Skip to content

Chapter 16

Chapter 16

Kallon Kitse Book One Complete Hausa Novels 1,198 words 0 views Progress saved
Download Book

ku panke) saida ta bi duka yan uwanta biyar ta saka mu su a baki kafin k'awar ta *Kaltume* da *Salamatu*, haka aka gama shagali aka yi murna sosai aka watse. *Komai na da mafari a rayuwa*, matar Ashir da Bashir da mama sun gama waina, sai dai babu mai kaiwa, Habib kad'ai ke gari kuma shi ma ya na wajen d'aurin auren abokin shi a wani k'auye *Dak'oro*, hakan ne ya tilasta mama cewa Khadija ta shirya sai ta kai a kan moton ta, shiryawa ta yi tare da Kaltume da su ke kusa da juna suka tafi, Kaltume ita ke rik'e da kwanukan abincin a baya, sun isa lafiya su ka kai abincin, cikin ladabi su ka gaishe da dattawan, da kansu su ka wanke babban faranti suka zuba mu su wainar sannan suka d'aure kwanukan su ka mu su sallama, kasancewar akwai rairai kafin su hau titi ya sa Kaltume ba ta hau ba ta na jiran Khadija ta fita daga rairain, cikin rashin sa'a wani tsoho ya taho zai shiga shagon d'inkin shi, tana murd'awa sai kuwa ta bige tsoho ya fad'i, dukan su suka fad'i k'asa da azama aka kawo mu su d'auki, duk da masuburbud'ar zafi (shagama inji salim, salansa inji mak'obtanmu) ta tab'a ba bai dame ta ba, tsohon mutane data bige shine a gabanta, kuka take ta na tambayar tsohon bai ji ciwo ba, duk da k'afar shi da ta buga yaji ta na masa ciwo haka ma gwiwar hannun shi daya fad'a samanta, amma sai ya nuna ba komai kawai ta tafi, cikin abokan mahaifin nata ne ya lura da hannun shi har jini ya d'an fara fitowa ta cikin riga, nan aka ce a kai shi likita Khadija tace ita ma za ta je, da k'yar suka lallab'a ta dan ta tafi gida, amma duk ta d'aga hankalinta sosai sai hawaye take, wani daga cikin dattawan ne yace "Kinga Khadija ki daina kuka, zai samu sauk'i, kinga ciwon ai kad'an ne, Allah ne ya aiko dole hakan ta faru, yanzu kije gida ki huta, zuwa gobe sai kije godanshi ki dubo shi ko, hakan ya yi?" D'aga kai ta yi alamar eh, sai da ta hau moton Kaltume ma ta hau sannan tace "Ina ne gidan?" "Gidan ya na nan yan banana wajen masallacin ladan." Ta na shan majina ta wuce zuciyar ta ba dad'i ko kad'an, tun da suka je gida daf da magrib sun samu duk yan uwan ta sun dawo daga uzurirrikansu ban da Naseer dake karatu a *France*, yanda ta shigo tana kumboro baki ta na murzar ido ta cire gilashi ne ya sa Ashir zaburowa ya kamo hannun ta yana fad'in "Auta lafiya? Me ya same ki kike kuka?" Zaunar da ita ya yi ya karb'i gilashin ya maida mata ya kalli Kaltume yace "Umma waya tab'a ta?" Cikin taushin murya Kaltume tace "Wani tsoho ta bige, ita ma kuma ta fad'i, amma duk ta damu." Bashir da Mansur a zabure suka matso Bashir na fad'in "Subhanallah, auta ba ki ji ciwo ba?" Dukansu duba jikin ta suke ko sunga ciwo amma shiru, Mama na gefe tana kallonsu ta yi shiru, a hankali Khadija ta janye siket d'in ta ta nuna musu in da take jin zafi, wajen har ya yi bak'i ai sai suka zabura da ganin wannan d'an ciwo, da gudu Habeeb ya wuce d'akin shi ya d'auko maclean dan a shafa mata, tuni kuma Bashir da Ashir sun umarci matansu da su d'auko musu suma, sai ga abun wanke hak'ora har hud'u a gaban su, nan dai suka shafa mata akayita lallab'a ta har zuwa dare. Kwance take a d'akin ta cikin bargo yayin da suk yan uwan ke kewaye da ita sai kanta dake kan k'afafun mama, d'aya