Chapter 45
Chapter 45
me zai ce ba ta fice daga d'akin gaba d'aya, kai tsaye madafa ta nufa ta samu ruwan zafi ta saka na'ana'a a ciki tare da cinta d'anya da ganyen lipton, suna dahuwa ta tace a kofi mai kyau sannan ta zuba zuma cokali biyu, ta juyo za ta fita kenan Haseenah ta shigo ciki, kallon kallo su ka yi in da Haseenah ke mamakin irin arniyar kwalliyar da Khadija ta yi kamar za ta biki, ita kuma ta na mamakin abin da ya shigo da ita madafar yanzu, har za ta fita sai kuma ta tsaya tace "Wani abu ki ke buk'ata ne?" Cike da gatsali tace "Eh, na zo na dafa indomie ne." Cike da rashin nuna damuwa Khadija tace "Ayya! Ki bari ya fito daga wanka mana sai mu ci abinci, ai yanzu ya shigo bai jima ba." "A'a nagode." Ta fad'a kai tsaye ta k'arasa shiga madafar, tab'e baki ta yi ta fita ta bar ta, ta na zuwa ta samu ya na ciki bai fito ba, cire takalmin ta yi da d'aurin d'an kwalin ta ta shiga ciki, ba tare da sanin ta shigo ba ta karb'i sabulun hannun shi ta fara goga mi shi a baya, juyowa ya yi ya na ganin ta ya fizgo ta ta fad'a jikin shi, dariya ta yi ta rufe ido saboda ruwan da suka zuba jikin ta, had'e ta ya yi sosai da jikin shi ya cire gilashin ta ya aje gefe, haka ma doguwar rigar cire ta ya yi ya jefar, a tak'aice dai tare su ka yi wankan su ka fito, da gaggawa ta d'auki kofin shayin da ta had'o mi shi ta ba shi ya shanye, cikin sauri su ka shirya su ka fito, ita tebur ta nufa shi kuma ya wuce d'akin Haseenah dan ya kira ta, ya na zuwa ya same ta ta kasa cin indomien da ta dafa saboda rashin dad'i, nan ya lallab'o ta suka fito falon a tare, cike da mamaki ta k'araso ta zauna ta na kallon Khadija ta gefen ido saboda ganin ta canza kayan jikin ta babu kwalliya a fuskar ta, a ran ta kam cewa ta yi "Hum! A nunawa shege shegentaka, wato ki nuna min wani abu ya faru har kinyi wanka, to mu zuba zuwa ni da ke." Baki Haseenah ta saki ganin abinci har kala kusan hud'u saboda kawai aci yanzu, tunda su ka fara ci take kallon Usman yanda a ke cin abincin, kenan ita ce ya raina ko? Ta tambayi kan ta, Khadija kam daga k'asa take wasa da k'afafun ta ta na shafar Usman da su har su ka kammala, saida ya ma Haseenah saida safe kafin ya dawo d'akin shi, a lokacin Khadija na d'akin ta ta na kama ruwa da ruwan kanunfarin da ta tafasa, saida ta k'ara shfa turare ta yi sassauk'an kwalliya ta saka rigar bacci, doguwar abaya ta d'ora sama sannan ta nufi d'akin. Kwance ya ke akan gado babu riga a jikin shi ya rufe ido kamar mai bacci, har ta shigo ta rufe k'ofar ta kashe hasken d'akin ta maye gurbin shi da siririn haske bai bud'a ido ba, cire rigar ta yi ta baccin ta bayyana, kallon shi ta yi har yanzu ido rufe tace " *Mon ange*, ka bud'e idon ka mana." Bud'ewa ya yi tare da sakin murmushi, ganin yar rigar dake jikin ta ya sa shi waro ido yace "Wayyo Allah, zo Khadija, zo gare ni dan Allah." Cikin salo da k'warewa ta haura kan gadon ta fad'a jikin shi, rumgume shi ta yi amma saiya k'ara matse ta sosai yace "Ki rik'e ni sosai Khadija." *To kowa dai ya san me zai faru, dan haka babu kyau shiga rayuwar ma'aurata.