Chapter 49
Chapter 49
da sarawar kan shi, da gudu Bilal ya k'araso ya rumgume ta, rumgume shi ta yi cike da k'aunar d'an na ta tace "Yarima kai da wa?" D'agowa ya yi ya na cire jakar bayan shi ya na fad'in "Tonton Naseer ne." Gira ta d'aga sama tace "Uhum! Wato dai kun zama abokai ko?" Dariya ya yi yace "Mummy bara kiga abin da ya siyo min, kuma Hajia ma ta siyo min wani abu." Murmushi ta yi ta mayar da hankalin ta kan Usman tace "Sannu da shigowa Babban mutum." Wani irin amo ya ji muryar ta na mi shi cikin kunne marar dad'in ji da sauti, juyawa kawai ya yi ya fita ta k'ofar da ya shigo ya nufi na shi falon, ya na fita ya ji wani sak'at a zuciyar shi saboda ba ya ganin Khadija, Khadija kam abun ya bata mamaki sai dai hayaniyar Bilal da kayan da ya ke fito da su ya na nuna mata ya sa ba ta wani saka a kai ba, shi kam ya jima zaune sai ya d'auko tunani kamar akan bak'on al'amarin nan, amma kuma sai ya ji k'walwar shi ta yi wani jugum kamar babu komai a ciki, hakan ya sa ya yi tsaki sama da dubu kafin Haseenah ta shigo ta same shi. Dare ya yi dare Khadija ta kasa bacci ta na tsammanin jiran shigowar Usman amma babu shi babu labarin shi, tun Bilal na mata hira na abubuwan da suka faru a gida har bacci ya d'auke shi, haka ita ma baccin ya d'auke ta daga wurin ba ta ankara ba, haka har akayi sallaha asuba gari ya waye bai lek'o ba, shi kuma ya na can ko ya ji a ran shi ya zo sai kuma ran shi ya b'ace haka kawai, har Haseenah ta masa magana ya zo ya mu su sallama ya share kawai, dad'i ta ji a zuciyar ta amma a zahiri ta nuna bai dace ba. Washe gari da safe haka kawai Usman ya ji ba ya son fita ya yi nesa da Haseenah, ko k'ofar gida bai fita ba in ba sallah ya je yi ba, bayan sallah la'asar Aziza ta zo gidan tare da rakiyar k'awar ta, kai tsaye b'angare Khadija suka fara nufa saboda nan kad'ai k'ofar a bud'e, Khadija da a lokacin abun duniya ya isheta na rashin ganin Usman bayan kuma ta na da tabbacin ya na gidan, amsa sallamar ta yi a dak'ile tare da kallon su a raunane, har su ka zauna babu wanda ya sake magana, kallon Uwani ta yi dake gefe tace "Uwani kawo mu su abun sha ko." To." Ta fad'a ta na mik'ewa, k'ala Khadija ba ta sake cewa komai ba har Uwani ta dawo da abun sha, sai lokacin Aziza tace "Aunty Khadija wai ina Bilal? Ban gan shi ba." Kallon ta Khadija ta yi cike da rainin wayo saboda tunawa da ta yi ranar da taji Aziza da bakin ta tana kiran d'an ta shege, a kaikaice ta sake kallon ta tace "... *Allah ka bawa dukanin musulmi lafiya.* 06/02/2020 Γ 22:23 - πππ: ππππππππππ *KALLON KITSE* _(Ake wa rogo)_ ππππππππππ _SAMIRA HAROUNA_ *Littatafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _D'AUKAR FANSA_ *3* _BA SO BANE_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI_ *6* _JIHADI_ *7* _K'ANGIN RAYUWA_ *8* _ITACE K'ADDARARMU_ *9* _KAWU NA NE_ *10* _MAATA_ *11* _KALLON KITSE..._ *SADAUKARWA GA* _MATAN FARKO_π§πΌ *(UWAYEN GIDA)* πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€ ```Fatan alkairi masoya``` *πΈπ¦ZAMAN AMANA WRITER'S* (GIDAN ZAMAN LAFIYA DA AMANA INSHA ALLAH)π€π€ *SANARWA! SANARWA!! SANARWA!!!