Chapter 100
Chapter 100
ya na shafa bayan ta ya na fad'in "Kinji yanda zuciya ta kuwa ta buga lokacin da na ambaci kalmar takardar nan, dan Allah Khadija ki daina azabtar da ni haka, gaba d'aya kinsa na zama kamar mahaukaci saboda k'ok'arin ganin kin dawo gare ni, ki tausayawa uban yaran ki mana." Luf ta yi a k'irjin ta na share hawayen ta, sun jima a haka kafin yace "To ya ake ciki yanzu? Za ki koma ne ko ko sai na aiko mi ki da takardar har gida?" Wani naushi ta kai mi shi a ciki wanda ya sa shi bushewa da dariya ya dafe ciki, tashi ta yi zaune kafin ta kalle shi tace "A gaskiya ba zan iya binka ba a daren nan, kawai ka je gobe na dawo da kaina." Dariya ya yi ya kamo kunnen ta ya rad'a mata "Ashe yarinya ta na so na mata b'arin madara." Murmushi ta yi tace "Matsala ta da kai rashin kunya." "Um hakane, amma ai ke ki ka koya min." Tashi ya yi yace "Da gaske za ki dawo gobe?" "Zan dawo mana, ba ni na fad'a ba." "Idan ma ba ki dawo ba wannan karan su Hajia Kaltume da Turai zan aiko su d'auke ki su kai min ke." Kallon shi ta yi tace "Turai dai? Lallai." Tsaye ya mik'e yace "Yanzu kira min Bilal da shi zan tafi, dan nasan dole ma ki dawo idan na tafi da shi ai." Ita kam saboda ta yi niyyar komawa ya sa ta mik'e tace "Muje idan ka d'auke shi sai ka wuce." Tare suka fita daga d'akin su ka nufi d'akin Bilal, idon shi biyu ya na rik'e da wayar shi a hannu, nan ta canza mi shi kaya su ka tafi da niuyar za ta zo mi shi da sauran kayan, saida ya shiga d'akin Mama da ta jima da bacci ya tsokane ta yace ya tafiyar shi, idan ta damu da shi ta je ta yi bikon shi ita ma, saida ta rako su har k'ofar gida Bilal ya bud'e motar ya shiga, Usman na ganin haka ya damk'i Khadija da wata wawar sumbata da ta rikita su dukansu, da k'yar ya sarara mata kafin ya kalle ta da jajayen ido yace "Ki yi sauri ki zo da wuri, ina buk'atar ki kusa da ni Hajia ta." Motsa bakin da ta yi ya sa ya yi murmushi yace "Na ji dai idan kin kama ni ki yankanin amma fa bayan kin shayar da ni ruwan ki." Dungure mi shi kai ta yi tace "Wai kai ka manta da ka tsufa ne, watanni kad'an fa su ka rage ma ka ka cika shekara *arba'in da biyar* cif a duniya, amma ka na abu kamar wani tsohon bazawari." Saida ya sa hannu ya na shafar k'irjin ta yace "Kafin na cika hamsin da biyar kuma sai kun haifa min yara goma, kin ga ai ba na mayar da kai na tsoho ba, kuma ma ai ba daga nan abun yake ba, k'arfi da mazantakar na nan." Ya mata nuni da zuciyar shi. Da haka suka rabu ya tafi da Bilal, yau kam Khadija ta yi bacci cikin nutsuwa saboda burin ta ya cika, ta juya Usman son ran ta ta hakane ma har ta gano yanzun Haseenah ba ta da wani girma a idon shi, dan haka ta yi bacci da zumud'in gari ya waye ta fara shirin komawa. A wajen Usman kam Haseenah ba ta san da shigowar shi ba saboda har ta yi bacci ita ma, saida ya shinfid'e Bilal a gadon shi kafin ya wuce d'akin ta ba dan komai ba sai dan ganin halin da take ciki kamar yanda yake yi kullum, bud'a k'ofar da ya yi ne ya sa ta tashi ta na murza ido, kallon ta ya ke sosai ya na jin wata sha'awar na sake fizgar shi, sai dai kuma ba ya so ya neme ta saboda ba ita ta taso shi ba dama, da k'yar ya iya cewa "Ki yi hak'uri na tashe shi ko? Ashe hr kin kwanta ma, yau kam ban shigo da wuri ba." Gyara zama ta yi tace "Sannu da shigowa." "Yawwa sannu, ya ki ke?" Kallon shi kawai ta yi ba tace komai ba, juyawa ya yi zai fita yace "Saida safe ko, yau ma zan kwana a d'aki na saboda muna tare da yarima ne." Da mamaki tace "Yarima kuma?" Juyowa ya yi yace "Eh, Bilal ba." Wani haushi ne taji ya kamata, saukowa ta yi daga kan gadon tace "Kenan a gidan na su ka yi dare haka? Babban mutum ka na ganin abin da ka ke yi ya dace kenan? Wannan fa ba adalci bane, ka daina kula ni, ka daina min magana, ba ka cin abinci na, sannan ba ka kwana a d'aki na, me nai ma ka hakane da ka ke min irin wannan hukuncin? Ni ba wani abu bane a gare ni dan na durk'usa har k'asa na ba ka hak'uri, ka fad'a min dan Allah." Gyara tsayuwa ya yi ya na kallon ta, hak'ik'a komai gaskiya ta fad'a, sai dai baisan me zaice ba domin kuwa ba zai iya fad'a mata haka kawai ya ke jin tsanar ta ba, cikin taushin murya yace "Kinga ki yi hak'uri da duk abin da ke faruwa, kawai harkoki ne su ka d'anyi tsamari, amma insha Allahu komai ya kusan zuwa k'arshe, ki k'ara hak'uri kinji ko, saida safe." Ya fad'a ya juya kenan ta sake cewa "Shikenan ka je ka kwana da Bilal, dad'inta dai ba ya da abin da ni ke da shi, komai daren dad'ewa nasan dole ka neme ni a duk in da na ke." Juyowa ya yi ya kalle ta da mamaki yace "Da Bilal d'in za ki yi kishi? D'ana ne fa shi, kinsan mahimmancin shi a gare ni kuwa? To shi d'in kamar rayuwa ta ne, ina k'aunar sa fiye da komai, ki iya bakin ki in dai akan iyali na ne, ba na juran b'acin ran su ko kad'an." Idon ta cike da ruwa tace "Usman ba ka adalci wallahi, kullum nunawa ka ke Khadija da d'an ta sune rayuwar ka, kullum sune ma su mahimmanci a wajen ka amma ni ko oho, to kasan ba ka so na me ya sa ka aure ni?" Girgiza kai ya yi yace "Ni bance ba na son ki ba, sai dai abin da na sani kawai shine ina son iyali na, idan ki na son zama da ni ki so su kema, kuma kar ki d'auka Khadija kishiyar ki ce ki yi kishi da ita, maganar gaskiya ta wuce nan a wuri na, Bilal d'ana ne da ya fito daga jiki na tsatsona, amma ina wa mahaifiyar shi son da bana ma sa, kinsan me ya sa?" *Ita rayuwa dama haka take, da kin zauna da su lafiya da wannan ranar ba ta zo ba, kuskuren da mu mata keyi wani lokaci shine, ba ma fahimtar abin da mazajenmu suke so, idan har ki ka fahimci mijinki na bala'in son mahaifiyarsa ko yan uwansa ko yayansa, sai ke ma ki bishi ki nuna musu so na gaskiya, ba dan komai ba dan kawai ki faranta mi shi, hakan
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117