Chapter 13
Chapter 13
gidan mijin ki ba." Cikin sanyin jiki Haseenah tace "Ke, wannan ai ba komai bane, gaskiya ta fad'a." "Tab'." Cewar Aziza tare da kallon k'awar ta, farantin abincin su ta d'auka ta d'auki bredin tace "Muje d'aki sai mu ci ko." Tashi su ka yi su ka bi bayan ta, abinci su ke ci su na hira, Haseenah dai na sauraren su sai dai ta yi dariya, har su ka gama su ka d'ora daga inda su ka tsaya, ko da yamma ta yi su ka kama mata aikin dare ta yi, da su ka gama za su tafi kyaututtuka ta ba su, turaruka da sauran kayan kwalliya da kud'i wai su shiga adaudaita, da k'yar su ka karb'i kud'in da ta dage sosai, su na tafiya ta koma d'aki ta yi wanka ta shirya dan tarbar mijin ta, ta na gamawa ta d'auki d'aya kwanukan abincin ta sallama har falon Khadija, amsawa ta yi Bilal na zaune kusa da ita ya na karatu, da murmushi ta amsa ta na fad'in "Amarya ke da kan ki?" Sunkuyawa ta yi ta aje kwanukan ta d'ago ta kalle ta tace "Ga abincin ku nan." Juyawa ta yi za ta fita Khadija tace "A'a, ban gane abincin mu ba, ni da wa? Ko kin manta ba'a raba abinci a gidan nan? Ai Abban Bilal bai yarda da haka ba, duka iyalinshi su na cin abinci tare ne." Juyowa ta yi cike da gadara da ido tsakar kai tace "Eh, na sani, amma waccen ai tsohon yayi ne, yanzu kuma na shigo gidan, dole za'a samu canje-canje da dama, daga yanzu in dai girki na ne gaskiya miji na zai ci abinci a nawa b'angaren ne ba na shi ba." Juyawa ta yi har ta fara takawa Khadija ta gyara zama tace "Haseenah, nasan kinsan abinda ki ke shirin aikatawa kamar k'ok'arin rusa farin cikin gidan nan ne, dan haka kar ki ce za ki biyo min ta wannan hanyar, da ba zan d'auka ba, kin ganni nan? Wallahi ba na d'aukar raini ko rashin kunya, zaifi mi ki tun wuri ki fara taka tsantsan, abinci kuma ki d'auki kayan ki ba zan ci ba, ba kuma zan bawa yaro na ba, dan bansan me ki ka saka mana a ciki ba." Wata dariya Haseenah ta yi tace "Ikon Allah na kwance ya fad'i, wato ke yanzu tunanin ki kenan? Nima zan yi abin da ke ki ke yi ne, hum! To ki farka, ni ba boka ba malam zan mallaki miji na, ke kuma da ki ke barbad'e a abinci sai ki yi ta yi, da sannu k'aryar ki za ta k'are a gidan nan." Tsaye ta mik'e da mamaki a fuskar ta tace " Au! Kema tunanin ki kenan? Hhhhhhhh, lallai yarinya, in kuwa har wannan shine tunanin ki, to ki zanca tun wuri, dan wata rana zuciyar ki za ta iya raya mi ki kema ki bi boka da malam dan samun zuciyar babban mutum, kinga kuwa har abada ba za ki san sirri na ba." Matsowa ta yi kusan ta dafa kafad'ar ta tace "Haseenah, ina kishin miji na, amma duk da haka bai sa na ji a raina cewa zan iya cutar da ke ba, ki kwantar da hankalin ki sannan ki nutsu, sannu a hankali sai kema ki ciri tuta a wajen mijin ki, ni zan taimaka mi ki kamar yer uwa ta." Matsawa ta yi nesa da ita yace "Me? Taimako? Ki na kishiya ta za ki taimake ni dan na samu soyayyar mijin mu? Allah ya kiyaye, to me ki ka d'auke ni? Ban