Chapter 41
Chapter 41
ajiyar zuciya yace "Lafiyar su k'alau, kai kawo min lemu mai sanyi na sha." Ya k'arashe da kallon Bilal. D'auko masa ya yi ya kawo ya ba shi ya amsa, sai da ya fara sha ya kalli Bilal yace "Ina auntyn ka take?" "Ta na d'akin ta." Cewar Bilal ya na kallon k'ofar falon mahaifin shi, tura shi Nura ya yi yace "Je ka ce ina kiran ta, ka ce ta fito ta kwashi gaisuwa tare da albarka mai gida ya dawo." Da dariya Bilal ya nufi k'ofar falon mahaifin shi, cikin daka tsawa Khadija tace "Kai Bilal, ka na da hankali kuwa? Dallah malam dawo ka zauna min nan." Da mamaki duka su ka kalle ta, in da ta nuna masa da hannu ya zauna hakan ya bata damar kama kunnensa tace "Wallahi ka sake zuwa in da matar can take sai na b'ata ma ka rai, kaji ko?" Yanda ta d'aga murya tare da k'ara murd'e kunnen shi ya sa yace "Na ji Mummy, ki yi hak'uri ba zan k'ara ba." Nura da ke kallon ikon Allah ne yace "Khadija me ya sa za ki ma sa haka? Naga da ke da ita ai duk d'aya ne, iyayen shi ne ku." Tsaye khadija ta mik'e tace "Dakata min Nura, ni daban ita daban, wallahi duk yanda za ta kyautata mi shi ba za ta tab'a zama kamar ni uwar shi ba, dan haka kar ka sake had'a min yaro da wata banzar mata da ba ta san darajar shi ba, idan ka zo gani na ne na gode, idan wajen ta ka zo ka shiga ta na ciki." Juyawa ta yi ta shige uwar d'akin ta, mamaki ne ya kusa kashe Nura, dan shi dai a sanin shi wani ma ba su tab'a samun matsala da Khadija ba bare kuma dangin mijin ta, cikin sanyin jiki ya aje robar lemun hannun shi ya mik'e zuciyar shi na tunanin wane irin kishi ne da Khadija haka? Bilal ne ya mik'e yace "Tonton (uncle) Nura zan bika wajen Hajia." Shafa kan shi ya yi yace "To ka fara fad'awa Maman ka, idan ta amince sai ka d'auko kayan ka mu tafi." "To." Ya fad'a ya juya da k'arfi ya shiga d'akin, zaune ya same ta yace "Mummy, tonton Nura yace na d'auko kaya na mu tafi gida wajen Hajia." Cikin jin haushi tace "Babu in da za ka je, ka wuce d'akin ka ka kwanta ko kuma ka yi karatu." Hawaye ne su ka cika idon shi saboda shi dai haka ba ta tab'a faruwa tsakanin shi da maman shi ba sai yau, juyawa ya yi zai fita sai taji ya bata tausayi, amma kuma hushin ta da duk dangin Usman da suke murnar an mata kishiya, a hankali tace "Bilal." Juyowa ya yi ya dawo ya tsaya, hannun shi ta kama tace "Ka had'a kayan ka zan kira tonton Naseer ya zo yanzu ya d'auke ka, hakan ya yi?" Ba tare da sakin fuska ba ya d'aga kai alamar eh, fita ya yi Nura na tsaye yace "To ya? Za mu wuce ne?" Kamar zai fashe da kuka yace "Mummy ta hana." Ji ya yi kafin yace "Shikenan kar ka damu, ai gobe juma'a, watak'ila ku tafi gidan tare da Abban ka." Shiru bai ce komai ba har ya fita daga gidan ba tare da ma ya shiga wajen Haseenah ba, ta na kiran Naseer kam dama bai shiga gida ba, dan haka ya taho d'aukar shi, sai dai lokacin Usman ya shigo gidan, sun gaisa kamar yanda su ka saba tare da wasa da dariya, amma har Khadija ta had'awa Bilal kayan shi su ka tafi babu fara'a a tare da ita bare ta yi magana, a tak'aice dai haka duka gidan su ka gudanar da daren su babu armashi a ciki, dan Usman ya nunawa Haseenah kuskuren ta ma ko abincin ta bai ci ba, haka ma a d'aki da suka kwanta juya mata baya ya yi, dan in har za ta iya cin zarafin d'an shi har haka to fa akwai yiwuwar ya nuna mata ba'a mi shi wasa da gudan jini. Washe gari da safe ma haka abin ya ke, kasancewar Khadija ta san a wannan lokacin ya na d'akin shi ya na karatu ya sa ta shiga har can ta gaishe shi, bai wani yi karin kummalo ba ya yi shirin masallaci, *11:00* cif ya fita ya bar gidan zuwa masallaci kamar yanda ya saba, bai dawo cin abinci da rana ba sai aikowa da ya yi aka d'aukar ma sa, da yamma kuma ya kira Khadija yace su shirya dukan su za su je su yi barka gidan Issoufou, tunda magriba Khadija ta gama shirin ta tana jiran shi, Haseenah ma ba ta b'ata lokaci ba wajen shirin duk da fitar ta ta farko kenan, watak'ila ta na zumud'i ne saboda yace zai aje ta har gidan su ma su gaisa da mutane, ana idar da sallah isha'i ya shigo gidan, shi ma sai da ya sake shiri kafin su ka fita gaba d'aya, Haseenah ce baya tare da kwanukan abincin da zata kai gidan su. Babu mai magana a motar dan kowa da abin da ke ran shi, sai Khadija da ke latsa wayar ta hankali kwance, gidan su Haseenah su ka fara tsayawa dan ya fi kusa da gidan Issoufou, Usman da Haseenah ne su ka fita, amma ganin Khadija ba ta da niyyar fitowa ya sa ya kalle ta yace "Uwar gida sarautar ta motsa ne? Ko sai na fito da ke?" Ko kallon shi ba ta yi ba tace "Ku shiga kawai zan jira ku." Wani murmushi ya yi yace "Ke ma kinsan ba zan lamunci haka ba ai, fito mu wuce dallah." Cike da damuwa tace "Ba na cikin yanayin dad'i, ba na so kowa ya fahimci hakan har a dasa min hak'ora, dan ina fitowa za ace ba na da mutumci na fiya kishi da yawa." Bud'e murfin motar ya yi ya kamo hannun ta ta fito, bai saki hannun ta ba har sai da su ka shiga cikin gidan, sakin ta ya yi ya saci kallon ta yace "In dai ina da mahimmanci a wajen ki, to ki kankaro min mutunci na a gurin mutanen nan, kar ki bari laifin 'yar su ya shafe su." Kallon shi ta yi da farko turo baki ta yi, amma da ya marairaice sai ta saki fuskar ta na murmushi, Haseenah da tuni ta shiga gidan su ba ta ma san tsiyar da ke faruwa ba, sallamar su ce ta sa ta mik'e ta d'auko mu su kujeru su ka zauna, mahaifin ta na daga gefe zaune akan kujera, sai mahaifiyar ta na cikin sange zaune akan katifa da alama sunyi shirin bacci kenan, sosai su ka gaisa cike da mutunci da girmamawa, jim kad'an su ka mik'e Khadija na fad'in "Mama mu za mu wuce, saida safen ku." "To Allah ya bamu alkairi, Allah fisheku dare." Cewar maman. Da "Ameen." Su ka amsa, Haseenah kamar kar ta tafi take ji haka dai ta taso su ka fito, su na d'aukar hanya Usman ya kalli Haseenah ta madubi yace "Ke Hajia haka ake harkar duniya, daga kawo ki ku gaisa
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117