Chapter 117
Chapter 117
yarima ma zai zama waliyi na." Dariya suka saka a tare sai Khadija da tace "Komawa baya kenan, to idan zaka je d'aurin auren dai ka shafa gawayi a kanka danka rufe wannan farin abun na kan ka." Sake shafa kan yayi yace "Alamar arzik'i ne ai, kuma naga kema akwaita a kanki." Cike da k'aguwa Bilal yace "wai yanzu na zo da matsalata amma ku manta kun shiga sabgar gabanku, Allah ya shirya min ku iyayena, banda kamarku a duniyar nan." Harya juya zai fita ya tsaya ya nuna su Humaira da yatsa yace "Kuma wallahi babu inda za ku je, na gaji da wannan yawan na ku kullum." Khadija ce tace "To ni ka ban makullin tawa motar zan fita, ai dai kasan aro ne na baka jiya ko." Kallon Usman yayi yace "Idan sarki ya bayar da izinin fita sai ku fad'a min zan kawo mu ku." Cike da jin dad'i Usman ya aika mishi da sumbata yace "Allah ya maka albarka yarona, shi ya sa banda matsala da gidan nan ko bana nan nasan akwai original Usman a gidan, da ni ne da yanzu sun min fari da ido na basu makullan." Fita yayi daga d'akin sai Usman daya kalli su Aisha yace "Ku kuma ki fito daga nan munafukai kawai, dama da kinga suna raba ido kinsan basu da gaskiya, kuma wallahi ku ka sake shigar masa d'aki ba neman izini da kaina zan hukuntaku." Cikin turo baki suka sauko suka fita daga d'akin suna kumbura, dan tunda su ka ji Bilal ya rantse sun sa babu inda za su je, suna fita Usman ya kalli tsofaffin nashi yace "Ku shirya da kyau, wannan hutun na k'arshe zan had'a yaran nan da Bilal na aurar da su." Wata sanyayyar ajiyar zuciya Khadija ta sauke tace "Alhamdulillah, wallahi naji dad'i da wannan maganar, dan duk sanda na kalli yaran sai naji fargaba ya ziyarceni, gashi k'awayen su sun fara aure, sai kaga an fara sakawa yaranka wani tunani na daban alhalin kana tsaye kan tarbiyarsu tsawon lokaci." Haseenah ce tace "Allah yasa haka shi yafi zama alkairi, amma ka fitar musu da maza ne?" "Eh to, a tunani na dai da zan had'a Aisha da *Kamal* (babban d'an Murtala) ne." Humaira kuma sai a had'a ta da *Mujahid* (d'an Issoufou d'an uwan Usman), amma fa sai in basu da wanda suke so, dan ba zamu had'a su da wanda ba sa so ba tunda zamaninmu da nasu ba d'aya ba, da a lokacin yanzu ne aka mana auren da aka yi mana ni da *Dijangala* to na tabbatar ba za su zauna ba." "Ai ko ni da ga yanzu ne aka had'a ni da kai to da babu abin da zanyi da tsoho." Cewar Khadija kafin ta d'ora da "A gaskiya dukansu sun fad'a min suna da samarinsu har shi Bilal d'in." Kallonta Usman yayi yace "Kenan duk sun fad'a mi ki nine suka mayar bare." Gwalo ta mi shi tace "Nifa uwa ce." Haseenah ce tace "Aunty su wa suka fad'a mi ki suna so?" Cike da k'asaita tace "Sirri ne tsakani na da yara na." Tasowa Usman yayi ya bata kunnanshi yace "To fad'a min a kunne naji." Ai kuwa rad'a mi shi tayi cewa "Bilal ya fad'a min suna soyayya ne da *Ikram* (yar Kaltume), sai Humaira tace suna soyayya da *Kamal* d'in da ka ke son had'a Aisha da shi, sai kuma Aisha tace wani yaro ne mai sunan *Jabir*, d'ane ga Alhaji Abbakar, amma kuma da wata yar matsala." Kallonta ya yi yace "Matsalar me?" D'orawa ta yi da "Domin kuwa *Miemie* (yar Ashir) tana mutuwar son Bilal, dan har ta fad'a masa ma, kuma yace ba zai iya cewa baya sonta ba saboda tana birge shi sosai." Dariya usman ya yi sosai kafin yace "Dan haka saiku shirya, yaronku da mata biyu zai fara insha Allah, na yarda da mazantakarshi." _Tofa fan's wata sabuwa, ga Usman na shirin lak'abawa Bilal mata biyu a lokaci daya, tabbas akwai wasu darussa a cikin labarin rayuwar gidan Bilal, sai dai Meeranku yanzu ta zama lazy wrriter, da zan zo na kawo mu ku d'orawar shi amma ba zan iya ba saboda na gaji yasin._ *Alhamdulillah* *Alhamdulillah* *Alhamdulillah* *Ina godiya ga Allah da ya nuna min na kammala littafi lafiya kamar yanda na fara, Allah ubangiji kasa a anfana da darasin dake ciki, Allah ka sa mu tsarkake zuciyoyinmu wajen yin kishi mai tsafta, duk wanda suke da abokan zama Allah ka k'ara had'a kansu, wanda basu da kuma Allah ka had'a su da na gari, Allah ka k'ara sanyaya mana zuk'atanmu.*👏👏👏
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117