Chapter 48
Chapter 48
wani yanayi da ita dai ba ta tab'a ganin shi a ciki ba ya sa ta d'an kalle shi da mamaki, ganin nufota kawai ya ke ba magana ya sa ta k'ara yin baya da in'i'na tace "A..Abban...Bil." Ba ta k'arasa ba yace "Khadija akan me ku ka ci zarafin mata ta a gidan biki cikin mutane?" Mamaki ne fal a idon ta, rarraba ido ta fara yi sai motsa baki ta ke ta na so ta yi magana amma ta kasa, nuna ta ya yi da yatsa yace "To daga yau kar haka ta sake faruwa, idan ba haka ba kuma ran ki zai b'ace, sannan Hajia Turai ba na son ki sake mu'amula da ita, kinji na fad'a mi ki." Bai jira me za tace ba ya fita daga d'akin ya nufi d'akin Hassenah wacce ta buga tagumi ta na jiran ta jime zai faru, ya na ganin ta da wannan tagumin sai ya ji tausayin ta a tunanin shi akan abin da ya faru ne, ita kuma ba ta ma san me ya faru ba, zaune ya yi kusan ta ya kalle ta yace "Amarya ta, dan Allah ki yi hak'uri kinji akan abin da ya faru, insha Allahu na mi ki alk'awari hakan ba za ta sake faruwa ba." Cikin rashin fahimta tace "Me kuma ya faru? Akan me ka ke magana?" Jannyo ta ya yi jikin shi ya na shafawa yace "Idan ke ba ki fad'a min ba ai Hassana ta fad'a min, amma kamar yanda na fad'a mi ki ne ba zai sake faruwa ba in Allah ya yarda." Shiru ta yi a k'irjin shi ta na tunanin me ye ya faru to? Jin ta yi shiru ya sa ya d'agata daga jikin shi da cewa "Zan shiga wanka, amma ki tabbatar kin fito mun ci abinci ba sai na zo da kai na ba." Da kai kawai ta ma sa alamar to, fitowa ya yi ya nufi d'akin shi, ya na bud'a k'ofar ya tsallaka ya sake jin gaban shi ya tsinke ya fad'i tare da sarawar kai, hannu d'aya ya saka ya dafe kai ya rintse ido sosai, da k'yar ya iya furta "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un." Gaba d'aya jikin shi ne ya yi sanyi a haka ya cire kayan shi, zai shiga wanka Khadija ta yi sallama a d'akin ta shigo, shiru ya mata kamar bai ji ta ba har ta tsaya gaban shi, wani abu ya ke ji a zuciyar shi da bai tab'a jin irin shi ba tunda ya ke da ita, amma da ya ke sabon abu ne sai ya taushi zuciyar shi, a hankali ta rik'e kunnuwan ta cikin taushin murya tace "Ka yi hak'uri *sadauki na*, na karb'i kuskuren da k'awaye na su ka yi, kuma zanyi yanda ka ce da yardar Allah." Ba fara'a a fuska yace "Ya wuce." Ban d'aki ya nufa ta yi saurin rik'o hannun shi ya juyo, marairaicewa ta yi tace "Ka tab'a wanka da kan ka idan ban taimaka ma ka ba?" Wani murmushi ya yi kamar mai ciwon baki kafin ya ja hannun ta zuwa ban d'akin, sosai Khadija ta fahimci akwai sabon al'amari a tare da shi, dan har ta gama mi shi wankan nan ba su yi wata magana ba, kamar yanda sai dai ya mata murmushin yak'e kawai, haka ta gama mi shi shiri su ka fito cin abinci, sun zauna kenan Haseenah ta fito ita ma, tunda ya kafe ta da ido bai d'auke ba har ta zauna, murmushi kawai ya ke sakar mata har Khadija ta gama zuba abinci. Haka aka ci abinci babu wani nishad'i bare jin dad'i, su na gamawa ya nufi wajen Haseenah dan yi mata saida safe, ita ma Khadija shiga ta yi dan ta yi shirin bacci, amma har ta gama ta dawo bai dawo d'akin shi ba, abun mamaki shine har ta d'auki minti ashirin kwance kafin ya shigo, ya na can Haseenah na zuba shagwab'a wai zai tafi ya bar ta, ya na shigowa kashe wuta ya yi ya kwanta, zunbur Khadija ta mik'e da tafarfasar zuciya ta na kallon k'eyar shi tace "Me zan gani haka Abban Bilal?" Juyowa ya yi a kasalance yace "Me fa?" "Baya fa ka juya min, me na ma ka haka da zafi? Akan abin da ya faru ne? Dan Allah ka yi hak'uri in dai abin da ya faru ne zai sa ka juya min baya." Yanda ta yi maganar cikin muryar kuka ya sa k'wak'walwar shi hasko mi shi wacece ita, tashi ya yi zaune ya rumgumo ta jikin shi yace "Shikenan to ya wuce, ki yi hak'uri kar ki min kuka, ba na yi bane da gangan, kawai ba na jin dad'i ne." Da kuzari ta kwantar da shi akan gadon tace "Kwanta to na ma ka tausa." Cire mi shi rigar shi ta yi a hankali ta fara shafar bayan shi, yanda ta gama kashe mi shi jiki ya sa ya juyo ya sauke idon shi akan ta, da k'arfi ya fizgo ta ta fad'a jikin shi ya had'e labb'an su...saida safe. Kwana biyun da ya yi a wajen Khadija ya zo da al'ajabi, dan sosai ta ke gani bak'in al'amura daga gare shi, shi kan shi ya na jin wannan canji a tare da shi, amma tasirin wani abu ne ya ke mi shi togaciya ga abin da ya ke ji, asabar da yamma Haseenah ta karb'i girki, a daren ranar da ta yi anfani da maganin nan a marar ta ko da Usman ya kusanceta ya ji duk fad'in duniya babu maccen da ya ke son kasancewa da ita sama da ita, ba ma wannan bane yafi d'aga hankali kamar yanda ya ke jin kamar ita ce ma macen da ta fara gamsar da shi a shinfid'a, gaba d'aya ya nemi tasirin wata mace ya rasa, tun a daren ya fara ririta Haseenah kamar yau ya fara ganin ta ko sanin ta. Washe gari ma bayan ya fita ta sa aka samo mata fura ta dama, sosai ta had'a furar kafin ta zuba maganin na k'arshe a ciki, da kan shi ya zo cin abinci bayan ya kammala ta kawo mi shi furar cikin kofin tangaran mai kyau, kallon ta ya yi yace "Fita na ke so na yi fa, idan kuma na sha furar nan jiki na zai mutu na yu bacci." Cike da shagwab'a tace "Uhum uhum, wallahi ni dai ban yarda ba sai kasha, saboda kai fa na had'a." Take ya ji sak'on ya kai zuciyar ya ji ai tafi k'arfin ma ya yi gardama da ita, amsa ya yi tare da kurb'ar furar har ya shanye, mik'ewa ya yi ya shiga wanka ya na fitowa ko riga bai saka ba ya kwanta sai bacci. Da da magriba ta tashe shi ya yi alwala ya tafi masallaci, bai shigo gidan ba har ya yi sallah isha'i, ya na idawa ya d'auko hanyar dawowa a lokacin kuma Naseer ya dawo da Bilal gida, sun jima a k'ofar gidan su na kafin Naseer ya tafi shi ya shigo ciki, kai tsaye tare da Bilal suka shigo b'angaren Khadija, tunda ya hangi Khadija akan kujera ya ji wani bala'i ya taso mi shi tare
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117