Chapter 111
Chapter 111
baya na ke fargaba da shakkun fad'a mi ki, ki yi hak'uri ko da hakan zai b'ata mi ki rai, kinga Khadija da ki ke gani?" Ya fad'a ya na nuna Khadija dake gefen shi, Haseenah dai ta baza kunne ta na saurare, d'orawa da "Ba iya matata ba ce kad'ai, rayuwa ta ce, kuma kin dawo gidan nan ne a dalilin ta, ita ta dage har saida ta ga kin dawo gidan nan, ke na tak'aice mi ki ma har saida ta kai munyi fad'a da ita ko magana ba ma yi saboda ke kawai, Haseenah dan Allah ki tsarkake zuciyarki ku zauna lafiya, Allah kuma ya bani ikon yin adalci a tsakanin ku." Khadija ce tace "Ameen mijin mu, Abban Bilal da kuma k'annan shi ma su zuwa, mun yarda ka ci gaba da jagorancin mu har zuwa gidan aljanna, mu na da yak'inin ba za mu tab'a yin nadama saboda kai *adalin miji* ne da mu ka yi sa'ar samun shi a wannan zamanin." Fuskar nan ta Usman kamar gonar audiga haka yake mata murmushi, saida ta kai aya yace "Allah yasa matata, Allah kuma ya sa ba zigani ki ke yi ba dan naga ki na neman fasa min kai." Dariya ta yi sosai ta mi shi fari da ido tace "A haba dai alaji, ai kasan ba ma haka da kai, duk abin da zai fito daga baki na akan ka gaskiya ne, saima saya wani abun da na ke saboda tsaro." Kashe mata ido ya yi ita ma kuma haka, Haseenah ta saki baki ta na kallon su, wani zafi taji ya na taso mata a zuciya tare da jin mugun kishi, amma a take ta lumshe ido ta furta a ranta "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un, Allah kasa na fi k'arfin zuciya ta." Ta na bud'a ido ta kalle su sai taji sanyi tare da jin sauk'in abin da ke ran ta, murmushi ta yi ta na ci gaba da kallon su ta ayyana a ranta in har ta na son zama da Usman dole ta girmama matar shi, sannan ya zama dole ta iya zama da su ta durmiya cikin rayuwar da suke, da k'yar ta mik'e tsaye saboda nauyin da ta yi tace "To sarakan soyayya, ni zan shiga na kwanta, kunsa fa na yi kewar gado na." Ba Khadija ba har Usman saida ya dara kafin yace "Kenan rayuwar gida babu dad'i ko?" Turo baki ta d'anyi tace "Babu kam." Jingina ya yi a kujera yace "Dan haka sai kowace ta kama kanta ta, in ba haka ba zan dinga yanka mu ku kati ne ku na tafiya gida ku na hutu." Kallon shi Khadija ta yi ta kalli Haseenah tace "Idan mutum ya shirya siyan abinci da kwanan kad'aici to ai ko yanzu a shirye muke, dan idan zamu shekara gida ma kaga lafiya lau mu ke kum hankali kwance." Haseenah ce ta juy tace "Saida safen ku aunty." Da murmushi tace "Allah tashe mu lafiya." Mik'ewa Usman ya yi yace "Bara na raka ki mai ciki, kar ki je ki zame." Hannun ta ya kama har suk isa falon ta, suna shiga ya saki hannunta har ta shiga uwar d'aka ta kwanta, juyawa ya yi zai fita yace "Ina zuwa." D'akin Khadija ya je ya mata saida safe kafin ya koma d'akin Haseenah, sam bai wani sakar mata fuska ba har bacci ya d'auke su, dan har ga Allah har yanzu ya na jin haushin ta idan ya tuna baya, kawai babu yanda zaiyi ne Khadija ta tilasta mata ya dawo da ita, kuma tunda ya dawo da ita dole ya sauke hakk'ok'in ta ko kuma ya had'u da fushin