Chapter 81
Chapter 81
wannan baiwar da ka min, Allah ka tabbatar min da alkairi." Saukowa ta yi daga kan gadon ta shiga wanka, da sauri ta k'arasa ta fito ta saka kaya ta yi sallah, gyalen ta ta saka ta d'auki jaka tasa takalma ta fito, da kallo Mama ta biyota tace "Ke kuma ina zuwa haka da rana patsal-patsal haka?" Kasancewar duk matan gidan na d'akin ya sa ta matsa kusan amaryar Ashir tace "Duk cikin nan ke ce babba, dan haka ke ce zan iya fad'awa dan ba na jin kunyar ki." Rad'a ta mata a kunne kafin ta fice daga d'akin da sauri, dariya amaryar Ashir ta yi ta kalli Mama tace "Mama wai kinsan me?" "Sai kin fad'a mana zan sani." Cewar Mama, saida ta jinjina kai tace "Ai Mama sai kin bani goron albishir kafin na fad'a." "Ita goron ki ka bata kafin ta fad'a mi ki? Ai naga kyauta ta fad'a mi ki." Dariya matar Bashir ta yi tace "To ai Mama shugaban k'asa ya hana aikin banza." Tab'e baki Mama ta yi tace "To can ku k'arata ku da shugaban k'asar na ku, ku rik'e sirrin ku ba na son ji." Dariya amaryar Ashir ta yi tace "Mama Khadija fa cewa ta yi ta na zargin ta na da juna biyu, yanzu ma za ta je asibiti ne a tabbatar mata da gaskiya." Waro ido Mama ta yi tace "Ke *Safiya* ba na son k'arya, da gaske ki ke?" "Wallahi kuwa Mama haka ta fad'a." Wani murmushin farin ciki Mama ta yi kafin tace "Allah ya tabbatar da alkairi, *wani hanin ga Allah baiwa ne*." "Hakane Mama." Suka amsa da shi. Khadija na fita cikin sauk'i ta samu adaidaita sahu ta kai ta *Clinique tattali*, kamar yanda ta yi tunanin kam hakane ta faru, dan kuwa ta samu k'awar ta ce akan aiki mai sunan *Maryama*, kasancewar babu mutane a asibitin ya sa suka fara tab'a hira kafin ta fad'a mata abin da ya kawo ta, nan ma saida aka sha wata hirar kafin ta mata gwajin fitsari, ko da ta duba dan ta ga sakamakon Khadija tace"Dakata." Kallon ta ta yi ita kuma tace "Kawai ki min murmushi idan har gaskiya ne tunani na, in kuma babu to ki had'e rai." Dariya Maryama ta yi tace"Kaga wani sabon gwajin ciki kuma, to bara na gani." Ta na dubawa kam ta ga ciki dai ya tabbata, haba wa ai sai ta washe mata hak'ora tace "Ke kiyi farin ciki, wallahi ciki ya tabbata, kai Khadija na miki murna wallahi." Rumgume juna su ka yi cikin farin ciki, ba ta jima ba ta mata sallama ta bar asibitin, daga nan kuma gidan k'awar ta ta wuce Kaltume dan sanar da ita, da shigarta gidan ta ji sun k'ara birge ta abun sha'awa, dan farko *Madina* kishiyar Kaltume ta so ita ma ta yi kalar nata iskancin, sai dai ina tuni Kaltume ta nuna mata ruwa ba sa'an kwando bane, sannan shi kan shi mijin na su *Alhaji Ibrahim* yasan da ya fad'a tarkon Kaltume da babu mai k'watar shi idan ba ubangiji shi ba, a k'arshe dai Madina ta fahimci tazara mai tsayi ce tsakanin su da ita dole ta hak'ura, musamman da ya zama babu mai iya bata shawara ga yanda za ta mu'amulanci rayuwar gidan ta, cikin sauk'i sai suka zauna lafiya kamar ba kishiyoyi ba, yanzun ma saida suka gaisa sosai ita da Khadija har suka fara tab'a hira kafin Kaltume tace su je daga ciki, nan fa ta fad'a mata ta na da