Chapter 60
Chapter 60
had'e, bud'e ido ya yi ya sauke akan Khadija da ke shirin kai loma a bakin ta, shiru ya yi ya na kallon kowa har suka kai bakin su suma, kasa had'ewa su ka yi suka furzar dan haka Khadija ta d'ago ta kalli Haseenah, murmushi ta mata cike da makirci tace "Ramawa ki ka yi kenan?" Zazzare ido Haseenah ta yi ta kalli Usman da ya kafe ta da ido ya na kallo, cikin in'i'na tace "... *Maganin biri karen maguzawa, waya fad'a mi ki barno gabas take.* 12/02/2020 Γ 21:57 - πππ: ππππππππππ *KALLON KITSE* _(Ake wa rogo)_ ππππππππππ _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _D'AUKAR FANSA_ *3* _BA SO BANE_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI_ *6* _JIHADI_ *7* _K'ANGIN RAYUWA_ *8* _ITACE K'ADDARARMU_ *9* _KAWU NA NE_ *10* _MAATA_ *11* _KALLON KITSE..._ *SADAUKARWA GA* _MATAN FARKO_ π§πΌ *(UWAYEN GIDA)* πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€ ```Fatan alkairi masoya``` _Bismillahir rahamanir rahim_ *23* "Wallahi ba ni bace, babu abin da na saka a abincin nan." Had'e fuska Khadija ta yi tace "Kinga Haseenah, ni da ke yanzu duk d'aya ne, tunda kin rama to komai ya wuce, kin fahimta." Cikin b'acin rai Usman yace "Yanzu miye haka? Me ku ke son mayar da ni to? Ke koma miye ai laifin ki ne tunda ke ki ka fara, ki na babba amma ko tsaya d'aukar raini ga k'aramar k'anwar ki, mtssss." Tsaye ta mik'e ta na kallon shi tace "Dakata Abban Bilal, ni nafi k'arfin na tsaya jawa kai na raini wajen wannan mutsitsiyar yarinyar, gata ka tambaye ta tsakani da Allah uban waye ya fara zuba gishiri ko sugar a abinci? Ita ce da kan ta, har ni za ta wa makirci, saboda ta baka ka kurb'a shine za ta dinga ja min magana a wajen ka ta hanyar lalata abincin da ta girka, me ta ke nufi da hakan? Tasan dole ni za'a zarga dama ba ita ba, shine ni ma na nuna mata mace ce ni kuma gaba na ke da ita ko a haihuwa." Zata fice ya mik'e tsaye yace "Dawo nan." Dawowa ta yi ta tsaya sai Haseenah da ta mik'e ta kalle shi tace "Wallahi k'arya ta ke min babu abin da na saka, kawai sharri ne ta ke so ta ja min, taya ma zan lalata abin da na girka da hannu na?" Kusanta Khadija ta matso cikin b'acin rai ta nuna ta da hannu tace "Wallahi ki ka sake cewa ina mi ki k'arya sai na fitar mi ki da jini a baki, marar kunya kawai fitsararriya, ke har ni za ki kalla ki ce ina mi ki k'arya? Wace ce ke dan Allah da zan mi ki k'arya?" Usman ma matsowa ya yi yace "Ta fad'a d'in k'arya ne, ko k'aryar ta mi ki ne ba ki aikata ba? To gata nan ki fitar mata jinin dan Allah, wallahi da na gaggauta d'aukar mataki a kan ki, kiji mace kai ki yi laifi kuma ki ce ba za'a mi ki magana ba, ke wace ce?" Cikin tafasar zuci ta kalle shi tace "Ni ce ma macen? To ta mace maka k'ofar d'aki, kuma na fad'a wallahi ta sake cewa na mata k'arya sai na kife ta da mari kuma a gaban ka." Ai fa abu ya yi k'amari, sai kawai Usman ya jawo Haseenah da k'arfi ya dawo da ita gaban Khadija yace "Ke fad'a mata ta yi k'arya na ga me za ta yi, kiji iskanci kai ki yi laifi