ubangiji, Haseenah kuma sam ba ta yi bacci ba saboda sabon ciwon bayan da ya taso mata, tun tana shiru ta na addu'a har ta daddab'a Usman ya farka, nan fa ya rikice saboda ba'a tab'a nak'uda a gaban shi ba, haihuwar Bilal ma baya garin, Khadija ya taso daga bacci ta taimaka mi shi, kayan haihuwar Haseenah na gida ba'a d'auko ba sai Khadija ce ta d'auko nata su ka tafi asibiti da su, saida aka karb'e ta an shiga d'akin haihuwa kad'ai Usman ya kira Hajia ya fad'a mu su, kafin Hajia ta iso Khadija ma ta fara jin bayan ta na d'aurewa tare da rik'ewar mara, a hankali taja baya ta zauna kan bancin da ke wajen, da sauri Usman ya sunkuya ya na kallon ta yace "Ya dai Nana, ko dai kema jikin ne?" Wani iska ta furzar ta girgiza kai tace "Um um." Sake kafeta ya yi da ido yace "Kin tab'a ba komai?" "Babu." Ta fad'a ta na huci, kallon tuhuma ya mata yace "Khadija ko dai kema a shigar da ke ciki ne?" "Ka bar shi kawai, ba buk'ata." Ta fad'a a wahalce, "Kin tabbata?" Da k'yar tace "Na tabbata." Mik'ewa ya yi yace "Shikenan, amma dan Allah da kinji wani abu ki yi magana tun da wuri." Komai ba tace ma sa ba har Hajia ta same su tare da malam da ya kawota, kamar dama jiran zuwan Hajia ake sai ko ga wata likita ta fito ta kalli Usman tace "Alhamdulillah ta haihu lafiya, an samu d'iya mace." "Alhamdulillah." Suka fad'a kusan a tare, nan akayi duk abin da ya kamata wanda suke buk'ata, lokacin dare ya yi sosai Hajia tace Usman ya koma gida da Khadija ita za ta zauna wajen su, ba b'ata lokaci suka kama hanyar gida Khadija sai gyangyad'i take, kallon ta ya yi ya na murmushi yace "Hajia wane suna ki ka zab'a da za'a sawa 'yar ta ki?" Cikin doguwar hamma tace "Ka tambayi maman ta mana, watak'ila ta na da sunan da take sha'awa ita ma." Wani kallo ya mata yace "Ta na da wata uwa ce da ta wuce ki a duniyar nan?" Cike da kasala tace "To idan da hali a saka mata *Nana Aisha* kaga idan na haihu nan kusa nima munyi 'yan biyu kenan sai a saka mata *Humaira*." Cikin murmushi yace "Idan kuma namiji ki ka sake sunkuto min fa." Cikin zolaya tace "Sai ka saka masa *Humair*." "To amma..." Da sauri ta katse shi tace "Dan Allah ka rabu da ni bacci na ke ji." Dariya ya yi yace "To idan ki ka yi bacci a motar fa?" Kai tsaye tace "Saika d'auke ni ka kwantar da ni akan gadon ka." Wani kallo ya mata yace "Me ya sa sai a kan gado na?" "Saboda ina so haihuwa ta same ni akan gadon." Marairaicewa ya yi yace "Yanzu ku saboda Allah haka za ku had'e min kai ku haihu lokaci d'aya, kenan dole nima sai na yi jego kamar ku." Dariya Khadija ta dinga shek'awa har da rik'e ciki kafin tace "Ai daidai kenan, kaga kai ma sai ka nemi k'unzugu ka aje saboda tarban jinin bik'i." Kamar zaiyi kuka yace "Allah ni dai ban yarda ba, babu wani jego da zanyi haka kawai da raina da lafiya ta, dole kisan dubarar da za ki dinga min saboda na gujewa abkawa jego." Hararan shi ta yi tace "Saboda ni kad'ai ce ke da kai?" Saida ya kashe mata ido yace "Amma ai ke dabance, ke kad'ai
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117