Skip to content

Chapter 104

Chapter 104

Kallon Kitse Book One Complete Hausa Novels 1,199 words 0 views Progress saved
Download Book

cikin zafin rai ido jawur yace "Haseenah me nai mi ki a rayuwa? Me ya sa ki ka cutar dani? Me ya sa Haseenah?" Cikin duburburcewa tace "Wallahi ba ni bace, ka yi hak'uri dan Allah, ba zan.." Shak'e mata wuyan da ya yi ne yasa komai nata tsayawa idon ta fitowa waje, cikin fitar hayyaci Usman ke fad'in "Haseenah ke annoba ce, jaraba ce kuma masifa ce ke da bala'i, barin irin ki a doron duniya wallahi japa'i ne, wallahi da zan kashe ki amma ba zan iya ba saboda cikin da ke jikin ki, Haseenah banga anfanin zama da ke ba a rayuwa ta, kin raba ni da hankali na da ubangiji na, kin raba ni da iyaye na da 'yan uwa na, kin raba ni da matar da nafi so a rayuwa ta, sannan kin raba ni da d'ana da ya fito daga ciki na, Haseenah ni kam ya zanyi dake? Wane irin hukuncin ma zan mi ki ne da zai sa na huce abin da ki ka min." Haseenah dake ta fafutukar neman rayuwa ya na sakin ta ta samu ta sauke wasu numfarfashi, mik'ewa ya yi tsaye ya juya baya ya cire hular kan shi yana shafa sumar shi kamar zai cire kan, sake juyowa ya yi ya nuna ta da hannu yace "A dalilin ki yanzu haka Bilal na kwance asibiti, bansan ko zai rayu ba saboda yanda jikin shi yake, dan haka Haseenah ba zan iya ci gaba da zama dake ba, kije gidanku kawai na sake ki saki biyu." Wata k'ara Haseenah ta yi ta d'ora hannu akai tace "Ahhhhhhh, na shiga uku na lalace, dan Allah Usman ka rufa min asiri ka yi hak'uri ka yafe min, wallahi ba zan sake ba na rantse ma ka, ka taimaka min mana ka dubi cikin nan dake jikina, kar ka mayar dani bazawara tun yanzu Usman ko haihuwar fari banyi ba." Girgiza kai yayi ya tab'e baki yace "Hum, ai ko meya faru ke kika jawa kan ki, dan haka ki tattara naki ya naki ki bar min gida na, idan ki ka bari na dawo gidan nan na same ki wallahi saina lahira ya fiki jin dad'i." Yana fad'a ya fice daga madafar ya shiga b'angaren shi, rage kayan jikinshi ya yi ya shiga ya watsa ruwa saboda yaji sanyi, yana fitowa maganin ciwon kai yasha kafin ya canza kaya ya bar gidan ko kallon b'angaren Haseenah baiyi ba, a tunanin shi ma tana barin gidan zai ruguza wannan b'angaren dan ya zauna lafiya, dan ba zaisake bari zuciyarshi ta raya mi shi sake k'ara wani aure nan gaba, lokacin har an fara kiran sallah la'asar sai kawai ya tsaya ya yi sallah kafin ya isa asibiti. *Ana tare*🀝 11/03/2020 Γ  19:36 - πŸ’‹πŸ˜˜πŸ’‹: πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘ *KALLON KITSE* _(Ake wa rogo)_ πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘ _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _D'AUKAR FANSA_ *3* _BA SO BANE_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI_ *6* _JIHADI_ *7* _K'ANGIN RAYUWA_ *8* _ITACE K'ADDARARMU_ *9* _KAWU NA NE_ *10* _MAATA_ *11* _KALLON KITSE..._ *SADAUKARWA GA* _MATAN FARKO_ πŸ§•πŸΌ *(UWAYEN GIDA)* πŸ‡ΈπŸ‡¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_πŸ€œπŸ€› ```Fatan alkairi masoya``` _Bismillahir rahamanir rahim_ *38* Bai samu ganin Khadija ba saboda a lokacin suna sallah, kuma an rufe d'akin da Bilal ke kwance saboda hayaniyar da tayi yawa aka barshi shi kad'ai kafin wani lokaci, fita Usman d'in ya yi yace