Chapter 66
Chapter 66
dan haka ta marairaice tace "Um,um gaskiya ni na fasa tafiyar ma, ka ga kai kasuwancin ka ne zai kai ka, bai kamata muje tare ba kuma na hana ka sabgar gaban ka, kawai kaje Allah ya tsare mana kai, ranar da na haihu sai mu tafi tare da yaronmu mushak'ata." Saida ya rumgume ta yace "Gaskiya ban ji dad'i ba, Haseenah ba zan iya farin ciki ba ki na nesa da ni, me ya sa ba za ki je ba? Zan iya yin wata d'aya fa ko sati uku ban dawo ba, ki na ganin zan iya rik'e kai na bayan na saba da ke a d'an lokacin nan." Cike da gatsali tace "To ba ga aunty Khadija ba, ku je tare mana, ni kuma sai mu zauna abunmu ni da yarona Bilal, ko ya ka ce?" Tunda ta ambaci sunan ya ji kamar ta jefe shi da mashi akan tsohon ciwon shi, b'ata rai ya yi yace "Ya ina magana da ke za ki kawo min maganar matar can? Gaskiya ba na so kar ki sake." Saida ta shafi fuskar shi tace "To shikenan yi hak'uri ba zan sake ba." "To yanzu fad'a min za ki je ne?" Ya fad'a ya na k'ara cukuikuyeta, ba alamar wasa tace "Gaskiya ba zan je ba, kawai ka tafi kai kad'ai." "Shikenan, amma taya zan barki ki zauna tare da matar can? Na ga fa ba wani sakin jiki ki ke da ita ba." Shiru ta yi ta na tunanin abinyi ita ma, da sauri yace "Ko na kira Hajia ta turo mi ki Aziza? Tunda kinga dama ita ce ke zuwa nan idan zanyi tafiya." Wani murmushi ta yi da bai kai ciki ba tace "To shikenan ba damuwa, hakan ma ya yi ai." Da haka ya fito ya shiga d'akin shi ya yi wanka ya shirya ya fito kan teburi, saida Haseenah ta fito kafin su ka fara cin abincin, tabbas daga yanda ya ke cin abincin za ka san ya masa dad'i, amma da zaran ya had'a ido da wacce ta dafa abincin saiya d'aure fuska, haka su ka gama ya tashi ya fita su ka bishi da addu'a, Khadija da ta bi bayan shi har wajen mota sannan ya juyo ya kalle ta yace "Ya dai malama ki ke bina haka?" Murmushi ta yi tace "Abban Bilal hushi ka ke dani har yanzu akan abin da ya faru?" Wani d'auke kai ya yi yace "Mtsss, ba komai kawai, kawai dai ki na ba ni mamaki ne." A hankali ta janyo hannun shi ta na shafawa, in da shi kuma ya ke jin kamar hannun wuta ne da ita, cikin taushin muryar da tasan ta na tasiri akan mijin ta ta fara magana "Dan Allah ka yi hak'uri ka yafe min, insha Allah ba zan sake b'ata ma ka rai ba, ka ji? Ka yafe min, kasan hankali na ba ya kwanciya idan ina ganin ka haka." Saida ya raba hannunshi da na ta yace "Shikenan ba komai, Allah ya sa haka." Juyawa ya yi zai shiga mota tace "Shikenan kuma ba komai za ka tafi." "Kamar me fa?" Cikin yanayin jan hankali tace "Ba rumgumewa, ba sumbata, abun ba armashi." Kasak'e ya yi ya na kallon ta da tunanin abinyi, matsawa ta yi kusan shi ta shafo fuskar shi, a hankali ta kai bakin ta kan na shi ta zura harshenta cikin bakin shi, harshenshi ta kama tana wasa da shi in da ta kai d'aya hannun ta cikin rigar shi ta na murza k'irjin shi, d'aya hannun kuma shafar sumar kan shi take ta na yamutsata, tunda ya lumshe ido ya rasa kuzarinshi, hak'ik'a ya na son abin da take ma sa sosai d'in nan, amma ya na jin ba zai iya biye mata ba, amma da ya ke Khadija bala'i ce saida ta watsa mi shi duk wani lissafin shi da nutsuwa ya ma manta ina ne ya ke yanzun, me kuma zaiyi ko ya ke yi, saida ta ji jikinshi ya saki sosai sai wani gurnani da yake ya na k'ok'arin kai hannayen shi cikin rigar ta kawai ta raba kan ta da shi, wani arnan kallo ta masa da manyan idon ta a cikin gilashi kafin ta kashe mi shi ido d'aya, wata yar mik'a ta yi tare da fad'in "Ashhhh." Bye bye ta mi shi ta juya da nufin komawa ciki, wata karairaya ta dinga yi wanda ya sa hankalin Usman k'ara tashi saboda yanda take juya jikinta, wata zabura ya yi saboda wani zirrrrr da ya ji tun daga k'asa har sama, fitowa ya yi daga motar ko rufewa baiyi ba ya bi bayan ta har da gudu ya na so ya kamo ta, ta na shiga falon ta ga Bilal zaune sai kawai ta wuce d'akin ta, Bilal na ganin baban shi ya bi bayan maman shi sai kawai ya mik'e ya fita, wajen mai gadi ya zauna su na hira ya na kallon hanya, Usman na shiga wani k'arfi ne ya zo mi shi cikin sauri ya ke son aika sak'on shi, haka dai al'amari ya yi nisa sosai suka gangara, tabbas tun bakin k'ofar za ka ji abubuwa kala kala masu rikatar da mutum, amma ya na k'arasa shiga ciki sai ya ji wani b'acin rai da rashin ma'ana da...abubuwan ma dayawa, da k'yar ya k'arasa abin da ya fara cikin d'an lokaci ya samu nutsuwa ya tashi ya yi wanka ya saka kayan shi, ko kallon ta baiyi ba ya wuce abin shi ya na jan tsaki ya na gunguni. *A gurguje* Bayan ya fita gida ya nufa in da ya aje mu su duk wani abun buk'ata, sannan ya fad'awa Hajia ta tura Aziza can ta taya Haseenah kwana, tunda yamma ko da Haseenah ta karb'i girki Usman ya zo gidan, bai bari ta yi aikin ba ya zura ta d'aki ya na ta huce haushin shi na safe, har saida ta kai ita kan ta Haseenah ta fara nadamar kan ta dan ba k'aramar wahalar da ita ya yi ba, hakan ya sa ko da dare ya yi yace ta shirya suje cin abinci, saida su ka shirya za su tafi ya shigo falon Khadija yace Bilal ya zo su fita unguwa, sam ba ta yi tunanin har da Haseenah ba, har su ka fita sune sai sha d'aya da rabi na dare suka dawo, kai tsaye kowa falon shi ya nufa, sai lokacin ne Bilal ya fad'a mata har da auntyn shi su ka tafi, ba ta nuna mi shi komai ba, amma ta na shiga d'aki ta yi yan dabaru ta ci abinda ya sawak'a saida ta zubar da hawaye, har ta yi bacci ba ta ga Usman ba da sunan zai mu su saida safe. Misalin *08:10* ya shigo falon ta cikin shirin da gani ba tambaya kasan tafiya zaiyi, tare suke da Haseenah dan Bilal na d'aki har yanzu ya na shiri, kud'i ya mik'o mata yace "Ga wannan kya yi anfani da shi, ni yanzu zan wuce Niamey zuwa asuba kuma jirgin mu zai tashi, nasan akwai komai babu wani abin da za'a buk'ata, sannan maganar kai Bilal makaranta na barwa amarya ta duka makullan motar da tawa da taki,
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117