Chapter 64
Chapter 64
ta yi sakayau da ita, domin ya bata hak'uri ya sa ya k'arasa bakin titin da ke ofishin wajen masu siyar da waya, nan fa ya siya mata tsandareriyar waya ta ban hak'uri haka Bilal, dan ya jima ya na si ya siya mi shi dan ya dinga game, saida ya tsaya ya yi sallah azahar kafin ya wuce gidan, har madafa ya same ta ya bata wayar, ta yi murna sosai ta masa godiya, kallon ta ya yi yace "Ina Bilal?" "Ya na falon maman shi, ba irin lallab'ar da ban masa ba ya fito ya k'i." Fita ya yi ya na fad'in "Ina zuwa." Ganin ya sa ta bi bayan shi dan kar azo tambayar Bilal wani abu zaiyi, tare su ka shiga ya na kwance da alama ma bacci ya ke ji, zaune ya tashi yace "Abba sannu da zuwa." Shafa kan shi ya yi ya na zama kusan shi yace "Yarima hutawa ake?" "Um." Kawai ya fad'a yayin da Haseenah ta harare su ta wutsiyar ido a zuciyar ta tace "Hum! Yarima dai yarima, ku ba ku gaji sarauta ba amma ku lak'abawa yaro sunan yarima, haba dai." Ta k'arshe da yin k'wafa. Ledar hannun shi ya mik'a mi shi yace "Duba ka ga tsarabar ka." A hankali Bilal ya ciro kwalin ciki, ya na ganin waya ce ya yi sauri budewaya fito da ita sai shek'i take, dariya ya yi ya rumgume mahaifin na shi yace "Abba nagode, na ji dad'i sosai." Rumgume shi ya yi cike da so da k'auna yace "Hakan na ke son ji dama." Karb'ar wayar ya yi ya had'a mi shi da kan shi in da ya janyo mi shi mega (data) daga na shi ma'ajiyin sannan ya nuna mi shi yanda zaiyi ya dinga janyowa duk lokacin da ya ke so, nan fa suka zauna su na ta danne danne a wayar ya na nuna mi shi abubuwa da dama, Haseenah kam in ranta ya yi dubu tabbas ya b'ace, musamman da ya nunawa Bilal yanda zai iya janyo data amma ita saida ya amshi wayar ya jawo mata, haka ta gamo girkin ta kawo tare su ka ci da yaro kamar yanda suke ci a baya a faranti guda, har la'asar ya na gida tare da Bilal saida su ka yi sallah a masallaci kad'ai ya fita yace zaije gidan, dan da safe bai je ya gaishe su ba. *Hajia Turai* ta na zuwa gida ta'aniya zazzaga bala'i, k'arshe dai shiryawa ta yi a motar ta taje gidansu Khadija, Khadija na falo sun gama girkin rana suna cin abinci ta zo gidan, nan fa ta tashi duk wani mai baccin rana a gidan ta na fad'a mu su wulak'ancin da Usman ya mata, Khadija da ta iya k'awar ta ta shiru ta yi saida ta kalle ta tace "Ke kuma sai magana na ke amma kin min banza, ko har yanzu ki na son mijin na ki?" Tasan in ba ta bita sannu ba sai sunyi baran-baran, dan haka tace "Haba kema dai bari fad'in haka mana, ai ni tuni na yi wuri na aje shi tunda ya tab'a min ke k'awa ta, kwantar da hankali kinji tawa ki manta da lamarinsu kawai." "Yawwa yanzu na ji magana, ai na d'aukar har yanzu ki na son komawa gidan shi." Ta fad'a ta na saka hannu cikin kwanon abincin, murmushi Khadija ta yi tace "Haba ina, ai sai a aljanna kuma idan da rabo mun had'u." Saida ta cika baki da abinci tace "Shegiyar yunwa na damu na, amma wannan mijin na ki ya k'i bari na ci abinci ya aika min da yan sanda gida na, ke kinga bala'i da zafin shi ni da Usman a ofishin yan