ciki kar kuso suji bud'ar da Kaltume ta rabka har k'ofar gida, tsabar nuna farin cikin ta ya sa nan take ta bawa yara kud'i tace su siyo alawa mai tsada su rabawa yara, anjima kuma da yamma za ta yi fanke na sadaka da godiya ga Allah, Khadija dai kallonta kawai tale ta na k'ara k'aunar Kaltume, tabbas a rayuwa bata da yar uwa mace amma Kaltume ta zame mata komai, har kusan yamma kafin ta bar gidan saboda kiran ta da Mama ta yi, haka ta koma gida nan ma Mama da aka k'ara tabbatar mata gaba d'aya gida ya d'auka Bilal zai samu k'ane ko k'anwa, in da Mama ke binshi da gwalo ta na fad'in "Tuzurun wofi, yanzu dai sai naga k'afafun uban wa za ka hawa ko kuma wanda zaka wa shagwab'a, dama can rashin ganin wani ne a gaban ka ya sa ka wannan iskancin." Shi kam cewa ya ke to sai me, ai k'ane za'a mi shi dan haka bai damu ba, kuma idan ya na son hawan k'afafu ga nata nan zai hau, da haka har 'yan biyar su ka zo suma suka d'ora nasu farin cikin ana addu'ar Allah ya sauketa lafiya. *Mu ma dai munce ameen.* Kamar kullum Usman ya je gaishe da iyayen sa, kuma kamar yanda ya saba riska yau ma malam baya nan, sai dai ya bar sak'on wannan ruwan addu'ar a bashi ya sha, saida ya shanye Hajia ta fito daga ban d'aki tace "Tashi kaje ka yi wanka ruwa na nan na had'a ma ka." Kasa magana ya yi saboda mamaki da kuma rashin sanin abin da zai fad'a, saida ta maimaita da "Ko ba ka ji ba ina magana?" Saida ya gyara zama ya kalli jikin shi da kyau yace "Amma Hajia na yi wanka fa, wane irin wanka ne zanyi yanzu kuma?" "Ka tashi ka shiga lokaci tafiya yake." Marairaicewa ya sake yi yace "Amma Hajia wai dan..." Katse shi ta yi da "In za ka tashi ka tashi kafin ka b'ata min rai." Tashi ya yi kamar zai k'urma ihu saboda haushi, ya rasa irin wannan sabon al'amari na iyayen shi, haka ya tub'e kayan da ya sanyo yanzun ya yi wanka da wannan hakukuwan na magani, haka ya sanyo kayan ya fito duk ruwan jikin shi sun tsaya a kayan, ya na fitowa Hajia kuma ta bashi damammiyar fura da maganin jiya a ciki, saida ta masa jan ido yasha dan cewa ya yi jiya baiyi bacci ba, hakan ya sa ta bud'e mi shi ido sosai sannan ya sha, wata 'yar kwalba ta d'auko bak'a mai d'auke da maganin *jibda* a ciki, da kan ta ta lak'ato a hannu ta shafa mi shi a wuya zuwa kai da hannuwan shi har zuwa damatsenshi, bashi ta yi tace ya d'iba ya shafa a cikin shi har zuwa k'irji, kamar zaiyi kuka ya kalle ta yace "Hajia wai duk wannan na miye haka? Wannan abun nan amai zai saka ni, sam warin shi babu dad'i." Shiru kawai ta yi ba tace komai ba dole ya shafa yanda take so, mik'ewa ya yi yace "Hajia ko za ki bani magungunan sai ki nuna min yanda ake sha, ina ga kamar hakan zaifi ko?" Kallon shi ta yi tace "Alhaji, kai ka haife ni ko ni na haife ka?" Cike da ladabi ya rusuna yace "A'a Hajia ki yi hak'uri, ban fad'i haka dan b'ata ran ki ba." "To ka wuce ka tafi in da za ka je kawai, sannan ba na so ka fad'a wa wani ko wata batun magungunan nan, ko da kuwa matan ka ne ban yarda ba, kaji ni ko?"
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117