cika mace ba ko me? To ba na buk'ata, nasan hayoyin da zan shawo kan miji na, ba sai wani ya taimaka min ba." Murmushi Khadija ta yi wanda har ya fito da haurun makkar ta guda biyu, Haseenah kam juyawa ta yi ta koma na ta falon ta zauna, ta na kallo Haseenah ta shigo da kwanon ta aje mata a kan teburin ta ta fice, tab'e baki ta yi tace "Ina daidai ke wallahi, sai dai duk abin da zai faru ya faru." Ba jimawa kam sai ga Usman ya shigo, kai tsaye b'angaren Khadija ya nufo da tunanin zai tarar da duka iyalin na shi anan, Khadija da ran ta ke b'ace kasa tashi ta yi ta tarbe shi kamar yanda ta saba, da gudu Bilal ya k'arasa ya rumgume shi, tare su ka k'araso wajen ta ya na fad'in "Yarima wa ya tab'a min mamanka ne haka?" Hannu ya mik'awa Khadija alamar su yi musabaha, dan in Bilal na tare da su suna kiyayewa wajen tab'a juna tun da ba k'aramin yaro bane, hannun ta ba shi lokacin da ta ke kallon Bilal da shi ma ya ke kallon ta, murya k'asa k'asa yace "Ba komai Abba." Zaune ya yi kusa da ita ya na kallon ta yace "Ba gaskiya ka fad'a ba yarima." Kallon shi ta yi tace "Sannu da zuwa." "Sannu da gida, ya kuka wuni?" "Lafiya k'alau." Ta fad'a a tak'aice, dariya ya yi ya kalli Bilal yace "Ka gani ko? Na fad'a ma ka akwai wani abu, ba haka Khadija ta ke amsa min ba." Murmushin yak'e ta yi tace "Kai ma kasan in dai ka na lafiya to mu ma mu kan kasance cikin k'oshin lafiya." D'an juyawa ya yi yace "Ina amaryar ki ne ban ganta ba?" D'an canza fuska ta yi tace "Ta na b'angaren ta mana." Mik'ewa ya yi tare da kamo hannun ta da na Bilal yace "Muje to mu ci abinci ko, dan yunwa na ke ji sosai." Fizge hannun ta ta yi tace "Kaje kawai ka ci, mu har munci abincin mu ai." Da tsantsar mamaki ya ke kallon ta, amma sam ta k'i had'a ido da shi, hannun ta ya sake kamawa su ka nufi d'akin ta ya maida k'ofar ya rufe ya juya ya na kallon ta yace " Ina jinki, fad'a min me ya faru?" Zaune ta yi akan gado tace "Ba komai." Had'e fuska ya yi yace "Khadija kar ki min k'arya, gaskiyar abin da ya faru na ke so na ji." "Nace ba komai ko, ba komai, kaje kawai ka ci abincin ka, ni da d'ana har munci." Ajiyar zuciya ya sauke ya zauna kusa da ita yace "Khadija, wannan ba d'abi'ar ki ba ce, dan Allah kar auren da na yi ya sa ki canza daga yanda na sanki, kinji ko." Shiru ta yi har sai da ya janyo ta ya na shirin kai bakin shi a nata ta yi saurin rufe bakin ta da hannun ta, wani tuhumammen kallo ya mata yace "Meye haka? Ba kya so ne?" "Eh." Ta fad'a tana mik'ewa tsaye, fizgo ta ya yi ta koma kan gadon da k'arfi, kafe ta ya yi da ido yace "Me ya sa?" Juya mi shi baya ta yi, sake juyo da ita ya yi yace "Nace me ya sa ba kya so? Sai kin fad'a min dalili na rabu da ke." Zuciya a wuya sai kawai Khadija ta fashe da kuka ta fad'a kan k'irjin shi, cikin kukan tausayi tace "Ba na so kawai, Abban Bilal ba na so ka na kusanto ni, haushin ka na ke ji
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117