hannunta na sak'ale cikin hannun Habeeb ya na shafawa, sai mama dake shafar kanta Ashir kuma na karanta mata wani littafi mai sunan *magana jari*, lumshe ido take sosai ta na so tayi bacci, janyo hannun ta tayi daga hannun Habeeb ta tusa shi ta k'asan gilashinta ta murza idon ta tana turo baki gaba, ganin ta rufe ido ya sa Ashir matsowa kusan fuskarta yace "Auta." Bud'a ido ta yi ta kalle shi, cikin murya k'asa k'asa yace "Albishirinki." "Goro." Ta fad'a ta lumshe ido, d'orawa ya yi da "Na biya mi ki kujerar hajj, tare da Mama za ku tafi wannan karan insha Allah." Zunbur ta tashi zaune tace "Da gaske yah Ashir? Kai amma naji dad'i sosai, nagode." Da k'arfi mama ta maida kanta akan cinyar ta tace "Dan Allah ki kwanta ki yi bacci ko muma mun samu mu rintsa." Daddab'a ta ta ci gaba da yi har bacci ya d'auke ta, addu'a mama ta shafa mata Mansur ya cire mata gilashin ya aje mata gefenta kafin suka kashe mata wutar d'akin suka fita, har ga Allah wannan kulawar da suke nuna mata Mama tasan ta yi yawa, haka kuma matar Bashir da Ashir suna jin haushin hakan, saboda kai tsaye suna nuna musu farin cikinta yafi nasu, kulawar da suke nuna mata basa nuna musu kwatankwacin ta, shi ya sa mama ke fatan su rage ko dan kasancewar ta ya mace, dan ma ita d'in yarinya ce mai son aiki da kazar-kazar. *Allah ka k'ara mana k'oshin lafiya, sis Alawiyya Allah ya baki lafiya.* 12/01/2020 Γ  22:18 - πŸ’‹πŸ˜˜πŸ’‹: πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘ *KALLON KITSE* _(Ake wa rogo)_ πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘ _SAMIRA HAROUNA_ *Littatafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _D'AUKAR FANSA_ *3* _BA SO BANE_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI_ *6* _JIHADI_ *7* _K'ANGIN RAYUWA_ *8* _ITACE K'ADDARARMU_ *9* _KAWU NA NE_ *10* _MAATA_ *11* _KALLON KITSE..._ *SADAUKARWA GA* _MATAN FARKO_πŸ§•πŸΌ *(UWAYEN GIDA)* πŸ‡ΈπŸ‡¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_πŸ€œπŸ€› ```Fatan alkairi masoya``` _Bismillahir rahamanir rahim_ *10* Washe gari da safe Khadija ta shirya su ka tafi tare da Habeeb ya kai ta gidan tsohon da ta bige, sai da aka mu su kwatance su ka isa gidan, a k'ofar gidan Habeeb ya tsaya ita ta wuce ciki ta na rabka sallama tun daga soro, kasancewar safiya ce kusan matasan gidan ba su riga sun tafi harkokinsu ba, dan wasu ma su na cin d'umamen tuwo ta same su, izini aka mata ta shiga ciki, gaba d'aya ta had'e tace "Ina kwanan ku." "Lafiya k'alau." Aka amsa mata, d'orawa ta yi da "Antashi lafiya." "Lafiya lau mu ka tashi." "Ya mai jiki?" Ta fad'a ta na d'an kallon tsohuwar, da fara'a tsohuwar tace "Mai jiki da dama." Da mamaki tsohuwar ta kalleta a nutse tace "Sannu ko yan mata?" "Sannu Mama." Ta fad'a da murmushin ta, tsohuwar ce tace " Sai dai kuma ban shaida ki, gashi na ji har ki na tambayar jikin malam ko?" Da k'ayataccen murmushi tace "Eh mama, na zo duba jikin su ne, ba za ku shaida ni ba dama, ni ce hatsarin nan ya faru tare da ita." "Ayyah! Sannu ko, mai jiki ai da sauk'i, yanzu ma haka fitowa ya yi zai fita shago, babban yaron na shi ne ya hana shi yace ya koma ya kwanta, ya na ciki, muje na rakaki ki gan shi." Ledar hannunta ta sake mayar da ita d'aya hannun saboda nauyin ta kafin ta wuce, ta

Table of Contents

Chapters

117 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117