sanda." Yanda Khadija ta santa tasan yanzu ma saita sake dawo da labarin baya, hakan ya sa Khadija cewa "Haba k'awa ta rabu da su kinji, ci abinci dai yanzu muje d'aki akwai hira." Wata dariya ta yi "Hahahaha, haka na ke son ji k'awa ta, ki barsu kawai wallahi lokaci na zuwa da saiya dawo da k'afafun shi ya neme ki, wallahi saiya durk'usa har k'asa ya na neman afuwarki, ita kuma wannan tsinannar ko, haba, yo an fad'a mi shi mu na wasa ne, ai iskancin ma ba haka kawai mu ke yin shi ba, wallahi ko uban..." Tabbas Khadija tasan cewa za ta yi uban shi dan ita ba damuwa bane gare ta, dan haka ta rufe mata baki tace "A'a k'awata, surukina ne fa, dattijon arzik'i ne babu ruwan shi." "Hakane kuma, ai da ina so na mi ki misali da gyatumin shine." Duk abin da suke fad'a mamar Khadija na gefe na saurarn su, dariya kawai take ba tare da sanin su ba, haka suka gama sun shiga d'aki nan ma kuma Salamatu ta zo wacce Khadija ta fad'a mata a waya tana gida, aifa d'akin Khadija kamar zai tsage saboda hargowar da suke yi, har k'arfe biyar na yamma suna gidan nan kafin suka tafi. A wajen Usman kuma ko da ya je gida bayan sun gaisa da Hajia ta tambaye shi ya iyali, nan fa ya kora mata bayanin abin da ya faru daren jiya, Malam da shigowar shi kenan ya rabka salati ya na fad'in "Fodio, me na ke ji kana fad'a haka? Ka ce ta tafi gidan su sai ka neme ta? Me ka ke nufi da haka? Fodio ba ka ji kunyar fad'in maganar nan ba dan Allah?" K'asa ya yi da kan shi baice k'ala ba, malam ne ya d'ora da "To tashi ka fita, kuma da anyi sallah isha'i ka zo ka d'auke ni k'afar ka k'afa ta muje mu dawo da ita, ni ba za ayi wannan haukan da ni ba kaji na fad'a ma ka." A hankali ya mik'e ya saka takalmin shi zai wuce ta gaban malam ya kalle shi da kyau har ya fita, kallon Hajia ya yi yace "Anya kuwa yaron nan lafiyar shi k'alau?" "Ni ma dai abin da na ke tunani kenan, ya na wasu abubuwa kamar ba'a hayyacin shi ba." Cewar Hajia da ke k'ok'arin d'auke tabarmar da ya tashi akai. "Ai kuwa sai a d'auki mataki tun kafin abu ya yi nisa, amma in ba haka ba taya ma zai ce Khadija ta tafi gida saiya neme ta." "Gaskiya kam." K'arasa shiga d'aki malam ya yi ya na fad'in "Allah ya sawak'e." Kamar yanda ya fad'a ana sallah isha'i ya dawo gidan ya d'auki malam, basu zame ko ina ba sai gidan su Dijeh wajen biko, karo na farko a rayuwar su da haka ta faru, sallama su ka yi tun farfajiyar gidan aka amsa, Ashir da kan shine ya mu su iso falon Mama, dan dama suna nan zaune dukan su, matansu ne suka fito tare da yara aka bar mazan tare da Mama sai Khadija da ke d'aki ta kan iya jiyo maganganun da suke. *'Yata kawai ki koma*😉 14/02/2020 à 16:55 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *KALLON KITSE* _(Ake wa rogo)_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _D'AUKAR FANSA_ *3* _BA SO BANE_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI_ *6* _JIHADI_ *7* _K'ANGIN RAYUWA_ *8* _ITACE K'ADDARARMU_ *9* _KAWU NA NE_ *10* _MAATA_ *11* _KALLON KITSE..._
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117