* Haseenah da kishi ya hanata bacci ta kasa samun sukuni, gagara bacci ta yi in da shed'an ke zugata ya na hura mata wutar k'iyayya, a k'arshe ji tayi kawai bara ta lek'a ta ji me ke faru a d'akin, cikin sand'a ta fito ta tsaya k'ofar d'akin ta na saurare, sambatu da surutan da take ji ne su ka sake d'ugunzuma mata tunani, irin yanda taji muryar Usman ya tabbatar mata da kuka ya ke tsabar dad'in abin da ya ke ji, musamman da ya ke fad'in kar ta kashe shi ta yi hak'uri ya bata komai da ya mallaka, ba ta yi bacci ba a daren ko kad'an in da masoyan kam suka kwana k'wak'ume da juna cikin farin ciki, tabbas Usman ya sake yarda aure kawai muk'addari ne daga Allah, amma ba dan haka ba babu abin da zai sa shi k'ara aure ya na da kamar Khadija, da haka asuba ta yi su ka tashi sallah. *A gurguje* Haka rayuwar gidan Usman ke tafiya da dad'i wasu lokutan kuma sai a sannu, sai dai yanzu Haseenah ta d'an shiga taitayin ta ba ta cika shiga harkar Khadija ba bare har ta fad'a mata magana, Khadija kuma dama rayuwar ta take yi babu ruwanta da ita, Bilal ma na wajen kakanin shi hankali kwance ya na zuwa islamiyyar shi, ranar talata da yamma Khadija ta saki aiki Haseenah ta kama, sosai Usman ya yarda Khadija ita ce ta san shi farin sani, bayan kwana biyu ita ma ta saki aiki a ranar alhamis ta saki aiki Khadija ta kama, a ranar kuma ta kama ranar sunan matar Issoufou, tunda rana Usman yace su tafi tare tunda Khadija na da mota, sannan ta san gidan sab'anin Haseenah da zuwan ta d'aya kuma cikin dare. Tun Khadija na jiran ta kammala aiki su tafi dan ta samu ita ma ta dawo ta kama na ta aikin har ta gaji da jira, ganin ba kowa a gidan da zata aika ya sa ta sallama da kan ta har falon ta, Haseenah da ke uwar d'aka kwance ta amsa sallamar tare da fitowa, ta na ganin Khadija ta ja birki k'ofar d'akin ta na k'are mata kallo, da mamaki Khadija ta kalle ta ganin ko wanka ma ba ta yi ba, cikin dakiya tace "Wai Haseenah ba ki shirya bane?" A kasalance ta amsa da "Ban shirya ba." Jin ba ta sake cewa komai ba ya sa tace "To dan Allah ki gaggauta ki shirya mu wuce, wallahi ba dan ke ba ma ni ban tab'a kai wannan lokacin ba ban fita ba, musamman da nasan zanyi aiki." "To." Haseenah ta fad'a ta juya kawai ta koma ciki, Khadija na ganin haka ta fito ta na mita, a k'alla ta sake b'ata minti talatin ba Haseenah ba labarin ta, ran ta ne ya kai matuk'a wajen b'aci kawai ta d'auki jakar ta ta fita, Haseenah na jin fitar Khadija ta fito ta rufe d'aki dan dama ta shirya tunda ta mata magana, kawai ba ta yi ra'ayin fitowa da wuri bane, har farfajiyar gidan ta fito ta samu mai gadi tace "Wai har ta tafi ne?" Cikin girmamawa yace "Yanzun nan kam ta fita, dan ga motar can ko titi ba ta hau ba." Wayar ta ta ciro cikin jaka ta dannawa Usman kira, ya na d'auka ta fad'a mi shi ya zo ya d'auke ta Khadija ta tafiyar ta, da mamaki yace "Wai dama har yanzu ba ki
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117