kuma ki ce ba za'a mi ki magana ba, wacece ke da ki ka fi k'arfin a mi ki magana?" Idon ta ne suka rufe ta kalli Haseenah tace "Ki fad'a idan ke yar halak ce." Haseenah ta tabbatar babu abin da zai hana Khadija ta dake ta, dan haka ta koma gefen Usman ta na fad'in "Abban Bilal kaga, ni fa ba na son matsala, laifi ne ta aika ta kuma na yafe, dan haka kawai abar..." Ba ta k'arasa maganar ba Khadija ta kife ta da mari, cikin hargagi ta shak'o wuyan ta tana fad'in "Wa ki ka yafewa? Ni wai ki ke cewa kin yafe wa? To bari ki gani idan na ci uban ki gobe ko kud'i aka baki ba za ki sake shiga harka ta ba." Tuni Khadija ta yi fatali da ita a k'asa warwas, sosai ta shak'e wuyanta ta na jijjigata ta na fad'in "Za ki sake shiga harka ta, daga yau za ki sake rai na ni?" Duk abin nan da ake Usman na ta k'ok'arin raba su amma Khadija ta rik'e ta sosai, saida ya sa k'arfi sosai ya rumgumo Khadija ya d'aga ta daga jikin Haseenah, jefar da ita ya yi gefe in da ya kaiwa Haseenah d'auki ya kamota ta tashi, kallonta ya ke duk ta fita hayyacinta ido sunyi waje saboda wahala, ganin haka ne ya sa Usman juyowa cikin b'acin rai ya kashe Khadija da mari, gilashin ta ne ya k'arasa fita ya fad'i, dafe kunci ta yi ta d'ago ta kalle shi, cikin tsananin hushi ya nuna ta da hannu yace "Wallahi yau sai kin tafi gidan ku, ba zan d'auki wannan iskancin ba, haka kawai saboda kifi yarinya k'arfi sai ki dinga mata cin kashin da ki ka ga dama, to ba zai yiwu ba, kawai kije gida sai na nemi ki." Za ta yi magana Bilal ya sakaya hannun shi ta k'ugun ta ya na kallon Usman da ke rarrashin Haseenah ya nufi d'akin shi da ita, Bilal kam hannun ta ya kama yace "Mummy ki zo mu tafi, mu tafi gidan su Hajia kawai." Sunkuyawa ya yi ya d'auko mata gilashin ta ya d'aga hannayen shi da nufin saka mata, b'acin rai ne ya saka ta fizgar gilashin ta karya shi gida biyu ta jefar, hanya ta kama da nufin komawa d'akin ta amma sai ta yi karo da kujera, hannun ta Bilal ya kama bai saki ba har saida ya kai ta d'akin ta, su na Bilal ya sake d'auko mata wani gilashin ya saka mata kafin yace "Mummy, meya sa Abba ya daina son ki yanzu?" Kallon shi kawai ta yi ta mik'e ta d'auko akwatin ta ta zuba kaya, d'akin Bilal ta koma can ma ta had'o mi shi kayan shi kafin ta saka mayafi ta d'auki jakunkunan suka nufi k'ofar fita, a lokacin Haseenah ma sai kuka take ita wallahi gidan su za ta tafi kafin Khadija ta kashe ta, hakan ya sa lokacin da suka iso falon shi suka hangi Khadija da Bilal za su fita, da hanzari ya fito ya tare ta yace "Bilal d'ana ne, kuma ba da shi ki ka zo gidan nan ba, dan haka ki bar min yaro na." Fuska a had'e tace "Ni ma zan tafi da shi ne saboda ko da na zo gidan tare na same ku." Duk ya gane magana ce ta fad'a mi shi amma haka ya fizgo Bilal yace "Yana nan tare da ni, idan kuma da wanda ya isa ki aiko shi ya k'watar mi ki shi na gani." Tab'e baki ta yi tace "Hum! Wa ma zan aiko ya k'watar min shi? Ai sai marar kunya irin
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117