* *INA JIGA JIGAN MASOYAN πΈπ¦ZAMAN AMANA WRITER'S WAD'ANDA BASU DA TAMKA A WAJENMU????? DUK WANDA YAKE TARE DAMU A CIKIN GROUPS D'INMU TO MUN TABBATAR K'AUNARMU CE TASA KUKA KASANCE TARE DAMU, MUNA YABAWA KUMA HAR ABADA BAMU DA KAMARKU WALLAHI,π DUK DA HAKA DAI GA LOKACI YAZO, KUMA DAMA TA SAMU NA TABBATAR MANA DA KUMA NUNA MANA HAK'IK'ANIN K'AUNAR DA KUKE MANA,π* Kunsan cewa k'ungiyarmu *πΈπ¦ZAMAN AMANA WRITER'S* suna cikin gagarumin gasa na samun award Wanda *women24 TV WhatsApp group* suka shirya kuma zasu gudanar? A wannan gasar ne za'a samu k'ungiyar da tafi kowacce k'ungiya yawan fans da Kuma bin k'a'idar rubutu Dan ki samu damar zabar k'ungiyarmu *πΈπ¦ZAMAN AMANA WRITER'S ASSOCIATION* zaki iya tuntub'ar wannan lambar 09030159301 Dan su saki a *WOMEN24 TV WHATSAPP GROUP* anan ne za'ayi zab'en k'ungiyar da tafi kowacce k'ungiya yawan masoya *Women24 Tv* Ba zabe kad'ai zakiyi ba Zaki k'aru da abubuwa da yawa kamar haka *Yanda ake girke girke* *yanda zaki gyara jikinki* *yanda zakiyi makeup* *yanda zaki daura Dan kwali* Kuma suna shirye shiryen nan na *arewa24 tv* kamar su *TARKON KAUNA* *DADIN KOWA* *KWANA CHASA'IN* *JAMAI RAJA* *SAPNE SUHANE* *GIDAN BADAMASI* *RUDIN ZUCIYA* *BAGHYA LAKSHMI* *AKUSHI DA RUFI* *AUDIO NOVEL* *HAUSA NOVELS* Kada ki manta da ranar zabe inkin shiga group d'in ki zaba *πΈπ¦ZAMAN AMANA WRITER'S* tanan ne zaki iya nuna mana irin sonda kuke ma k'ungiyarmu da littattafammu, kuma a ko'ina ko a kowace k'asa masoyanmu suke sunada damar zab'enmu ba sai 'yan nigeria kad'ai ba. Allah yabar zumunciπ€ππ₯°π _Bismillahir rahamanir rahim_ *20* "Bilal ya na nan, kinyi kewar shi ne har haka?" Wata 'yar dariya ta yi tace "Ban gan shi bane ba ai." "Uhum." Cewar Khadija can k'asan mak'oshi, jim kad'an Khadija ta kalle su tace "Ku wuce ciki mana ai suna nan, dan nasan wajen su ku ka zo." Cike da kunya Aziza ta d'anyi jim kamar ba za ta tashi ba, a hankali su ka tashi tace "Bara mu gaishe ta sai mu wuce." Da ido kawai ta bisu ba tace k'ala ba, saida su ka fita ta gyara zaman ta, su kuma sun jima bakin k'ofa su na bubbugawa tare da sallama amma shiru, da k'yar Haseenah ta fito cikin riga da wando ta bud'e, saida ta saki wani d'an k'aramin tsaki saboda ganin su, washe baki ta yi ta na fad'in "A'a'a'a, su Aziza ne a gidan mu? Sannun ku da zuwa, ku shigo mana, ashe ku ne ke ta bubbugawa, ina wanka wallahi." Duk ta yi maganar ne lokacin da suke shiga ciki, zaune su ka yi ita ta wuce ciki, da kallo su ka bita kafin su mayar da kallon su kan telebijin, Usman ta samu kwance akan gadon ta kamar mai son yin bacci, da k'yar ta samu ta rabu da shi ta sanyo hijabi ta fito, nan fa su ka shiga hira dan dama Usman yace kar ta gajiyar masa da kan ta za su fita cin abinci tare, dan haka ba ta damu ba har Aziza ta d'an kalle ta dan ita dama madafar ta ke son shiga, cikin taushin murya tace "Auntyn mu yunwa fa na ke d'an ji." Hararan gefen wutsiyar ido ta wa Aziza amma a zahiri ta yi dariya tace "Ki ke d'an ji ko ki ke ji?" Dariya su ka yi tace "To na ke ji, akwai indomie?" "Kinsan ai ba za'a rasa ba, bara na d'ora mu ku" Ta fad'a cike da k'arfin hali, Aziza ce tace "Ah haba dai amaryar mu, ina mu ina saka ki aiki, yayan mu fa na d'aki, dan haka ki bar mana komai ni zan shiga da kai na, ko kin
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117