Chapter 5
Chapter 5
Mariya me ye haka? Na fad'a mi ki fa za mu fita tare da su *Zeinab*, amma shine ki ka b'ata mana lokaci haka." Cikin d'aga murya tace "Ke dallah can, ke in da kinsan me ya tsaidani ma ko magana kya yi." "To me ya tsaida ke d'in?" Sai da ta aje jakar ta da bak'ar ledar hannun ta ta gyara zama da kyau tace "Kishiyar ki na had'u da ita wajen bikin." Cikin harara ta kalle ta tace "Ke aunty Mariya, ke kuma ina ki ka san kishiya ta da har ki ka gan ta wajen biki? Ko ni fa ban tab'a ganin ta a zahiri ba, bare kuma ke." Tsaki Mariya ta yi tace "Aikin banza, to tunda na ce mi ki na ganta ba sai ki tambaye ni ya akayi mu ka had'u ba." "To na ji, ya akayi ku ka had'u." *Tofa, kinga irin wannan sune yan haddasa bala'i.* 29/12/2019 Γ 13:46 - πππ: ππππππππππ *KALLON KITSE* _(Ake wa rogo)_ ππππππππππ _SAMIRA HAROUNA_ *Littatafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _D'AUKAR FANSA_ *3* _BA SO BANE_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI_ *6* _JIHADI_ *7* _K'ANGIN RAYUWA_ *8* _ITACE K'ADDARARMU_ *9* _KAWU NA NE_ *10* _MAATA_ *11* _KALLON KITSE..._ *SADAUKARWA GA* _MATAN FARKO_π§πΌ *(UWAYEN GIDA)* πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€ ```Fatan alkairi masoya``` ππππππππ _Bismillahir rahamanir rahim_ *4* Saida ta kalli maman su wacce ta ke da yak'inin za ta tsawatar mu su kafin tace "Kawai dai a gurin bikin mu ka had'u, kuma masha Allah wallahi ba ki ganta ba, kyakyawa da ita, musamman gilashin idon ta ya k'ara mata masifar kyau, gaskiya ta birgeni sosai saboda da ganin ta akwai fara'a da kuma kama jiki." Wani bak'in ciki ne ya tokare Haseenah a wuya, amma sai ta dake tace "Ni dai yanzu ki ban abin da ki ka rage wajen siyayyar." Hannu tasa a jaka da nufin fito da kud'in, hakan kuma ya yi daidai da tashin maman su ta shiga cikin d'aki, dan haka Mariya ta gyara zama murya k'asa k'asa tace "Haseenah kinsan wacece kishiyar ki kuwa?" Cikin yamutse fuska tace "Ni kuma ina zan sani." Gyara zama ta sake yi tace "Hum! Haseenah, wallahi sai kin tashi tsaye tsayin daka, dan kishiyar ki ba ta wasa ba ce, wai kinsan su wanene k'awayen ta?" Cike da jin haushi tace "To wai ni dan Allah ina zan sani, haba, ki yi magana yin za ki yi kawai." Sai da ta bubbuga k'afar ta tace "Khadija kishiyar ki, su *Hajia Turai Dubai* da *Hajia Salamatou k'urori* da *Barira nagoma* da *Hajia Natali*, sune manyan k'awayen ta, shin kinsan ma wacece aminiyar ta?" "Sai kin fad'a." Cewar Haseenah. Sai da ta sauke numfashi tace " *Hajia Kaltume*, Kaltume mai kayan dad'i." D'orawa ta yi da " Haseenah, wallahi sai kin tashi tsaye, kinga matan nan da na lissafa mi ki, gogagggun wayayyu ne, manyan mata ne ma su ji da kan su, duk kishiyoyin matan nan in fad'a mi ki ba su da daraja a wajen majazensu, kinga Kaltume mai maganin mata, to in fad'a mi ki in ba ki cika cikakkiyar mace ba ma ba ki siyan maganin ta, dan k'aramin magani a wajen Kaltume shine na *jikka hamsin* (jaka hamsin), duk wata mace da ta k'oshi kuma ta ke mulki a gidan mijin ta to Kaltume ce sirrin farin cikin ta, dan wani shegen gyaran jikin idan ta mi ki shi, to wallahi