zai dawo anjima. A wajen Haseenah ba yanda ta iya dole ta d'an d'auki abin da ta d'auka ta fito ta na kuka ta bar gidan, amma da taje gida kasa fad'an komai ta yi sai tace kawai ta na girki ya same ta yace ta taho gida ya sake ta saki biyu, su kam iyayen take su ka d'ora laifin kan Khadija cewa ita ta shiga ta fita aka sake ta, Haseenah dai komai ba tace ba sai sauraren su, mahaifin ta ne yace zai je ya samu mahaifin Usman d'in dan ba zai d'auki wannan wulak'ancin ba a sako masa 'ya da tsohon ciki, ba ta yi yunk'urin hanawa ba tunda ita kan ta za ta so ta koma d'in, haka ko akayi bayan sallah magriba anyi katari malam ya na gidan mahaifin Haseenah ya sallama ya fito, da ganin shi malam ya tarbe shi yanda ya kamata ya shinfid'a mu su tabarma a waje su ka zauna, nan fa malam *Mussa* ya fad'awa malam abin da ke faruwa, sosai malam ya jinjina ya kuma fad'a mi shi baisan me ke faruwa ba sai yanzu, amma ya yi alk'awarin tuntub'ar Fodio yaji dalilin yin hakan, nan dai ya kwantar masa da hankali suka rabu lafiya, malam kam baiyi k'asa a gwiwa ba wajen kiran Usman yace ya same shi gida, ana idar da sallah isha'i ya k'araso ya samu malam, a cikin gida suka samu waje tare da Hajia suka tattauna sosai sosai, anan ya fad'a mu su cewa "A gaskiya Baba ba zan iya zama da yarinyar nan ba, domin kuwa duk ita ce silar abubuwan da suka dinga faruwa da ni, kawai ku rabu da ita can ta haihu, idan ta haihu zanje na d'auko abinda ta haifa bayan ta shayar da shi dan ba zan iya barin abin da ta haifa a hannunta ba saboda mugun halin ta." Malam ne yace "Amma duk abin da tayi Fodio bai kamata ka sake ta a wannan halin ba." Shirun da ya yi yasa Hajia cewa "Koma dai menene ita taja, a gaskiya Hassenah ta bamu mamaki, yarinya sumi-sumi ashe lunbu-lunbu ce macijin k'yaik'ayi, muna ta wa Khadija kallon mai laifi ashe ita ce muguwar." Murmushin gefen labb'a malam ya yi yace "Ai ni na sani dama *kallon kitse ne ku ke wa rogo*, kawai na zura mu ku ido ne har ita yarinyar ta mu ku ido, in banda hauka irin na ku ma ko gaske ne Khadija ta mallake Usman ai ni a gani na daidai ta yi, domin kuwa in har za mu iya yin magana irin ta jahilai to za mu iya cewa k'ashin arzik'in shi a jikin ta yake, shi ba kyau ba, shi ba hasken fata ba, shi ba kud'i ba a lokacin da ta aure shi, kuga kuwa tana da damar da za ta iya d'aukar kowane mataki dan ya zama na ta." Cikin sanyin jiki Hajia tace "Gaskiya ne, wallahi sai yanzu na ke jin kunyar ta akan abubuwan da suka faru, daurewa kawai nake ina kallon ta." Murmushi Usman yayi yace "Hajia ku kwantar da hankalinku in dai Khadija ce na tabbata ba ta kallon ku da wannan abun." Nan dai suka gama tattaunawarsu kafin ya mu su sallama yace zai tafi asibiti, su kuma dama acan su ka yi sallah magriba, ba su jima da dawowa ba Abban Haseenah ya zo, daga nan asibiti ya nufa ya samu kam kamar ana wata sabga d'akin taf da mutane, Khadija dake zaune kusan Bilal muryar shi ce ta fallasa mi shi yanayin da yake ciki, duk sai taji ba dad'i tausayin shi ya kamata, gaisawa ya yi da mutanen dake d'akin kafin ya isa a gadon Bilal, kafe Khadija ya yi da ido yace "Nana ya mai jikin?" Saida ta had'e abin da ya

Table of Contents

Chapters

117 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117