Skip to content

Chapter 56

Chapter 56

Kallon Kitse Book One Complete Hausa Novels 1,200 words 0 views Progress saved
Download Book

ka yi farin ciki hakan ya ishe ni." Mik'ewa ya yi yace "Nagode matata, ni zan koma can na canza kaya, amma ki tashi ki yi wanka yanzu sai ki fito mu ci abinci." Cike da makirci tace "Toh." Ya na fita ta sauka da gaggawa ta shiga ta yi wanka ta fito ta yi sallah, riga ta saka iya gwiwa yar kanti ta fito da ita kai babu d'an kwali, lokacin Bilal har ya shirya Bilyamin ya d'auke shi sun tafi, Usman na zaune akan kujera Khadija na zuba masa abinci, yanda ya d'aure fuska babu annuri ne ya sa ta share shi ita ma, mayar da kallon shi ya yi ga Haseenah da ta fito ta na karkad'e gashin ta cikin takon jan hankali, kallon ta Khadija ta yi har ta zauna akan kujera, da wani shegen murmushi Usman yace mata "Sannu da fitowa." Turo baki ta yi cikin shagwab'a tace "Ba zan sake ma ka magana ba sai nan da wata d'aya." "Me?" Ya fad'a da zaro ido, d'orawa ya yi da "Haba amarya rufa min asiri mana, ina zan saka kai na to idan ki ka daina min magana, kinsan fa ke ce haske kuma fitilar zuciya ta dama gidan nan ba ki d'aya." Sake turo baki ta yi ta kawar da kai tace "Ni ka k'yale ni kawai." "To wai me na yi ma da za'a min wannan hukuncin?" Kallon Khadija ya yi saboda aje farantin abinci da ta yi gaban shi, ita ma zubawa ta yi ta zauna ta fara tsakura ta na satar kallon su, amma zuciyar ta ta kai k'arshe wajen k'una, cike da shagwab'a tace "Ka ma manta kenan? Haka kawai ina bacci na za ka zo ka tara min gajiya, yanzu gashi duk jiki na ciwo ya ke, kuma saida na fad'a ma ka kar ka yi amma ka k'i saurara ta." Hannu ya sa ya na shafa wuyan shi cikin alamun rashin gaskiya, satar kallon Khadija ya yi wacce ta k'i d'ago kai saboda hawayen da ke son taho mata, dan ya kawar da zancen ya sa ya kalle ta yace "Ba ki zuba mata abincin ba ita." Wani jan kallo ta mi shi tace "Au! Wai ni ce ma zan zuba mata? To ai na ga duka yau kwanan mu ne ni da ita, me zai hana ta zuba da kan ta ko kuma ka zuba mata." Had'e rai ya yi yace "Ke me ki ke nufi ne? Ba na son maganar banza fa kinji ko, daga k'aramar magana za ki wani tasowa mutane, zuciyar ki ta raya mi ki k'arya da gaskiya kawai sai ki zauna akai." Zunbur ta mik'e tace "Au! Wai zuciya ta ma ce ta raya min kenan? To kamar yanda ba ka son maganar banza haka nima, wallahi Abban Bilal ka ji tsoron Allah kasan cewa za ka mutu." Maida kallon ga tayi ga Haseenah tace "Ke kuma ki sani duk rayuwar da aka ginata babu Allah a ciki wallahi k'arshen ta munin ta ya na bayar da mamaki, Allah ma shaida ne ban rik'e ki a zuciya ta ba ko kad'an, na so na zauna lafiya da ke mu taru mu farantawa mijin mu, amma na fahimci kin biyo abun ta bayan gida saboda cimma burin ki a kai na, ki sani Haseenah wallahi tallahi da ace zan yi dan na raba ki da Usman, to ina da bokan da idan har ya shiga tsakanin ki da shi wallahi tallahi ba ke ba duk wanda ya zauna tare da ke ma sai