "Duk daha beby, idan ma ba za ka sha ba ai sai ka karb'o shi, dan in har ya na wajen su to ba fashi sai ka sha shi ko da za ka mutu ne." Shiru ya yi ya na tuna lokacin da ya tambayi Hajia amma ta yi banza da shi, hakan na nufin dole dai ya sha ba makawa, dan haka yace "Ba tabbacin za su k'ara bani, amma in har sun bani na sha to zan karb'o shi daga wajen su na taho da shi." "Gaskiya kam, da ba zan so wani abu ya samar min miji ba uban 'ya'ya." Ta fad'a ta na gyara kwanciyar ta, daga haka babu wanda ya sake magana har bacci ya d'auki dukan su. *Yau kam* Alhamdulillah Khadija ta tashi jiki da sauk'i sosai, da kan ta ta gyara d'akin ta da na Bilal da ma na Mama, zuwa k'arfe goma kuma ta fita madafar da matan gidan ke aiki, da kan ta ta fara girkin rana kafin matan yan uwan ta suka fito su ka kama aka k'arasa, *12:10* yaran su ka fara shigowa da sallama wasu kuma da gudu, kowa wajen tashi uwa ya nufa kafin suka wuce d'aki dan cire kaya, lokacin ne Khadija ita ma ta shiga d'aki dan ta yi wanka ta yi alwala, ta na d'aure da k'irji za ta shiga ban d'aki wayar ta tayi k'ara, dawowa ta yi dan d'auka amma har ta tsinke, d'aukar wayar ta yi ta duba mai kiran, sunan k'awar ta ne Kaltume, aje wayar ta yi da niyyar idan ta fito ta kammala za ta kira ta, har ta aje ta yi sauri ta sake d'auka saboda idon ta da ya sauka kan kwanan (date) wata, dubawa ta yi da kyau taga tabbas yau wata na da kwana *21*, kai da kawowa ta fara yi tsakiyar d'akin ta na tunanin yanda ta kasa ankara da lokacin al'adarta har wata ya ja haka, sai lokacin kuma ta iya tunawa fa tunda Usman ya yi aure ma bata sake ganin jinin ta ba, to me hakan ke nufi? Ta tambayi kan ta. "Kenan ciki gare ki kamar yanda Mama ta tambaya?" Da sauri ta zo gaban madubi ta janye d'aurin k'irjin ta tana shafa marar ta, tabbas sai lokacin kad'ai ta iya fahimtar tudun da mararta ta yi, a hankali ya fad'a kan gado ta yi zaune ta rufe ido, wasu hawayen farin ciki ne suka zubo mata ba tare da sanin ta ba, hannu ta sa ta share ta d'aga hannu sama ta furta "Alhamdulillah Allah, Allah kaine Allah, kuma kai ka ce mu rok'e ka za ka amsa mana, Allah nagode ma ka abisa

Table of Contents

Chapters

117 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117