tun a daren farkon ki kin gama da mijin ki kenan, duk wata mace da za ta raba ki da shi, to sai dai fa in ta sihiri ne, amma d'and'anon ku ba ya tab'a zama d'aya a wajen shi." Gaba d'aya jikin Haseenah ne ya yi sanyi da jin wannan al'amari, ganin haka ya sa Mariya cewa "Akwai mafita d'aya da ta rage mi ki." "Wace iri?" Cewar Haseenah da saurin ta, d'orawa ta yi da "Nasan kishiyar ki a tsume take da had'in Kaltume, kuma tunda ita ce aminiyar ta kinga kenan ba za ki tab'a cin mata ba , amma abu d'aya shine, kema ki samo kud'ad'e a hannun Usee, sai kawai muje mu ga Kaltumen, sannan akwai wata ma da ke kawo min kayan mata, ita ma sai ta had'a mana da nata, koya ki ka gani?" "Hakan ma ya yi, kuma kinga dama shi mutum ne mai kyauta, ba sai ka tambaye shi ba ya ke yi." "Dan haka sai ki samo mana kud'i a hannun shi, amma fa duk da haka sai mun d'an k'ara da malamai, ko ba komai su tayaki da addu'a dan ki samu bakali a wajen shi." Tashi ta yi tsaye tace "Shikenan aunty Mariya, yanzu wannan kud'in ma ki rik'e a fara wani abun da su, yau ko gobe zan sa ya zo sai na samu kud'in, amma kar ki bari mama ta ji, kinsan halin ta yanzu sai tace ba ta yarda ba." "Ni? Ina zan fad'a mata, ba ki ga sai da ta tashi ba ma na fad'a mi ki." "To ni zan tafi su Zeinab na jira na." "Sai kun dawo." Ta fad'a ta na bin ta da kallo. *Allah ya fidda _Delu_π daga rogo.* β©β©β©β©β©β© Khadija kam a wajen bikin suna can har yamma, sai da su ka gama zubin da suke na k'awaye kafin su ka fito tare da Kaltume, motar ta su ka shiga ta bata wasu harkokin, kamar yanda ta san Khadija farin sani, ba ta anfani da kowane irin garin magani, musamman wanda za ace ayi matsi da shi, ta na sallamar ta ta fita daga motar ta rufe tace "Sai kin zo k'awata." Kaltume ce tace "A'a k'awata, gaskiya ba na so na zo gidan ki yanzu, na fi so sai an fara shagulgulan bikin nan, lokacin na k'ara had'o mi ki wasu kayan." Dariya Khadija ta yi tace "Ke fa muguwa ce, wato kullum burin ki kiga bawan Allah nan ya na gasa min aya a hannu ko? To daga wannan da na karb'a sai amarya ta zo ta haihu, idan za ta yi arba'in sai mu shirya tare." Cikin d'aga murya Kaltume tace "Ina, ana babbak'ar gwiwa wa ke jiyo k'aurin zomo, ai dole yarinya ta gane da banbanci wallahi, wanda ya sa ta shigo gidan Khadija ta Usee, shi zai sa ta gane Khadija ta mata nisa na har abada." Cikin dariya Khadija tace "Dan Allah k'awata ki ragawa yarinyar nan, har yanzu fa ba mu san ta ba bare mu san da me za ta shigo gidan ita ma." Cike da gadara da tabbatarwa tace "Ai ko ni Kaltume za ta d'aura a k'ugun ta taje dani gidan, wallahi na riga da na bawa Khadija sirrin da za ta mata rata mai tsayin gaske." "Na yarda, yanzu dai sai anjima, sai munyi waya ko?" "To ba damuwa k'awata, ina k'ara fad'a mi ki dai, dan Allah banda nuna kishi a fili, ayi komai cikin kissa k'awata, ban da matsala da ke ta wannan fannin , amma kishi masifa ne wallahi." "Hakane k'awata, kuma insha Allah zan kiyaye, nagode sosai." "To, ki kula da kan ki." "Kema haka." Da haka ita ma ta shiga ta ta motar ta bar wajen, Khadija
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117