ya tsane shi, amma tuna akwai Allah kuma zan mutu ya sa na d'aga mi ki k'afa, amma muje zuwa." Ta na fad'a ta juya ta koma falon ta, janyo Haseenah ya yi ya d'ora a cinyar shi ya fara bata abincin ya na fad'in "Ki shirya kayan ki, ina tunanin tafiya da ke Dubai a satin nan, dan ba zan yarda na barki tare da matar nan ba a gidan nan." Duk da a zuciyar ta akwai abin da taji shed'an na raya mata, amma sai ta nuna ta yi murna ta hanyar cewa "Dubai? Ni? Wayyo Allah yaushe? Da gaske ka ke?" "Um, ki shirya kawai, ina tunanin tafiya nan da kwana biyu zuwa uku." Haka suka gama cin abincin ya fita ita kuma ta koma d'aki, ta jima ta na waya da Mariya ta na fad'a mata canjin da aka samu, amma ba ta fad'a mata abin da ta ke shirin aikatawa ba har suka yi sallama, su na gamawa Haseenah ta shirya tsaf ta fito, kai tsayz k'ofar fita ta nufa mai gadi ya bud'e mata k'ofa, a lokacin Khadija na madafa ta tsinkaye ta ta fice, aikin gaban ta ta ci gaba da yi ba tare da tunanin komai ba, har ta gama aiki da duk abin da ta ke yi, ta na zaune falo tare da Bilal Usman ya shigo, ta yi mamakin ganin shi a lokacin sosai, shi ma kuma ya na ta kiran Haseenah ne ta k'i d'aga wayar shi duk abin duniya ya dame shi, hakan ya sa ya zo gidan kuma ya na nufa b'angaren ta ya ga k'ofar rufe alamar ba ta nan, shi ya sa ya shigo wajen Khadija, tsaye ya yi a kan ta yace "Na ga yarinyar nan ba ta nan ko kinsan in da ta tafi?" Wani murmushin ta yi tace "Ni kuma ina zan san in da ta tafi? Ko gaishe ni ka ga ta na yi bare na samu kimar da za ta fad'a min za ta fita." Wani dogon tsaki ya yi ya sake kara wayar shi a kunne, ta na kururuwa wayar amma ta k'i d'auka, sake maida kiran ya yi hakan ya sa mahaifin Haseenahr d'auka, dama ko da ta je gida da kuka ta isa, ta na zuwa ta k'ara fashewa da kuka wai ita wallahi ta gama auren gidan Usman, anyi tabbaya amma ta k'i fad'a saida aka kira Baban ta ya zo sannan tace "Ni kawai ba zan koma gidan shi ba, wallahi ba na bacci a cikin dare sai a dinga bani tsoro, yanzu kuma kawai..." Kuma sai ta yi shiru, mahaifin ta ne yace "Kawai me?" Kallon shi ta yi da ido tsakar kai tace "Ba komai, ni kawai ba zan koma ba." Ta na ganin kiran Usman a waya sai ta ture wayar wai ko sunan ma ba ta son gani, hakan ya sa iyayen jikin su yin sanyi su ka fara tunanin shiga baga ne na kishiya kawai, shine yanzu da ya kira baban ta ya d'auka, saida su ka gaisa cikin mutumci kafin yace ya zo ya same shi gida ya na son ganin shi, ba musu yace ya na nan tafe yanzun, dan shima idan bai ganta ba ba zai iya salun nutsuwa ba, Khadija na kallo ya fita daga gidan da sauri. Ya na zuwa kam suka tattauna sosai in da Haseenah ke cewa kawai ya sake ta ba za ta koma ba, shi kam yace ba zai iya rayuwa ba yanzun babu ita, dan haka dai aka sasanta mahaifin ta yace ta je gida zai samar mata magani, haka ya d'auko ta suka dawo gida bayan ya bawa Baban

Table of Contents

Chapters

117 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117