Skip to content

Chapter 84

Chapter 84

Kallon Kitse Book One Complete Hausa Novels 1,201 words 0 views Progress saved
Download Book

ke kallo ka ke fad'a ma haka? Ko dan ka na ganin a waya ne shine ya ba ka damar fad'a min abin da ka ga dama? Lallai wuyan ka ya isa yanka Nura, har ni za ka bud'a baki ka aibata matata a gaba na a dodon kunnuwa na, to nagode, kuma ka yi hak'uri idan ran ka ya b'ace saboda kiran da na ma ka, ni dama ba aikin ka zanyi ba, na ce ka zo ne dan na baka kud'in da za ka fara shirye-shiryen bikin ka tunda an riga da an gama magana, amma tunda har ka ci mutuncin matata a gaba na ba tare da fargaba ba, to na fasa sai ka je ka samu malam saiya ma ka komai, ko kuma ka je ka fad'awa wacce ta sanya aka nemo ma ka auren ka ga saita d'auki nauyin komai." Ya na fad'a ya kashe wayar ya jefa kan kujera, zaune ta yi ta na kallon shi tace "Ya dai babban mutum na ji ka na waya haka kamar ka na fad'a? Kai da wa ne haka?" Cikin fusata yace "Ni da wannan banzan Nura fa, wai har ni zai kalli tsabar ido na ya na fad'a min magana har ya na ci mi ki mutunci, amma ba laifin shi bane laifi na ne da na sakar mu su fuska har su ke samun damar fad'a min abin da duk ya fito bakin su." Cikin ladabi tace "To me yace ma ka?" "Ki barshi kawai, ban san tunawa." Matsowa ta yi kusa da shi ta b'alle mab'allin rigar shi ta sa hannu ta na shafa k'irjin shi ta na fad'in "Na fi ka sanin cewa yan uwan ka ba sa so na, musamman yanzu da aunty Khadija ba ta gidan nan, wallahi gaba d'aya haushi na suke ji, gani su ke kawai laifi na ne ni ce silar barin ta gidan, amma ka sani ba zan tab'a damuwa da hakan ba in dai har ka na tare da ni." Rumgume ta ya yi yace "Kar ki damu Mummyn beby, babu abin da zai raba ni da ke saboda ina bala'in son ki sosai." Nura kam shi ma cikin hushi ya aje wayar shi ya ci gaba da aikin da ke gaban shi ya na balbala masifa shima, bai damu ba dan yace ba zai bashi gudummuwa ba, dan dama a shirye ya ke kafin ma ya fara maganar auren, dan haka ya yi niyyar yi wa kan shi komai ba tare da jiran taimakon wani ba, sunyi mai wuyar tunda sun nemo mi shi auren. Har ya gama abin da ya ke ya dawo gida kowa bai fad'awa abin da ya faru ba, dan Nura mutum ne mai zuciya da kuma rik'o sosai, wannan abun da ya faru ko da an yafi juna zaiyi wuya ya d'ora idon shi akan Usman ba tare da ya tuna wannan ranar ba, uwa uba kuma Haseenah da ya ke da tabbacin ita ce silar faruwar komai, har ya yi wanka ya ci abinci zai fita Hajia tace "Wai kai ya ku ka yi da Fodio da ka je gidan?" Fuska a had'e yace "Ba komai Hajia, dama wani sak'o ne zai bani na kai wani wurin." "To ai ni na d'auka ko maganar auren ta ka ce za ku tattauna." Hanyar fita ya nufa ya na fad'in "A'a ba ita bace." Har ya kusa kaiwa k'ofar fita ta sake cewa "Zo ka kira min shi a waya, ni tun yamma na ke kira ba na gane me ake fad'a, kuma har yanzu bai shigo gidan ba har dare ya yi." Dawowa ya yi ya karb'i wayar ya danna kiran lambar Usman ba tare da yace komai ba, wayar na k'ara a lokacin amma ba'a d'auka ba. Manne suke da juna basu rabu ba, sai dai ta samo mu su abu su tab'a kawai su yi sallah idan lokacin ya yi, mai gadi bawan Allah sam sun ma manta da a al'amarin shi bare a aika mi shi da abinci, sai dai ya siyo kawai ya ci amma ran shi bai mi shi dad'i ba, a haka har dare ya riske su Usman sai amsa waya ya ke musamman abokan shi na rashin ganin shi yau da ba ayi ba a waje, wani ikon Allah kuma saida su ka yi shirin kwanciya sai ciwon mara ya hana Haseenah sukuni, cikin rud'ewa ya d'auke ta su ka nufi asibitin da aka fara duba ta tun farkon rashin lafiyar ta, suna gaban likita lokacin kiran Hajia ya shigo wayar shi, kasa d'auka ya yi ya mayar da hankali kan abin da likitan ke fad'a cewa ta daina duk wani aikin wahala, in fa ba haka ba zata iya yin b'arin cikin nan, haka aka sallamo su suka dawo aka ce ta ci gaba da shan magungunan da aka bata na farko, tun cikin mota yake fad'in "Wallahi ba za ki k'ara dafa ko ruwan zafi ba a gidan nan, ke baki san yanda na ke son abin da ke cikin nan naki ba, amma bari cikin ki ya k'ara k'wari wallahi k'asar waje zan fita da ke ki haihu acan, dan ni ban ma gamsu da likitocin nan d'in ba, daga yanzu kuma zuwa lokacin zan samo mi ki yar aiki ko kuma Aziza ta dawo nan ta dinga aikin gidan." Ita dai ta na sauraren shi dafe da marar ta har suka isa gida, da kan shi ya canza mata kaya ya kwantar da ita ya bata magani tasha sannan ya rufe ta da zanin rufa, k'ura mata ido ya yi ya na kallo har bacci ya d'auke ta, wani bala'in tausayinta da kuma son ta ne ke k'ara gyauraya da jinin shi, ta yanda yake jin kamar ya mayar da cikin jikin shi saboda ta samu sauk'i, ya jima zaune kafin ya fito da wayar shi ya ga kiran Hajia, fita ya yi falo ya sake maida kira cikin sa'a kuma Hajia ta d'auka, a d'an kakkauce suka gaisa kafin ta tambaye shi ya yi aiki da magungunan nan, "Sosai ma Hajia, ai duk na yi aikin da su." Cewar Usman fa, tambayar shi ta kuma yi me ya hana shi zuwa yau? Malam ma ya bayar da ruwan addu'a a abashi amma bai zo ba, haka kawai ya tsinci kanshi ya sharara k'arya ta hanyar fad'i "Hajia ai wani abu ne ya d'an taso da ya sa dole sai da na je *katsina*, kuma sai bayan isha'i na dawo ina zuwa na gaji sosai kawai na d'an kwanta, yanzu ma ina bacci ne na farka sai kuma na ga kiran ku." Cike da gamsuwa Hajia tace "Ah to shikenan, saida safe, Allah hutar da gajiya." "Ameen Hajia, nagode, saida safen ku." Ya na fad'a ya kashe wayar ya shiga uwar d'akin shi ya canza kaya kafin ya dawo d'akin Haseenah. Washe gari da safe kafin malam ya fita saida ya sake bayar da ruwan addu'a, Hajia dai ba ta ma fad'a mi shi na jiya na nan ba kawai ta amsa, sai kuma akayi sa'a Usman ya zo gidan, shi ma kuma ya zo ne da maganar Aziza ta koma can da zama ta na taya ta aiki,

Table of Contents

Chapters

117 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117